Sashe 15
Kulsum Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Wunin ranar zungur ta yi shi ne da tunanin maganganun Taufeeq Mohammed Bello, wadanda ta auna ta ga cewa gaskiya ce zallah ya gaya mata. Ta amince za ta bi shawarar sa, za ta ci gaba da kauda Turaki daga kan hanyar ta. Matsalar ikon hakan ba nata ba ne. Ko ta yi kokarin hakan ba ta cin nasara. Ta amince an halicce ta ne domin ta rayu da soyayyar Turaki, soyayyar wanda bai san tana yi ba.
Washegari Taufeeq ne ya kai ta makaranta da kansa. Ya yi hakan ne domin ya samu damar yin sallama da ita. A gobe zai koma Lagos, kokarin sa na son ta sake da shi ya fara yin nasara.
Suna tafe a hanya ya ce, “Kulsum me zan samu? Gobe zan koma Lagos”.
Dan murmushi ta yi, ta ce, “Me nake da shi da zan ba ka Yaya Taufeeq?”
Ya juya kan motar ya shiga harabar makarantar, sannan ba tare da ya juyo ya dube ta ba, ya ce, “Your phone number”.
Ta fadada murmushin ta tare da cewa, “Don dai wannan ba ni wayarka in sa maka”.
Hannu ya mika ya dauki wayar daga inda ya ajiye ta a aljihun motar ya ba ta. Ta juya kyakkyawar wayar samfurin Iphone a hannunta, sannan ta soma dialing lambobinta a ciki. Ta yi saving da (Sister Kulsum) ta mika masa.
Daidai lokacin da ya yi parking a parking lot (wurin adana motoci) ya kashe motar ya juyo ya dube ta with affection (cike da kauna) cikin kwayar idanunsa.
“I will call you tonight, (zan kira ki da dare) Yusha'u zai zo ya tafi da ke, ni akwai inda zan je. Gobe in na tafi zan yi kewar abokiya ta Kulsum”.
Ta yi ‘yar dariya, abokiyar nan da yake fada yana amusing dinta. Don dai ita ba ta san mace da namiji na wata abota ba.
Ya kwantar da kai a kan sitiyari, murya can kasa ya ce, “Kulsum za ki yi kewata?”
Yadda ya yi maganar loving and romantic kamar ba Taufeeq ba. Tafukanta ta kai ta rufe fuskarta, ta rasa me ya sa ta ji kunya. Watakila yadda ya yi maganar ne.
Ya bude mata kofar side din ta ta fita tana saba jakarta.
“Yaya Taufeeq na gode”.
Ta juya ta soma tafiya, shi kuma ya bi ta da kallo. Ya rasa irin son da zuciyarsa ke ma Kulsum, mai mamaye zuciya haka farat daya.
Sai da ya daina hango ta, sannan ya yi reverse ya bar makarantar.
******
University Of Reading, UK.
Har ya shigo ofishin ya zauna bai sani ba. Ya dora haba a kan hannayensa yayi zurfi a tunani. Dr. Abdul’Ahad Maikano, ya sa hannu ya kwankwasa tebirin da yake tsakaninsu. A hankali ya dago ya dube shi, idanunsa sun kada sun yi jazir.
Abdul’Ahad ya ce, “Dr. Abubakar ko lafiya tunda ka dawo ban ganka ba? Ban ji feedback na zuwan ka gida ba?”
Ya sauke hannayensa bisa tebirin tare da sauke nannauyar ajiyar zuciya. A hankali ya ce, “Abdul’Ahad na rasa Kulsum, sakaci na ya jawo min babban da na sani. Maimartaba ya raba auren da kansa, sun maida UmmuKulsum ga iyayenta, su kuma sun bar garin da ita. Na tashi a tutar babu, ma’abocin da na sani. Hakika bijirewa iyaye babu inda zai kai mu sai ga rashin albarka da rashin kwanciyar hankali. Ina ma na karbi auren Kulsum da kyakkyawar manufa da ban kasance cikin kuncin da nake a yanzu ba”.
Maikano ya tausaya wa abokinsa, ya san irin wannan nadamar, ita ake kira ‘NADAMA MARA AMFANI’, ya ce, “Amma tsakaninka da su fa? Ina nufin iyayen ka?”
Ya ce, “Sun yafe min da kyar da sidin ludayi, sannan Maimartaba ya ba ni shekaru uku in kammala duk abin da nake yi a nan in koma gida, su kuma kakannin Kulsum sun ce ko sunan kasar da aka tafi da ita ba su rike ba, mun dai rabu a kan in sun zo end of the year za su karba min lambar wayar marikan nata. Su kuma su Maimartaba sun ce, in mun daidaita tsakanin ni da ita shi ke nan za su amince mu koma auren mu”.
Abdul’Ahad ya ce, “Ni kuma ka san wani abu? Ban yarda kakannin Kulsum ba su san inda aka tafi da ita ba. they just want to teach you a lesson or something else… in za ka koma next year zan raka ka mu je tare, kuma insha Allahu ba za mu dawo ba sai tare da Kulsum. Game din yanzu tsakanin kai da Kulsum ne babu interference na iyaye. Idan ka maida kanka dan soyayya Aboki ka samu Kulsum ka gama”.
Murmushin gefen baki Turaki ya yi, murmushin kasaitar sa da ginshirar sa da ya saba. Wannan kuma wani abu ne da bai san ya yake ba (lallashin mace da soyayya), ya saba shi ake cewa ana so har a yi ta husumar kishi a kansa. Yau Abdul’Ahad na fadin shi zai koma neman soyayya. A yadda yake jin son Kulsum ta dawo cikin rayuwarsa yana jin ba abin da ba zai iya ba, in dai zai same tan.
Ya fara tuna rayuwarsa, bayan shigowarsa UK, ya fara karatun medicine a jami’ar Reading Berkshire, ya kammala da kwali mai daraja inda kai tsaye ya tafi specializing a Ophthalmology wato fannin likitancin ido.
A dukka wadannan shekarun yana rayuwa ne with the guilt na laifin da ya san ya aikata wa Kulsum, yana kuma cike da taraddadin komawa ga iyayensa don ya san cewa ya yi musu laifi. Sannan tsaurin karatu irin na medicine ya hana shi samun lokacin komawa gida. Daga ranar da abun ya faru (ranar da ya karbe wa Kulsum alfarmarta) kamar an sa igiya an zarge zuciyarsa da soyayyarta. Everything happens like a magic, kuma kamar an tsara shi ya tafi a hakan. Abin da bai sani ba shi ne, Maimartaba ya tsara din, kuma komai ya tafi a yadda ya tsaran. (Kulsumu ta zauna a zuciyarsa koda ya tafi, idan ya san ya tafi ne ya barta a cikakkiyar matar sa).
Ganin girman laifin da ya aikata wa Kulsum a ranar da zai taho ya san Umma ta dau zafi da shi, shi ya sa ya ki kiran waya, kullum kokari yake ya kammala abin da ke gabansa ya koma gida bakidaya ya fuskanci kowanne irin hukunci daga iyayensa. Da wannan damuwar ya rayu a dukkan shekarun da ya kwashe yana karatu. Yana gama karatunsa kuma university din ta rike shi ya yi mata aikin koyarwa temporary sabida kyawun takardunsa.
Tun a shekararsa ta farko ya hadu da Abdul’Ahad Aminu Maikano. Babansa diplomat ne, ‘yan asalin jihar Katsina. Abotarsu mai ban sha’awa ce, sai dai Abdul’Ahad bai san komai a kan Turaki ba sabida zurfin ciki da rashin son magana irin nasa. Sai fa lokacin da ya rasa yadda zai yi da damuwarsa har ta soma sabbaba masa rashin lafiyar ciwon kai mai fitar da shi hayyacin sa da Abdul’Ahad din ya samu ya bayyana masa komai nasa.
Kuma bisa shawarar Abdul’Ahad din ne ya zo gida har abubuwa suka kwana yadda suka wakana. Madallah da aboki irin Abdul’Ahad mai fitar da abokinsa daga damuwa. Ya ji dadin shawarar sa, don haka ne yanzu ba ya boye masa komai da ya shafe shi. Tunda ga shi ya samu ya shirya da iyayensa.
Tunda ya dawo duk bayan kwana uku sai ya kira gida, secretly kuma suna waya da Batulu tana gaya masa har yanzu ba bayani, ta je wurin Goggo sau ba adadi ko za ta ci karo da wani abu a kan Kulsum din, amma sai dai su yi hira ta taho, kullum zancen Goggo daya ne, ita ba ta san sunan kasar da aka tafi da Kulsum ba. Baffa kuwa ba abokin zancenta ba ne da ma. Ga Kulsumun babu kawa balle aminiya, ita ce da ma kawar tata. Kuma aminiyar ta. She is very anti-social. Amma tunda Goggon ta ce za su zo karshen shekara ita kuma ta yi masa alkawarin kawo masa labarin Kulsum idan ta zo gari, sannan Goggo ta yi alkawarin bada lambarsu.
*** *** ***
Washegari Taufeeq ne ya kai ta makaranta da kansa. Ya yi hakan ne domin ya samu damar yin sallama da ita. A gobe zai koma Lagos, kokarin sa na son ta sake da shi ya fara yin nasara.
Suna tafe a hanya ya ce, “Kulsum me zan samu? Gobe zan koma Lagos”.
Dan murmushi ta yi, ta ce, “Me nake da shi da zan ba ka Yaya Taufeeq?”
Ya juya kan motar ya shiga harabar makarantar, sannan ba tare da ya juyo ya dube ta ba, ya ce, “Your phone number”.
Ta fadada murmushin ta tare da cewa, “Don dai wannan ba ni wayarka in sa maka”.
Hannu ya mika ya dauki wayar daga inda ya ajiye ta a aljihun motar ya ba ta. Ta juya kyakkyawar wayar samfurin Iphone a hannunta, sannan ta soma dialing lambobinta a ciki. Ta yi saving da (Sister Kulsum) ta mika masa.
Daidai lokacin da ya yi parking a parking lot (wurin adana motoci) ya kashe motar ya juyo ya dube ta with affection (cike da kauna) cikin kwayar idanunsa.
“I will call you tonight, (zan kira ki da dare) Yusha'u zai zo ya tafi da ke, ni akwai inda zan je. Gobe in na tafi zan yi kewar abokiya ta Kulsum”.
Ta yi ‘yar dariya, abokiyar nan da yake fada yana amusing dinta. Don dai ita ba ta san mace da namiji na wata abota ba.
Ya kwantar da kai a kan sitiyari, murya can kasa ya ce, “Kulsum za ki yi kewata?”
Yadda ya yi maganar loving and romantic kamar ba Taufeeq ba. Tafukanta ta kai ta rufe fuskarta, ta rasa me ya sa ta ji kunya. Watakila yadda ya yi maganar ne.
Ya bude mata kofar side din ta ta fita tana saba jakarta.
“Yaya Taufeeq na gode”.
Ta juya ta soma tafiya, shi kuma ya bi ta da kallo. Ya rasa irin son da zuciyarsa ke ma Kulsum, mai mamaye zuciya haka farat daya.
Sai da ya daina hango ta, sannan ya yi reverse ya bar makarantar.
******
University Of Reading, UK.
Har ya shigo ofishin ya zauna bai sani ba. Ya dora haba a kan hannayensa yayi zurfi a tunani. Dr. Abdul’Ahad Maikano, ya sa hannu ya kwankwasa tebirin da yake tsakaninsu. A hankali ya dago ya dube shi, idanunsa sun kada sun yi jazir.
Abdul’Ahad ya ce, “Dr. Abubakar ko lafiya tunda ka dawo ban ganka ba? Ban ji feedback na zuwan ka gida ba?”
Ya sauke hannayensa bisa tebirin tare da sauke nannauyar ajiyar zuciya. A hankali ya ce, “Abdul’Ahad na rasa Kulsum, sakaci na ya jawo min babban da na sani. Maimartaba ya raba auren da kansa, sun maida UmmuKulsum ga iyayenta, su kuma sun bar garin da ita. Na tashi a tutar babu, ma’abocin da na sani. Hakika bijirewa iyaye babu inda zai kai mu sai ga rashin albarka da rashin kwanciyar hankali. Ina ma na karbi auren Kulsum da kyakkyawar manufa da ban kasance cikin kuncin da nake a yanzu ba”.
Maikano ya tausaya wa abokinsa, ya san irin wannan nadamar, ita ake kira ‘NADAMA MARA AMFANI’, ya ce, “Amma tsakaninka da su fa? Ina nufin iyayen ka?”
Ya ce, “Sun yafe min da kyar da sidin ludayi, sannan Maimartaba ya ba ni shekaru uku in kammala duk abin da nake yi a nan in koma gida, su kuma kakannin Kulsum sun ce ko sunan kasar da aka tafi da ita ba su rike ba, mun dai rabu a kan in sun zo end of the year za su karba min lambar wayar marikan nata. Su kuma su Maimartaba sun ce, in mun daidaita tsakanin ni da ita shi ke nan za su amince mu koma auren mu”.
Abdul’Ahad ya ce, “Ni kuma ka san wani abu? Ban yarda kakannin Kulsum ba su san inda aka tafi da ita ba. they just want to teach you a lesson or something else… in za ka koma next year zan raka ka mu je tare, kuma insha Allahu ba za mu dawo ba sai tare da Kulsum. Game din yanzu tsakanin kai da Kulsum ne babu interference na iyaye. Idan ka maida kanka dan soyayya Aboki ka samu Kulsum ka gama”.
Murmushin gefen baki Turaki ya yi, murmushin kasaitar sa da ginshirar sa da ya saba. Wannan kuma wani abu ne da bai san ya yake ba (lallashin mace da soyayya), ya saba shi ake cewa ana so har a yi ta husumar kishi a kansa. Yau Abdul’Ahad na fadin shi zai koma neman soyayya. A yadda yake jin son Kulsum ta dawo cikin rayuwarsa yana jin ba abin da ba zai iya ba, in dai zai same tan.
Ya fara tuna rayuwarsa, bayan shigowarsa UK, ya fara karatun medicine a jami’ar Reading Berkshire, ya kammala da kwali mai daraja inda kai tsaye ya tafi specializing a Ophthalmology wato fannin likitancin ido.
A dukka wadannan shekarun yana rayuwa ne with the guilt na laifin da ya san ya aikata wa Kulsum, yana kuma cike da taraddadin komawa ga iyayensa don ya san cewa ya yi musu laifi. Sannan tsaurin karatu irin na medicine ya hana shi samun lokacin komawa gida. Daga ranar da abun ya faru (ranar da ya karbe wa Kulsum alfarmarta) kamar an sa igiya an zarge zuciyarsa da soyayyarta. Everything happens like a magic, kuma kamar an tsara shi ya tafi a hakan. Abin da bai sani ba shi ne, Maimartaba ya tsara din, kuma komai ya tafi a yadda ya tsaran. (Kulsumu ta zauna a zuciyarsa koda ya tafi, idan ya san ya tafi ne ya barta a cikakkiyar matar sa).
Ganin girman laifin da ya aikata wa Kulsum a ranar da zai taho ya san Umma ta dau zafi da shi, shi ya sa ya ki kiran waya, kullum kokari yake ya kammala abin da ke gabansa ya koma gida bakidaya ya fuskanci kowanne irin hukunci daga iyayensa. Da wannan damuwar ya rayu a dukkan shekarun da ya kwashe yana karatu. Yana gama karatunsa kuma university din ta rike shi ya yi mata aikin koyarwa temporary sabida kyawun takardunsa.
Tun a shekararsa ta farko ya hadu da Abdul’Ahad Aminu Maikano. Babansa diplomat ne, ‘yan asalin jihar Katsina. Abotarsu mai ban sha’awa ce, sai dai Abdul’Ahad bai san komai a kan Turaki ba sabida zurfin ciki da rashin son magana irin nasa. Sai fa lokacin da ya rasa yadda zai yi da damuwarsa har ta soma sabbaba masa rashin lafiyar ciwon kai mai fitar da shi hayyacin sa da Abdul’Ahad din ya samu ya bayyana masa komai nasa.
Kuma bisa shawarar Abdul’Ahad din ne ya zo gida har abubuwa suka kwana yadda suka wakana. Madallah da aboki irin Abdul’Ahad mai fitar da abokinsa daga damuwa. Ya ji dadin shawarar sa, don haka ne yanzu ba ya boye masa komai da ya shafe shi. Tunda ga shi ya samu ya shirya da iyayensa.
Tunda ya dawo duk bayan kwana uku sai ya kira gida, secretly kuma suna waya da Batulu tana gaya masa har yanzu ba bayani, ta je wurin Goggo sau ba adadi ko za ta ci karo da wani abu a kan Kulsum din, amma sai dai su yi hira ta taho, kullum zancen Goggo daya ne, ita ba ta san sunan kasar da aka tafi da Kulsum ba. Baffa kuwa ba abokin zancenta ba ne da ma. Ga Kulsumun babu kawa balle aminiya, ita ce da ma kawar tata. Kuma aminiyar ta. She is very anti-social. Amma tunda Goggon ta ce za su zo karshen shekara ita kuma ta yi masa alkawarin kawo masa labarin Kulsum idan ta zo gari, sannan Goggo ta yi alkawarin bada lambarsu.
*** *** ***