← Book details Kulsum Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 22

Sashe 1

Kulsum Part 2 Complete Hausa Novel · about 4 min read


KULSUM

2

Littafin

SUMAYYAH ABDULKADIR
[email protected]

SADAUKARWA
SADAUKARWAR littafin Kulsum bakidaya taki ce A'ISHAH MAHMOUD SHAFI'I (MARUBUCIYAR ZANEN DUTSE, BAYAN NA MUTU, KOMAI NISAN DARE da WAYE SHI?). Sabida gudummuwar ki a dukkan al'amurana. Allah ya bar zumunci a tsakaninmu har 'ya'ya da jikoki.

Yayar ki, TAKORI
7/11/2020

GODIYA
Godiya ta musamman ga Nura Sada Nasimat sabida jimirin sa na bin rubutuna kafin bugawa da bada shawarwari. Allah ya raya mana Yusuf Nura Sada rayuwa mai albarka.

JINJINA
Ga daukacin mambobin TAKORI'S ONLINE FORUM, littafin Kulsum ya jinjina muku, ni da ku hadin Allah ne. Allah ya bar mana zumunci har gidan aljannah. You are my source of inspiration.

GARGADI
Ban yarda a karanta wannan littafi a kowacce kafa ta sadarwa ba ba tare da izni na ba, tun daga radio, facebook, whtsp idan har ban yi izni ba, yin hakan karya doka ne kuma abin tuhuma ne daga lawyer na Barrister Sadiq Rufa'i Wali.

KULSUM-2
Tunda Kusulmu ta ke a rayuwarta ba ta taba tafiya mai dadi da ni'imar wannan ba. A.C na buga ta ko ta ina, wanda ya cakude da kamshin (car fresh) wato turaren mota mai dadin kamshi, ya bada wata irin iska mai dadin shaqa a cikin motar. Ta taba zuwa Gombe ita da surukar ta Hajiya Rakiya, amma ko daya lafiyar injin motocin da yanayinsu ba iri daya ba ne. Wannan mota ce ta zamani lafiyayya ta mukami sosai.
Ba su isa Birnin Tarayyah ba (garin da Haj. Nasara take) sai yamma lis, kai tsaye direban ya dauke hanya ya nufi kebantacciyar unguwar nan (Brains&Hammers). Kusulmu ta makure a jikin kofa cikin matukar gajiya wanda zaman mota fiye da awanni biyar ya haddasa mata, domin tunda suka taho banda gidan mai basu tsaya a ko'ina ba, sai kallon ikon Allah ta ke yi na abubuwan mamaki cikin babban Birnin Tarayyar Najeriya.
Dogayen gine-gine na zamani a ko'ina da motoci kala-kala bisa titina wadanda bata san da irin su a duniyar subhana ba. Ga gadoji na sama da kasa (fly over) wadanda bata taba gani ba. Don haka ta saki ido, baki da hanci duka tana shan kallo abinta. Ko kwakkwaran motsi bata yi kada a wuce wani abun bata gani ba.
Lokacin da direban ya tsaida motar a kofar gidan Hajiya Nasara daga farkon unguwar kasa amincewa idanunta ta yi cewa, wadannan gidaje ne, gidaje irin wadanda mutane suke rayuwa a ciki. Ita dai ko a fina-finai na hausa da suke kallo ita da Batulu ba ta taba cin karo da gidaje masu kyau, tsari da kayatuwar na unguwar su Hajiya Nasara ba. Ga shi gidan nata bai cika girma ba (pent house) kamar yadda turawa ke kiran sa.
Mai aikin Hajiyar wata kabila ce budurwa 'yar kabilar Igala, ta karbi jakar hannunsu su duka, tare da russunawa ta yi wa Hajiya Nasara barka da zuwa cikin harshen nasara, ta dubi Kulsumu tace "welcome Ma" Kulsumu ta yi mata murmushi. Don ta gane barka da zuwa take mata. Hajiya tace da ita cikin turanci.
Serah, kai ma ya ta jakar ta dakin can na kusa da na Nasma. Ki tabbatar ta ci abinci ta yi wanka ta huta. In ce ko dakin a gyare yake?
Ban jima da gyara shi ba tsaf, Ajiya. In ji Serah.
Hajiya Nasara ta dubi Kusulmu wadda ke tsaye tana zare ido kamar tsohon da yayi wa sarki karya, tsoron Ubangiji duk ya cika ta, tana mamakin yadda aka yi Goggo ta ke da alaka da Hajiya Nasara, don dai ita tun tashinta ba ta san a duniya akwai gidaje irin wadannan ba. Iyakar arziki da daula a wajen kowa a garinsu to ya kare ne gidan Sarkin Gaya. Ba don Goggo ta sha ba ta labarin Nasaran ba kafin ta ganta, kuma ta dade da sanin ko wacece ita a wurin Goggo, za ta iya rantsewa batan kai Nasara ta yi ta zo gidan su. Serah ta kama hannunta ganin ta tsaya kikam, sai aikin zare ido ta ke yi, ta ce,

Lets go to your room ka yi wanka kafin in kawo abinci, ka ji?
Chapter 1 · 0% Book details