← Book details Kara'in Inna Delu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 18

Sashe 14

Kara'in Inna Delu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Azumi fa kika ce Delu yo wane shegen ne zai yarda azumi nake, yo ni rabona sa azumi tin wancan shekarar, ko azumi nake saboda ket (Cake)Ɗin nan aradu na karya shi katsak sai dai in yi istigfari" Ya faɗa yana aikwa Inna wata harara dan ya lura kamar baƙinciki take ya ci cake ɗin.

"Amarya ke ake jira fa domin kowa yana son ganin kalar taki soyayyar" Cewar MC ganin amarya ta yi jinkirin bada cake.

Wani irin gyaɗa kai Jauro ya yi irin na kin dai ji ai ɗin nan. Inna kuwa wani kallo ta masa tare da ɗan danne gefen leɓenta ta saki wani murmushin yaƙe.

Wani irin hangame baki Jauro ya yi ganin za a saka masa cake aikuwa Inna tana zuwa bakin ta tura cake ɗin cikin bakin nasa tare da ƙara zungura shi da hannunta. Jauro kuwa da ya buɗe baki jin dirar wani tsatstsaman abu mai shegen ɗaci da wani warin kananzir sun baibaye masa baki, wani irin yamutsa fuska ya yi tare da zaro idanu dan gabaɗaya abun ya haɗe masa baki.

"Haɗiye mana Bebi" Cewar Inna tana sanya hannu ta haɗe masa leɓɓan bakin. Wani amai ne ya yunƙuro masa amma ganin Inna riƙe da leɓunansa ga idanun mutane a kansu dan kowa ya yi zaton duj cikin salon soyayya ne haka ya daure ya haɗiye dakyar yana neman yin amai aikuwa aka shiga tafa masa.

"Kai jama'a da kun san mai na ƙunsa a bakin nan nawa na haɗiya da baku tafa mini ba" Cewar Jauro a zuciyarsa kamar ya yi kuka.

Duk abin nan da ake Amna tana laɓe daga wani wuri tana kallonsu, dan ita ce ta je kicin ɗin Inna inda aka ajiye cake ɗin ta jiƙa bula lemo, ta yi amfani da sabon sirinji wajen zuba wa a jikin cake ɗin, ta jiƙa filajin mai yawa gabaɗaya ta ɗore a cikin cake ɗin daga ƙarshe ta ɗura kananzir duk da sirinji. Bayan ta je gidan su ƙawarta shi ne ta biyo ta wajen partyn na Inna domin ganin ya za ta kaya.

"Ba dai kin ce sai kin yi aure ba duk da iyayenmu sun hana ki kaÉ—an ma kika gani" Cewar Amna a zuciyarta.

Haka dai aka gama taro aka watse motoci suka maida su Inna gida.

Washe gari da yake a ranar ne za ta tare da yamma suka tafi gidan wata mai maganin mata duk da wanda Inna tasha wanda suka siyo daga kasuwa amma sai da ta ce Lantana ta raka ta dan tana so ta rikirkita ango haka suka je da Shattu da Inna da Lantana direba ya kai su. Cicciɓi aka dafawa Inna ta cinye, da ƴan shila aka ƙara mata da maganin matsi har da na gyaran nono, haka suka cake kuɗin mai kayan suka bata tun a mota Inna take ta sakin wani murmushi, Shattu ce ta gaji ta ɗan matsa kusa da kunnenta ta ce

"Wai ni kam Delu dariyar me kike?"

"Hmmm bari dai ke ai na fara tunano yadda ango zai rule saboda na sha gyara, kinsan Allah Shattu a gidan mai maganin nan da na shiga bayi fitsari tsabar matsin da aka mini ko yatsa bai shiga wurin nan ba, aradu ina jin Jauro sai ya ɗauka da budurwa yake tare, dan yanzu ma ɗan tofina jargaf yake ya jiƙe yadda kika san ƙorama haka na koma" Cewar Inna tana ƴar dariya yadda direba da Lantana da suke gaba ba za su ji ba. Hannu Shattu ta bata suka tafa suna sakin wata dariya irin tasu ta tsofaffi da su kaɗai suka san ma'anarta.

Dab da magriba wata mota golf da Kande ta iyo shatar ta tun daga garinsu aka ɗakko mata kayanta, ita da wata budurwa ƴar ƙawarta mai suna Balaraba suka taho motar ce ta ƙaraso gidan aka ƙarasa da ita ɓangaren da aka ce za ta zauna dan Jauron ne ma ya raka ta sai kuma aka saka almajirai suka kwashe kayan.

*DARE*

*JAURO*

Sanye yake da shadda mai babbar riga hannunsa riƙe da kedoji guda biyu, haka ya je ɗakin Kande da ke zaune ita da Balaraba suna zumɓure-zumɓuren baki, da sallama ya shiga amma babu wanda ya amsa sai dai abin da ya lura da shi tun shigarsa Balaraba ke satar kallonsa tana masa wani kallo da ya kasa gane na menene. Haka dai ya ajiye musu ƙaramar leda mai tanƙwashen kifi ɗaya rak ya musu sallama babu wanda ya tanka masa ya fito ya nufi ɓangaren amarya Delu dan Inna ta ce babu wani wanda zai haɗa ta da wata kishiya ya musu kashedi dan haka ma bai tarka ba.

Yana shiga falon da sallama Shattu ce da ke cikin ɗakin ta amsa masa, suka masa iso a kan ya ƙarasa cikin bedroom ɗin haka ya ƙarasa ya same su Inna zaune a bakin gado lulluɓe da mayafi kanta a sunkuye, ƙafar nn da hannu ta sha ƙunshi, Shattu da Lantana sun saka ta a tsakiya.

Cinikin baki aka yi ya biya Shattu da Lantana suka musu sallama suka tafi ɓagaren su Lantana. Bayan fitarsu ango ya miƙe ya cire babbar riga ya matsa yana yiwa amarya daɗin baki ya buɗe fuskar.
"Allahu akbar, lallai Allah ya yi halitta a nan kin ganki kuwa Delu duk duniya babu wata mace da ta fiki kyau da matsayi a wurina"

"Har Baba Asabe?" Cewar Inna tana wani fari da ido.

"Haba Bebi idan ana dara ai fidda uwa ake, ya za a yi ki haÉ—a kanki da uwata"

"Allah huci zuciyarka ai na ji ka ce duk duniya yo ai na É—auka har ita"

Banza ya mata yana jin babu daÉ—i a ransa, amma babu yadda ya iya tunda dai yau yana so ya kwashi ganimar amarya.

Hannun Inna ya kamo ta janye da sauri.

"Haba Bebi ya haka kuma? Bayan na biya sadaki"

"Ka biya sadaki ko dai an biya maka, wallahi kana taɓa ni na ji wani yammm "

"Duk ɗaya ne ai tun da dai mijinki nake, yo ai yammm ɗin da kika ji alamar lafiyarmu ƙalaw ne "

"Haba Jauro ai tun ranar aure aka gwadamu aka ce babu mai ƙanjamau"

"Ba wannan lafiyar ba, lafiyar gabatar d sunnar aure"
Hannu ta sanya ta rufe idanunta alamar kunya, haka dai ya kama hannunta suka zauna a ƙasan ɗakin, har sun zauna Jauro ya ce su cire kayansu dan kar su yi ƙarnin kifi.

"Ki...ki...kifi fa ka ce?"

"Eh mana kifin amarci"

"Haba Bebi yanzu tsakaninka da Allah kifi ne a matsayin kazar amarya duk yadda muka ci burin ranar nn" Ta faɗa tana zumɓura baki. Haƙuri ya shiga bata haka suka cire kaya ita sai ta saka rigar bacci mai ƙaramin hannu shi kuma ya zauna da gaeran wando kawai. A baki yake bata tana bashi sun yi nisa wurin cin kifin suna korawa da lemon kwalbar da ya sako guda biyu sai kawai Inna ta haɗiyi ƙaya lemon ta sha amma ƙaya ta ƙi gaba ta ƙi baya, tun abin kamar wasa ya koma ba na wasa ba, ganin Inna riƙe da maƙogwaro tana ta ƙolon amai, hakan ua sanya Jauro cewa

"Bari dai in je ɓangaren su Umaru ko za a samu gayan tuwo ki samu ki haɗiya ƙayar ta wuce" Yana faɗa bai jira cewar Inna ba ya fita da sauri dan gabaɗaya ma a ruɗe yake. Haka ya ƙarasa ɓangaren Baba daga shi sai gajeran wando tiɓi-tiɓi dan wandon ya kama shi, yana zuwa ya shiga doka ƙofar da uban ƙarfi Baba da matarsa har sun kwanta suka ji ana ta bugun ƙofa kamar za a ɓalla, haushi ya sanya Baban ƙin tasowa ya buɗe dan gabaɗaya zuciyarsa a dagule take haushin wai yau mahaifiyarsa ke tarewa sai wani rawar ƙafa take wai ita amarya wannan abun shi ke ci masa tuwo a ƙwarya. Matarce ta tashi tana wani yamutsa fuska ta sauko ƙasa dan a sama ma suke.Tana zuwa bata tambayi waye ba ta buɗe ƙofar Jauro da ke jiran a buɗe ƙofar yana ganin an buɗe sai kawai ya afka ciki, ita kuma bata tsaya ta tantance waye ba dan kallan tsoro ta masa tunaninta ma ko wani kwarton ne dan ganinshi tuɓe sai gajeran wando bai ƙarami ɗaga mata hankali ya yi ba.

A sukwane ta juya tana sakin ihu kwarto, ta haura sama dan step bibbiyu take tsallakewa tsabar a ruÉ—e take. Jauro kuwa haushinta ma ya ji dan haka ko ta kanta bai bi ba sai ya nufi kicin zai dubo tuwon san shi amaryarsa ce a gabansa ba zai tsaya dogon surutu ba ya je ya rasa ta.

Baba kuwa jin ihun matarsa da kuma kiran kwarto da take sai ya tashi ya ɗakko wata sanda wadda ya tanada saboda irin ranar nan dan haka kafin ta shigo ɗakin ma ya fito da gudu ɗauke da sanda, a bakin ƙofa suka yi kiciɓis ta shige ɗakin da gudu a ruɗe alamar a tsorace take, tana shiga shi kuma ya iyo ƙasan a sukwane, yana sakkowa falon ƙasan ya hango Jauro ya bashi baya ya nufi ƙofar fita, ganinshi da gajeran wando ya tabbatar masa da kwartancin ya zo, dan haka cikin sanɗa ya lallaɓa ya saukewa Jauro sanda a gadon baya, sai ga Jauro ya zube a reran hannunsa riƙe da gayan tuwon da ya ɗakko a kicin zai kai wa Inna taimakon gaggawa. Zubewar Jauro ta yi daidai da saukar idon Baba a akan fuskar Jauro idanu ya zaro ganin mijin mahaifiyarsa kuma angon wannan rana.

"Baba Jauro" Ya faÉ—a cikin tashin hankali yana jefar da sandar ya nufe shi, hakan ya yi dai dai da sakkowar matar Baban daga sama tana É—ari-É—ari.

"Alhamdulillah dear ka rafka masa sandar" Ta faɗa tana ƙarasowa inda aka baje Jauro. Banza Baba ya mata dan ya san yau sai ta Allah tunda ya rafke angon mahaifiyarsa tunanin da yake a gefe guda ma shin mai ya kawo shi ɗakin.

"Lah ashe bayan kwartanci har da satar tuwo ya zo" Ta ce lokacin da ta ƙaraso wajen idanunta a kan tuwon da ya faɗi daga hannunsa.
Chapter 14 · 0% Book details