Sashe 12
Kara'in Inna Delu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Lallai yau na gane shayi ruwa ne, banda mutane baku da tsoron Allah ku da kuka zo cin arziƙi amma wadatar biki tsarki da romo shi ne har aka samu wani ɗan kan uwan da ya lalata mana kwalliyarmu saboda baƙinciki, to inason wanda ya yi wannan aiki ya sani an yi ba a yi bane wai rufe ƙofa da ɓarawo, in ma baƙinciki mutum yake to sai dai ya mutu mutu dan ni da Bebi Jauro mutuƙaraba takalmin kaza, kuma masu cewa tsoho da tsohuwa to ni banga tsofan Jaurona ba ganinsa make kamar saurayi ɗan shekaru ashirin, yo ai guntun gatarinka ya fi sari ka bani kuma...
Maganar Inna ta tsaya ne sanadin ganin wani saurayi mai ƙarfin hali, wanda ya zo har gabanta y tsaya yana mata video dan shi daga can inda yake videon ba ya ɗaukuwa shi yasa ya zo gabanta dan yau ya yi alƙawari duk wata lfr sadarwa sai ya ɗorata yadda ta yi jargaf da manjan nan, ko kwalliyar da aka mata ba a gani manja ya rufe ta ruf.
Kallo Inna ta ƙare masa ta ganshi sanye yake da garar riga irin mai farin nan tass sai baƙin wando, cikin sanɗa da ƙarasa gabansa shi kuma ya maida hankali cikin wayar dan da ya fara ganin tana matsowa a a cikin wayar sai ya ganta kamar aljana kuma bai yi zaton wurinsa ta nufa ba ya ɗauka ta kammala jawabin ne za ta bar wajen.
Inna Delu na ƙarasowa ta miƙa hannu cikin zafin nama ta damƙo wuyan rigar saurayin nan, saurayi na ɗaukan video sai ji ya yi an rafkoshi kamar wanda ɗan sanda ya kama ɓarawo, ɗago kan da zai yi aikuwa ya sauke su a kan Inna Delu da manjan nan sharkaf sai ɗiga take kamar wacce ta yi noman kwakwar manja.
Wani takaici ne ya lulluɓeshi ganin hannunta da manja amma ta kama masa riga, rigar ma fara, wani irin zabura ya yi zai fara mata rashin kunya, Inna kuwa hannu ta kai ta damƙo hannayensa ta haɗa wuri ɗaya ta damƙe dama ɗan siriri da shi kamar sandar rake, bakinsa dai ya buɗa zai fara magana aikuwa Inna ta saki ɗaya hannun nasa ta gwabje masa baki ta janyoshi ta wanka masa mari sannan ta kai masa kyawawan ranƙwashi guda uku.
"Allah ya isa n...
Ai kafin ya ƙarasa Inna ta janyoshi jikinta ta rungume sai da ta tabbatar rigarsa fara ta gama samun manja har fuskarsa marabarsu da Innar yanzu kaɗan ne dan shi ma kamar wanda ya shafa shuni amma na manja. Ihu aka ɗauka a wajen wanda har ya fi na lokacin faɗuwa da kiss ɗin su Inna...
Wani takaici ne ya turnuƙe saurayin ganin irin cakumar da Inna ta yiwa rigarsa, domin kuwa ta yiwa rigar wani irin ɗiban karan mahaukaciya.
" Zamani kenan mura ta tadda kwaɗo wallahi sai kin san wanda kika yiwa wannan riƙon kamar kin samu wuyan saniya, wallahi sai kin banbance tsakanin kiɗa da karatu" Cewar saurayin a ransa yana ƙiyasta irin cin mutuncin da zai yiwa Inna domin huce takaicin haushin abin da ta masa za ta sanya duk inda ya yi ake nuna shi.
Hannu ya sanya ya rungomo Inna, wani irin zare ido Inna ta yi dan duk tunaninta faÉ—e zai mata
"Wallahi sai na kai amarcina gidan mijina dan yanzu layin Jauro ne, na Malam ya wuce kai kuwa baka isa ka sha zuma ta ba" Cewar Inna tana ƙoƙarin ƙwatar kanta.
Kafin ta gama tantancewa sai ji ta yi ya sakata daga rungumar da ya mata ya finciki ɗaurin ɗankwalinta haɗe da hular gashin da aka saka mata, sai ga kan Inna a bainan nasi, gabaɗaya kan a ƙwaiƙwaye yake babu ma kitso saboda kan ba zai kitsu ba, duk ya zube, dan dama ƙawarta Shattu ke haɗawa da tsumma tana mata zanen hausa shi ne yanzu aka sayi hula za a yi ƙara'in biki da ita.Yana yin jifa da hula da ɗan kwalinya kama wuyan rigarta sai da ya daidaici saitin ƙirjinta ya kama ya yaga rigar har wajen saitin cibiyarta, tana ƙoƙarin kare wurin saurayin nan ya yi ido biyu da bireziyarta da ke shaƙe da fanfas ɗin yara, da alama ciko ta yi kuma cikon daban nonon da ban, dan haka ai bai yi wata-wata ba ya sa hannu ya fisgi hannun bireziyar duka biyu sai kuwa ta cire sai ga fanfas suna faɗowa kamar ƙwallon mangwaro na faɗowa daga bishiya, dan guda huɗu ne ragas ko ina biyu ta saka dan cikon ya yi tudu. Inna kuwa ganin fanfas a ƙasa a zube kuma jin wurin ya ɗauki ihu har da amsa kuwwa sannan sai ta ji nonuwan nata na reto kamar lilon wasan yara domin ya fito daga bireziya babu mafakar fakewa dan haka bata yi wata-wata ba ta durƙushe hannunta riƙe gam a ƙirjinta.
Jauro daga inda yake ganin abin da ke faruwa sai kuwa ya yi wani tsalle kamar jakican sai gashi ya yi dirar mikiya a gaban wasu ƙarafe da ake ajiyewa a wajen daga can gefe, guda ɗaya ya warto ya taho rai a matuƙar ɓace dan shi ba komai bane ya ɓata masa rai irin yadda saurayin nan ya rungume Inna tare da kai hannunsa jikin bireziyarta wannan ne ya tada masa wani kishi marar misali
Saurayin nan ganin irin yadda Jauro ya taho a matuƙar fusace kamar kumurcin maciji hakan ya sanya ya bawa kansa shawarar cika wandonsa da iska dan idan ya tsaya bafulatanin nan ya far masa sai ya kwanta asibiti in ma bai kai shi kushewa ba. Da mugun gudu ya bar wajen Inna yana haɗawa da tsalle, haka ma Jauro ya mara masa baya ɗauke da ƙarfen, a ransa yana raya wa a ransa cewa ba zai yiwu ba kura da aiki gardi da shan bugu. Yadda suka zuba a na kare kamar ibro ya biyo ƙulu Allah jkn rai, haka suka falfala kamar sun ci ƙafar kare. Wurin kuwa ya karaɗe da ihu MC kuwa sai cewa yake
"Jama'a a yi haƙuri wuri fa ya hargitse an samu wani saurayi ya kaiwa amarya farmaki, dan haka ango ya fusata ya ga ba zai iya haƙuri ba bare ya jure ya bi bayan saurayin sai yadda hali ya yi"
Samarin nan kuwa sai cewa suke
"Sai ka cimmasa ango ya za a yi kai baka ga amaryarka ba, shi ya gane maka, har da rungumeta ya yi kamar shi ne angon" Haka suke faɗa suna ihu, dan su zuga Jauro dan ko tarkar riƙe masa saurayin babu wanda ya yi niyyar yi dan dama sun fi so su ga yadda wasan zai kasance dan su sha dariya.
Sai faman keta gudu suke Jauro da saurayin nan, dan saurayin na fita ya sha wata uwar kwana bai bi kan titi ba sai ya keta wata unguwa shi kuwa Jauro ya take masa baya dan Jauro tun daga ƙofar wajen taron ya sille takalmansa dan ba ya jin gudun zai yiwu da takalmi, ga farar rigar nan da ta sha manja fuskar nan ban da idanunsa a fuskar babu inda manjan bai taɓa ba amma a haka yake zabga gudun famfalaƙi sai ƙara haɗa gumi yake. Saurayin nan kuwa sai waiwaye yake idan ya hango tazarar da ya bawa Jauron sai ya ƙilƙili da dariya amma dan ƙarfin hali Jauro ba ya ganin tazarar da ya bashi kawai burinsa ya same shi ya kwantar da shi da ƙarfen nan.
"Wallahi ba zai yiwu ba aradun Allah, ina zan yarda mai ɗakko katifar amarya da ban mai morarta ma da ban" Ya faɗa a ransa yana ƙara wuyar gudu dan ya ga ya ɗan fara taddo saurayin duk da duk inda suka gifta sai kallonsu ake.
Sai da suka kusa zuwa wani wuri inda akwai taron jama'a saurayin ya rage zabga gudun sai da ya bari Jauro ya kusa ƙarasowa sai ya ware murya ya ce
"Ihu mahaukaci jama'a duka yake kun ga da ya damƙe ni yadda ya ɓata mini riga da manjan jikinsa, ai mutane na jin furucinsa sai kowa ya fara guduwa wasu suna shiga gida suna rufewa dan ganin yanayin jikin Jauro ga manja a jikinsa da fuskarsa ga babu takalmi ga ya riƙo ƙarfe kowa sai ya fara ta kansa a ƙarshe dai ya ma rasa inda saurayin ya yi dan ya ɓace masa ga mutane sai kiransa suke mahaukaci ba wanda ke sauraronsa bare ya faɗa musu lafiyarsa ƙalaw.
Daga ƙarshe dai ya zo wucewa zai koma wajen taron, ta wani ƙaramin lungu sai ji ya yi, ƙum an sakar masa wani ƙaton bokitin fanti a kansa, daga saman wata katanga yana ɗagowa ya yi ido huɗu da saurayin nan shi da wani abokinsa, kan ka ce kwabo sun diro daga katangar kamar wasu birrai sun sheƙa a guje, haka ya yi ta danƙara musu Allah ya isa, har da ɗan kukansa ya matse a hanya dan kansa har ya yi wani ƙaton ƙullutu a tsakiyar kan nasa.
A hanyar dawo wa yana tafiya amma wani ƙululun baƙincikin kishin abin da aka yiwa Delunsa na runguma da taɓa bireziyarta, da kuma bokitin fantin da ya sha a tsakiyar kai duk su ne suka haɗe masa goma da ashirin .
"Gaskiya mutanen birni basu da kara, yanzu wannan da a ce a rugarmu ne abin nan ya faru da kowa sanda zai ɗakko a bi kwarton nan da ya rungume mini amarya, amma a nan sai ihu suke babu wanda ya yi kataɓus bare ya taimaka mini, sai ni kaɗai gashi a ƙarshe sun rafka mini bokiti kamar wanda aka aiko su duk da akwai gashin furfura a kaina amma sai da bokitin ya mini illa" Cewar Jauro a ransa lokacin da ya taho a hanya har wani ƙwallar takaici ne ya taru a idanunsa dan ba a taɓa ce masa ko da taɓi-taɓi ba amma yanzu gashi an kira shi mahaukaci sanadin ƘARA'IN aurensa da Delu. A haka ya ƙaraso bakin get ɗin inda ya watsar da takalmansa, a hannu ya ɗauka dan haushi ma ya hana shi ya saka a ƙafarsa.
ƘARA'IN INNA DELU
Page 1⃣7⃣➡1⃣8⃣
Maganar Inna ta tsaya ne sanadin ganin wani saurayi mai ƙarfin hali, wanda ya zo har gabanta y tsaya yana mata video dan shi daga can inda yake videon ba ya ɗaukuwa shi yasa ya zo gabanta dan yau ya yi alƙawari duk wata lfr sadarwa sai ya ɗorata yadda ta yi jargaf da manjan nan, ko kwalliyar da aka mata ba a gani manja ya rufe ta ruf.
Kallo Inna ta ƙare masa ta ganshi sanye yake da garar riga irin mai farin nan tass sai baƙin wando, cikin sanɗa da ƙarasa gabansa shi kuma ya maida hankali cikin wayar dan da ya fara ganin tana matsowa a a cikin wayar sai ya ganta kamar aljana kuma bai yi zaton wurinsa ta nufa ba ya ɗauka ta kammala jawabin ne za ta bar wajen.
Inna Delu na ƙarasowa ta miƙa hannu cikin zafin nama ta damƙo wuyan rigar saurayin nan, saurayi na ɗaukan video sai ji ya yi an rafkoshi kamar wanda ɗan sanda ya kama ɓarawo, ɗago kan da zai yi aikuwa ya sauke su a kan Inna Delu da manjan nan sharkaf sai ɗiga take kamar wacce ta yi noman kwakwar manja.
Wani takaici ne ya lulluɓeshi ganin hannunta da manja amma ta kama masa riga, rigar ma fara, wani irin zabura ya yi zai fara mata rashin kunya, Inna kuwa hannu ta kai ta damƙo hannayensa ta haɗa wuri ɗaya ta damƙe dama ɗan siriri da shi kamar sandar rake, bakinsa dai ya buɗa zai fara magana aikuwa Inna ta saki ɗaya hannun nasa ta gwabje masa baki ta janyoshi ta wanka masa mari sannan ta kai masa kyawawan ranƙwashi guda uku.
"Allah ya isa n...
Ai kafin ya ƙarasa Inna ta janyoshi jikinta ta rungume sai da ta tabbatar rigarsa fara ta gama samun manja har fuskarsa marabarsu da Innar yanzu kaɗan ne dan shi ma kamar wanda ya shafa shuni amma na manja. Ihu aka ɗauka a wajen wanda har ya fi na lokacin faɗuwa da kiss ɗin su Inna...
Wani takaici ne ya turnuƙe saurayin ganin irin cakumar da Inna ta yiwa rigarsa, domin kuwa ta yiwa rigar wani irin ɗiban karan mahaukaciya.
" Zamani kenan mura ta tadda kwaɗo wallahi sai kin san wanda kika yiwa wannan riƙon kamar kin samu wuyan saniya, wallahi sai kin banbance tsakanin kiɗa da karatu" Cewar saurayin a ransa yana ƙiyasta irin cin mutuncin da zai yiwa Inna domin huce takaicin haushin abin da ta masa za ta sanya duk inda ya yi ake nuna shi.
Hannu ya sanya ya rungomo Inna, wani irin zare ido Inna ta yi dan duk tunaninta faÉ—e zai mata
"Wallahi sai na kai amarcina gidan mijina dan yanzu layin Jauro ne, na Malam ya wuce kai kuwa baka isa ka sha zuma ta ba" Cewar Inna tana ƙoƙarin ƙwatar kanta.
Kafin ta gama tantancewa sai ji ta yi ya sakata daga rungumar da ya mata ya finciki ɗaurin ɗankwalinta haɗe da hular gashin da aka saka mata, sai ga kan Inna a bainan nasi, gabaɗaya kan a ƙwaiƙwaye yake babu ma kitso saboda kan ba zai kitsu ba, duk ya zube, dan dama ƙawarta Shattu ke haɗawa da tsumma tana mata zanen hausa shi ne yanzu aka sayi hula za a yi ƙara'in biki da ita.Yana yin jifa da hula da ɗan kwalinya kama wuyan rigarta sai da ya daidaici saitin ƙirjinta ya kama ya yaga rigar har wajen saitin cibiyarta, tana ƙoƙarin kare wurin saurayin nan ya yi ido biyu da bireziyarta da ke shaƙe da fanfas ɗin yara, da alama ciko ta yi kuma cikon daban nonon da ban, dan haka ai bai yi wata-wata ba ya sa hannu ya fisgi hannun bireziyar duka biyu sai kuwa ta cire sai ga fanfas suna faɗowa kamar ƙwallon mangwaro na faɗowa daga bishiya, dan guda huɗu ne ragas ko ina biyu ta saka dan cikon ya yi tudu. Inna kuwa ganin fanfas a ƙasa a zube kuma jin wurin ya ɗauki ihu har da amsa kuwwa sannan sai ta ji nonuwan nata na reto kamar lilon wasan yara domin ya fito daga bireziya babu mafakar fakewa dan haka bata yi wata-wata ba ta durƙushe hannunta riƙe gam a ƙirjinta.
Jauro daga inda yake ganin abin da ke faruwa sai kuwa ya yi wani tsalle kamar jakican sai gashi ya yi dirar mikiya a gaban wasu ƙarafe da ake ajiyewa a wajen daga can gefe, guda ɗaya ya warto ya taho rai a matuƙar ɓace dan shi ba komai bane ya ɓata masa rai irin yadda saurayin nan ya rungume Inna tare da kai hannunsa jikin bireziyarta wannan ne ya tada masa wani kishi marar misali
Saurayin nan ganin irin yadda Jauro ya taho a matuƙar fusace kamar kumurcin maciji hakan ya sanya ya bawa kansa shawarar cika wandonsa da iska dan idan ya tsaya bafulatanin nan ya far masa sai ya kwanta asibiti in ma bai kai shi kushewa ba. Da mugun gudu ya bar wajen Inna yana haɗawa da tsalle, haka ma Jauro ya mara masa baya ɗauke da ƙarfen, a ransa yana raya wa a ransa cewa ba zai yiwu ba kura da aiki gardi da shan bugu. Yadda suka zuba a na kare kamar ibro ya biyo ƙulu Allah jkn rai, haka suka falfala kamar sun ci ƙafar kare. Wurin kuwa ya karaɗe da ihu MC kuwa sai cewa yake
"Jama'a a yi haƙuri wuri fa ya hargitse an samu wani saurayi ya kaiwa amarya farmaki, dan haka ango ya fusata ya ga ba zai iya haƙuri ba bare ya jure ya bi bayan saurayin sai yadda hali ya yi"
Samarin nan kuwa sai cewa suke
"Sai ka cimmasa ango ya za a yi kai baka ga amaryarka ba, shi ya gane maka, har da rungumeta ya yi kamar shi ne angon" Haka suke faɗa suna ihu, dan su zuga Jauro dan ko tarkar riƙe masa saurayin babu wanda ya yi niyyar yi dan dama sun fi so su ga yadda wasan zai kasance dan su sha dariya.
Sai faman keta gudu suke Jauro da saurayin nan, dan saurayin na fita ya sha wata uwar kwana bai bi kan titi ba sai ya keta wata unguwa shi kuwa Jauro ya take masa baya dan Jauro tun daga ƙofar wajen taron ya sille takalmansa dan ba ya jin gudun zai yiwu da takalmi, ga farar rigar nan da ta sha manja fuskar nan ban da idanunsa a fuskar babu inda manjan bai taɓa ba amma a haka yake zabga gudun famfalaƙi sai ƙara haɗa gumi yake. Saurayin nan kuwa sai waiwaye yake idan ya hango tazarar da ya bawa Jauron sai ya ƙilƙili da dariya amma dan ƙarfin hali Jauro ba ya ganin tazarar da ya bashi kawai burinsa ya same shi ya kwantar da shi da ƙarfen nan.
"Wallahi ba zai yiwu ba aradun Allah, ina zan yarda mai ɗakko katifar amarya da ban mai morarta ma da ban" Ya faɗa a ransa yana ƙara wuyar gudu dan ya ga ya ɗan fara taddo saurayin duk da duk inda suka gifta sai kallonsu ake.
Sai da suka kusa zuwa wani wuri inda akwai taron jama'a saurayin ya rage zabga gudun sai da ya bari Jauro ya kusa ƙarasowa sai ya ware murya ya ce
"Ihu mahaukaci jama'a duka yake kun ga da ya damƙe ni yadda ya ɓata mini riga da manjan jikinsa, ai mutane na jin furucinsa sai kowa ya fara guduwa wasu suna shiga gida suna rufewa dan ganin yanayin jikin Jauro ga manja a jikinsa da fuskarsa ga babu takalmi ga ya riƙo ƙarfe kowa sai ya fara ta kansa a ƙarshe dai ya ma rasa inda saurayin ya yi dan ya ɓace masa ga mutane sai kiransa suke mahaukaci ba wanda ke sauraronsa bare ya faɗa musu lafiyarsa ƙalaw.
Daga ƙarshe dai ya zo wucewa zai koma wajen taron, ta wani ƙaramin lungu sai ji ya yi, ƙum an sakar masa wani ƙaton bokitin fanti a kansa, daga saman wata katanga yana ɗagowa ya yi ido huɗu da saurayin nan shi da wani abokinsa, kan ka ce kwabo sun diro daga katangar kamar wasu birrai sun sheƙa a guje, haka ya yi ta danƙara musu Allah ya isa, har da ɗan kukansa ya matse a hanya dan kansa har ya yi wani ƙaton ƙullutu a tsakiyar kan nasa.
A hanyar dawo wa yana tafiya amma wani ƙululun baƙincikin kishin abin da aka yiwa Delunsa na runguma da taɓa bireziyarta, da kuma bokitin fantin da ya sha a tsakiyar kai duk su ne suka haɗe masa goma da ashirin .
"Gaskiya mutanen birni basu da kara, yanzu wannan da a ce a rugarmu ne abin nan ya faru da kowa sanda zai ɗakko a bi kwarton nan da ya rungume mini amarya, amma a nan sai ihu suke babu wanda ya yi kataɓus bare ya taimaka mini, sai ni kaɗai gashi a ƙarshe sun rafka mini bokiti kamar wanda aka aiko su duk da akwai gashin furfura a kaina amma sai da bokitin ya mini illa" Cewar Jauro a ransa lokacin da ya taho a hanya har wani ƙwallar takaici ne ya taru a idanunsa dan ba a taɓa ce masa ko da taɓi-taɓi ba amma yanzu gashi an kira shi mahaukaci sanadin ƘARA'IN aurensa da Delu. A haka ya ƙaraso bakin get ɗin inda ya watsar da takalmansa, a hannu ya ɗauka dan haushi ma ya hana shi ya saka a ƙafarsa.
ƘARA'IN INNA DELU
Page 1⃣7⃣➡1⃣8⃣