Sashe 22
Kaddara Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta turo baki. Sannan ta buga ƙafa a ƙasa. Ta juya ta zagaya ɗayan ɓangaren, ta shiga gidan gaba tana hawaye. Shi ma motar ya shiga. Sannan ya miƙa mata jakar chocolate ɗin hannunsa. Ta ɗauka tana ta ɓata rai. Wanda suke hannunta ma a ciki ta sa. Ta kame kanta gefe, ta ƙi yin magana sai hawayen da take.
Shi ma bai takura da sai ta yi maganar ba. Har sai da suka iso Bawri. Sannan ya tambayeta layin gidansu a Dutsen Alhaji. Sai a sannan ne ta yi magana. Kuma suna isa ƙofar gidan ta shiga ƙoƙarin buɗewa ta fita.
“Baby girl!”
Cak ta tsaya daga shirin fitar da take. Saboda wani abu da ya faɗo a cikin kanta. A gaba ɗayan rayuwarta mahaifiyarta ce kaɗai ke kiranta da sunan. Hakan ya sa ta juyo ta kalle shi.
“Kukan na mi ye?”
Ta kai hannu ta goge ƙwalla tana ci gaba da tura baki.
“Ba kai ne ka min tsawa ba”
Kansa ya girgiza.
“Gardama kika yi. And i hate stubbornness. Amma ki yi haƙuri”
Ta ci gaba da tura baki tana kumbura shi.
“Ki haƙura da wuri, saboda kar ki sake shigo min ciki tunani ki fitineni”
Ta kuma kallonsa.
“To na haƙura. Kuma na gode”
Tana kaiwa nan ta fice daga motar. Zuciyarta cike taf da farin cikin wannan kyauta da ya mata ta chocolate da cookies. Saboda abu ne da ta daɗe ba ta sa a ido ba, ballantana har ta kai ga sha. A ɗaya ɓangaren kuma tana cike da fargabar batun rage ma'aikata da za ayi a boutique ɗinsu. Shi ma wannan batu ya hana zuciyarta sukuni. Har ta shige gidan Mu'az na kallonta yana murmushi.
“Rigima Baby girl”
Ya faɗa yana shafa gajerar sumar kansa. Yana shirin tayar da motar kiran Faruk ya shigo wayarsa. Hakan ya sa ya fasa ya ɗaga wayar.
“Kaigama what's up?”
Daga ɗayan bangaren Faruk yace.
“Yanzu Muktar ya kirani. Ya sanar min da cewa yana son ganinmu ni da kai da gaggawa!”
Mu'az ya ɗan sosa kan hancinsa yana duba agogo.
“Okay a ina zan sameka?”
“Ina gida. Ka zo ka ɗaukeni sai mu wuce headquartern”
“Okay”
Daga haka ya sauƙe wayar. Sannan ya tayar da motar ya nufi gidan Faruk.
MUKTAR POV.
Zaune yake cikin office ɗinsa. Yayin da Faruk da Mu'az ke zaune a kan kujerun dake gaban teburinsa. Tun da suka zo headuatern, suka ritsa shi da tambayoyi na me ya same shi.
Saboda ganin raunukan da suke a jikinsa. Hannunsa na hagu da yake da tabbacin ya karye ya kuwa karye ɗin. Dan yanzu haka sai da aka yi wa hannun ɗori a asibiti. Ban da sauran wuraren da suka raunatu a jikinsa.
Saboda jiya har ƙarfe sha biyu suna asibiti shi da Walid da Ali. Kuma duk da yanda likitocin suka so ya zauna a asibitin ƙi ya yi. Saboda ba ya jin zai bar abin da ya faru ya tafi a banza. Dole ne ya ɗauki matakin gaggawa, a yanzu sun kuskure wurin halaka shi, wata ƙila nan gaba Allah zai iya basu nasara.
Ba mutuwarsa ce abar tsoro a wurinsa ba. Ya san cewa ko wani mai rai ƙarshen rayuwarsa a duniya mutuwar ce. Kamar dai yanda mahaifinsa ya rasu ya bar su shi da ƙaninsa da kuma mahaifiyarsu. Abin da zai fi ƙona masa rai shi ne da zai mutu ya bar Mariya da abokin aikata kisanta a raye, suna cutar Faruk da kuma sauran al'umma...
“Mukhy!”
Mu'az ya kirashi da ɗan ƙarfi, ganin kamar tunaninsa ya yi nisa da gangar jikinsa. Hakan ya sa ya dube shi da sauri yana amsawa.
“Na'am!”
“Ina ka tafi?”
Mu'az ya tambaya yana watsa hannu a iska. Muktar ya girgiza kansa yana ɗora hannunsa a kan table ɗin dake gabansu. Ya furzar da huci kaɗan. Sannan ya dubi Faruk, ya dawo ya dubi Mu'az.
“Kaigama!”
Faruk ya gyara zama yana faɗin.
“Na'am Mukhy!”
Muktar ya kalli Mu'az.
“MJ!”
“Umm!”
Shi ma ya amsa. Muktar ya jinjina kansa. Yana son sanin ta inda zai fara musu bayani a kan wata makusanciyarsu ita ce me laifin da suka daɗe suna nema ruwa a jallo.
“Kaigama! MJ!. Ba na so na zama mutum na farko da zaisanar da ku wannan mummunan labarin!... Dan haka zai fi kyau ku kalla da idonku, kafin bayanina ya biyo baya!...”
Su dai kallonsa kawai suke da rashin fahimta. Kuma duk sun ƙagu ya faɗa musu dalilinsa na yin kiransu. Ba su ce komai ba har ya juyo musu screen ɗin laptop ɗin dake kan teburin. Sannan ya naɗe hannunsa yana kallon fuskokinsu.
A lokacin da videon ya kai ƙarshe. Ba a ce a tsakanin Faruk da Mu'az wa ya fi wani shiga shock ba. Kallon juna kawai suka yi baki a sake. Kafin Mu'az ya yi ƙarfin halin kai hannunsa ya sake kunnawa.
Tunaninsa, zuciyarsa, da duk wani abu me faɗa a ji a jikinsa na faɗin wannan ba ƙanwarsa ba ce. Wannan ba Mariya ba ce. Wannan ba ƙanwarsa da ta fi kowa acikin ƙannensa soyiwa a ransa ba ce. Sam ba ita ba ce!... Ya ma za ayi ta kasance Mariya Jibrin Gimba?.
Shi dai Faruk ba irin wannan tunanin yake ba. A kallo ɗaya da ya yi wa videon ya gane matarsa. Saboda ya santa, ya kuma san wacece ita. Amma abin da bai gane ba shi ne, me ya sa Mariya za ta sace Munira, har ta kai ga kasheta?.
Sannan wannan mutumin da suke tare da shi, waye shi?. Me zai sa matarsa da ba za ka yi tunanin idan ka sa mata hannu a baki ba za ta ciza ba ta yi kisan kai?... Yanzu har Mariya za ta iya kashe wani?. Me ya sa?. Me zai sa ta kashe Munira?. A tare suka sake kallon juna, sannan suka kalli Muktar da shi ma yake kallonsu.
“Na san kallon wannan videon zai sa tarin tambayoyi a cikin kawunanku... Tabbas wannan Mariya ce. Matarka Kaigama, ƙanwarka MJ. Kuma...”
Bai kai ga ƙarasawa ba. Mu'az ya miƙe tsaye, sannan ya shaƙo wuyansa ya miƙar da shi tsaye yana jin kamar ya kashe shi ya huta. Sai huci yake yana jin zuciyarsa na zafi.
"How dare you talk about my sister in that tone!?”
Ya faɗi a kausashe. Muktar bai ce komai ba, kuma bai yi yunƙurin ƙwatar kansa ba. Saboda ya san ko shi aka zo aka samu da zancen cewa Walid ya yi kisan kai zai iya shiga cikin halin. Da ƙyar Faruk ya cire hannun Mu'az a wuyan Muktar, ya ja shi baya ba tare da ya ce masa komai ba.
“I can't believe he thinks Mariya is responsible for Munira's death!... And... and!”
Ya kasa ƙarasawa yana jin idonsa na cika da ƙwalla. Amma kuma ba ta zubo ba. Har ji yake numfashinsa na shirin ɗaukewa. Ya yi shiru kawai, yana fitar da iska daga huhunsa da ƙyar, kamar me ciwon zuciya.
“Get seated”
Faɗin Faruk yana zaunar da shi a kan kujera. Zaman ya yi yana dafe kansa da ya fara sarawa. Da ma shi haka yake, daga zarar ransa ya ɓaci zai fita hayyacinsa gaba ɗaya, idan bai yi sa'a ba ma sai ya kwanta jinya.
“Ina jinka Muktar”
Faruk ya haɗe kalaman yana haɗiyar yawu da ƙyar. Saboda jin wani abu ya toshe masa maƙoshi. Shi bai faɗa cikinsa ba, kuma bai fito ta bakinsa ba. Muktar ya zauna, sannan ya ci gaba da faɗin.
“... Na samo wannan videon ne a unguwar da aka sace Munira. Na same shi ne daga wurin wani yaro da a lokacin da aka sace Munira ya yi recording videon... A lokacin da na samu vedion ban yi ƙoƙarin sanar da kowa ba face Ali mataimakina, wanda tare da shi muka je. Abin da ya ba ni mamaki shi ne a wannan ranar wani ya biyoni gida yana ƙoƙarin kasheni. Amma Allah ya taimakeni na tsira. Sai dai kuma a daren jiya Mariya da wannan mutumin na cikin videon ne suka zo har unguwar mu. Kuma na gansu, sannan su ne suka bigeni da mota. Har na samu waɗannan raunikan na jikina... Shi ya sa na ce ba zan yi ƙasa a gwuiwa wurin sanar da ku wannan gaskiyar ba!”
Faruk ya dafe kansa. Tunanin abin da ya faru tsakaninsu jiya ya dawo masa. Ke nan jiya da daddare kashe Muktar ta tafi?. Innalillahi wa inna ialaihi raji'un. Ya furta yana murza goshinsa. Mu'az kuwa bai sake cewa uffan ba. Sai yatsun hannunsa da yake murzawa idonsa na sauya kala zuwa ja.
-------------------------------
_Wato a wasu lokutan. Abubuwan da ba mu yi zato ba su ne suka cika faruwa da mu._
_Irin haka ce ta faru ga Faruk da Mu'az._
_Shin! Wani dabi ne zai ɓarke a haɗejia, tsakanin Gambo da Maimuna da kuma Auwwa?._
_Shin, wani hali kuke tunanin Halima za ta shiga idan aka sallameta a aiki?._
_Me zai faru tsakanin Mariya da Faruk?._
_Sannan Mu'az, dan shi kam ya fi Faruk fusata._
_Yaya Mariya za ta yi domin wanke kanta a idon yayanta da kuma mijinta, da ma sauran jama'ar duniya da za su sani?._
_Shin, kuna ganin cewa, kisan Munira zai zama kisa na ƙarshe da Mariya za ta aikata?. Ko za ta ci gaba da zama a ƙungiyarsu ta bayin Shaiɗan!?._
_Hummm!_
_Akwai magana. To, ga duk wanda yake son sanin amsoshin waɗannan tambayoyin, sai ya biya ₦300. Tun kafin tafiyar nan ta wuce ku._
_Kun san daga ganin tafiyar nan ba ta wasa ba ce, dan har yanzu ba mu yi komai ba. Kuma ina me muku tabbacin ba za ku yi da na sanin siyan wanna littafi ba. Kun san alƙalamin Candy akwai suger._
••• ••• •••
*Zan yi amfai da wannan damar, wurin gode muku, SALMANIANS. Kun san da cewa ku ne on top a ƙalbina. I love you like wujiga-wujiga. Ina sonku fiye da irin son da kuke min*
Ga duk wanda ya shirya dan ayi tafiyar nan da shi, zai ₦300 kacal. Ta wannan account details ɗin da zan rubuta. Idan kuma har ya zama complete document sai dai ku biya ₦500.
5487270431
Salma Isah
Moniepoint
Shaidar biya kuma via.
08130172702.
Sai na ji ku SALMANIANS.
Best regards.
*SALMA AHMAD ISAH*
*(CANDY🦋)*
2024...
Shi ma bai takura da sai ta yi maganar ba. Har sai da suka iso Bawri. Sannan ya tambayeta layin gidansu a Dutsen Alhaji. Sai a sannan ne ta yi magana. Kuma suna isa ƙofar gidan ta shiga ƙoƙarin buɗewa ta fita.
“Baby girl!”
Cak ta tsaya daga shirin fitar da take. Saboda wani abu da ya faɗo a cikin kanta. A gaba ɗayan rayuwarta mahaifiyarta ce kaɗai ke kiranta da sunan. Hakan ya sa ta juyo ta kalle shi.
“Kukan na mi ye?”
Ta kai hannu ta goge ƙwalla tana ci gaba da tura baki.
“Ba kai ne ka min tsawa ba”
Kansa ya girgiza.
“Gardama kika yi. And i hate stubbornness. Amma ki yi haƙuri”
Ta ci gaba da tura baki tana kumbura shi.
“Ki haƙura da wuri, saboda kar ki sake shigo min ciki tunani ki fitineni”
Ta kuma kallonsa.
“To na haƙura. Kuma na gode”
Tana kaiwa nan ta fice daga motar. Zuciyarta cike taf da farin cikin wannan kyauta da ya mata ta chocolate da cookies. Saboda abu ne da ta daɗe ba ta sa a ido ba, ballantana har ta kai ga sha. A ɗaya ɓangaren kuma tana cike da fargabar batun rage ma'aikata da za ayi a boutique ɗinsu. Shi ma wannan batu ya hana zuciyarta sukuni. Har ta shige gidan Mu'az na kallonta yana murmushi.
“Rigima Baby girl”
Ya faɗa yana shafa gajerar sumar kansa. Yana shirin tayar da motar kiran Faruk ya shigo wayarsa. Hakan ya sa ya fasa ya ɗaga wayar.
“Kaigama what's up?”
Daga ɗayan bangaren Faruk yace.
“Yanzu Muktar ya kirani. Ya sanar min da cewa yana son ganinmu ni da kai da gaggawa!”
Mu'az ya ɗan sosa kan hancinsa yana duba agogo.
“Okay a ina zan sameka?”
“Ina gida. Ka zo ka ɗaukeni sai mu wuce headquartern”
“Okay”
Daga haka ya sauƙe wayar. Sannan ya tayar da motar ya nufi gidan Faruk.
MUKTAR POV.
Zaune yake cikin office ɗinsa. Yayin da Faruk da Mu'az ke zaune a kan kujerun dake gaban teburinsa. Tun da suka zo headuatern, suka ritsa shi da tambayoyi na me ya same shi.
Saboda ganin raunukan da suke a jikinsa. Hannunsa na hagu da yake da tabbacin ya karye ya kuwa karye ɗin. Dan yanzu haka sai da aka yi wa hannun ɗori a asibiti. Ban da sauran wuraren da suka raunatu a jikinsa.
Saboda jiya har ƙarfe sha biyu suna asibiti shi da Walid da Ali. Kuma duk da yanda likitocin suka so ya zauna a asibitin ƙi ya yi. Saboda ba ya jin zai bar abin da ya faru ya tafi a banza. Dole ne ya ɗauki matakin gaggawa, a yanzu sun kuskure wurin halaka shi, wata ƙila nan gaba Allah zai iya basu nasara.
Ba mutuwarsa ce abar tsoro a wurinsa ba. Ya san cewa ko wani mai rai ƙarshen rayuwarsa a duniya mutuwar ce. Kamar dai yanda mahaifinsa ya rasu ya bar su shi da ƙaninsa da kuma mahaifiyarsu. Abin da zai fi ƙona masa rai shi ne da zai mutu ya bar Mariya da abokin aikata kisanta a raye, suna cutar Faruk da kuma sauran al'umma...
“Mukhy!”
Mu'az ya kirashi da ɗan ƙarfi, ganin kamar tunaninsa ya yi nisa da gangar jikinsa. Hakan ya sa ya dube shi da sauri yana amsawa.
“Na'am!”
“Ina ka tafi?”
Mu'az ya tambaya yana watsa hannu a iska. Muktar ya girgiza kansa yana ɗora hannunsa a kan table ɗin dake gabansu. Ya furzar da huci kaɗan. Sannan ya dubi Faruk, ya dawo ya dubi Mu'az.
“Kaigama!”
Faruk ya gyara zama yana faɗin.
“Na'am Mukhy!”
Muktar ya kalli Mu'az.
“MJ!”
“Umm!”
Shi ma ya amsa. Muktar ya jinjina kansa. Yana son sanin ta inda zai fara musu bayani a kan wata makusanciyarsu ita ce me laifin da suka daɗe suna nema ruwa a jallo.
“Kaigama! MJ!. Ba na so na zama mutum na farko da zaisanar da ku wannan mummunan labarin!... Dan haka zai fi kyau ku kalla da idonku, kafin bayanina ya biyo baya!...”
Su dai kallonsa kawai suke da rashin fahimta. Kuma duk sun ƙagu ya faɗa musu dalilinsa na yin kiransu. Ba su ce komai ba har ya juyo musu screen ɗin laptop ɗin dake kan teburin. Sannan ya naɗe hannunsa yana kallon fuskokinsu.
A lokacin da videon ya kai ƙarshe. Ba a ce a tsakanin Faruk da Mu'az wa ya fi wani shiga shock ba. Kallon juna kawai suka yi baki a sake. Kafin Mu'az ya yi ƙarfin halin kai hannunsa ya sake kunnawa.
Tunaninsa, zuciyarsa, da duk wani abu me faɗa a ji a jikinsa na faɗin wannan ba ƙanwarsa ba ce. Wannan ba Mariya ba ce. Wannan ba ƙanwarsa da ta fi kowa acikin ƙannensa soyiwa a ransa ba ce. Sam ba ita ba ce!... Ya ma za ayi ta kasance Mariya Jibrin Gimba?.
Shi dai Faruk ba irin wannan tunanin yake ba. A kallo ɗaya da ya yi wa videon ya gane matarsa. Saboda ya santa, ya kuma san wacece ita. Amma abin da bai gane ba shi ne, me ya sa Mariya za ta sace Munira, har ta kai ga kasheta?.
Sannan wannan mutumin da suke tare da shi, waye shi?. Me zai sa matarsa da ba za ka yi tunanin idan ka sa mata hannu a baki ba za ta ciza ba ta yi kisan kai?... Yanzu har Mariya za ta iya kashe wani?. Me ya sa?. Me zai sa ta kashe Munira?. A tare suka sake kallon juna, sannan suka kalli Muktar da shi ma yake kallonsu.
“Na san kallon wannan videon zai sa tarin tambayoyi a cikin kawunanku... Tabbas wannan Mariya ce. Matarka Kaigama, ƙanwarka MJ. Kuma...”
Bai kai ga ƙarasawa ba. Mu'az ya miƙe tsaye, sannan ya shaƙo wuyansa ya miƙar da shi tsaye yana jin kamar ya kashe shi ya huta. Sai huci yake yana jin zuciyarsa na zafi.
"How dare you talk about my sister in that tone!?”
Ya faɗi a kausashe. Muktar bai ce komai ba, kuma bai yi yunƙurin ƙwatar kansa ba. Saboda ya san ko shi aka zo aka samu da zancen cewa Walid ya yi kisan kai zai iya shiga cikin halin. Da ƙyar Faruk ya cire hannun Mu'az a wuyan Muktar, ya ja shi baya ba tare da ya ce masa komai ba.
“I can't believe he thinks Mariya is responsible for Munira's death!... And... and!”
Ya kasa ƙarasawa yana jin idonsa na cika da ƙwalla. Amma kuma ba ta zubo ba. Har ji yake numfashinsa na shirin ɗaukewa. Ya yi shiru kawai, yana fitar da iska daga huhunsa da ƙyar, kamar me ciwon zuciya.
“Get seated”
Faɗin Faruk yana zaunar da shi a kan kujera. Zaman ya yi yana dafe kansa da ya fara sarawa. Da ma shi haka yake, daga zarar ransa ya ɓaci zai fita hayyacinsa gaba ɗaya, idan bai yi sa'a ba ma sai ya kwanta jinya.
“Ina jinka Muktar”
Faruk ya haɗe kalaman yana haɗiyar yawu da ƙyar. Saboda jin wani abu ya toshe masa maƙoshi. Shi bai faɗa cikinsa ba, kuma bai fito ta bakinsa ba. Muktar ya zauna, sannan ya ci gaba da faɗin.
“... Na samo wannan videon ne a unguwar da aka sace Munira. Na same shi ne daga wurin wani yaro da a lokacin da aka sace Munira ya yi recording videon... A lokacin da na samu vedion ban yi ƙoƙarin sanar da kowa ba face Ali mataimakina, wanda tare da shi muka je. Abin da ya ba ni mamaki shi ne a wannan ranar wani ya biyoni gida yana ƙoƙarin kasheni. Amma Allah ya taimakeni na tsira. Sai dai kuma a daren jiya Mariya da wannan mutumin na cikin videon ne suka zo har unguwar mu. Kuma na gansu, sannan su ne suka bigeni da mota. Har na samu waɗannan raunikan na jikina... Shi ya sa na ce ba zan yi ƙasa a gwuiwa wurin sanar da ku wannan gaskiyar ba!”
Faruk ya dafe kansa. Tunanin abin da ya faru tsakaninsu jiya ya dawo masa. Ke nan jiya da daddare kashe Muktar ta tafi?. Innalillahi wa inna ialaihi raji'un. Ya furta yana murza goshinsa. Mu'az kuwa bai sake cewa uffan ba. Sai yatsun hannunsa da yake murzawa idonsa na sauya kala zuwa ja.
-------------------------------
_Wato a wasu lokutan. Abubuwan da ba mu yi zato ba su ne suka cika faruwa da mu._
_Irin haka ce ta faru ga Faruk da Mu'az._
_Shin! Wani dabi ne zai ɓarke a haɗejia, tsakanin Gambo da Maimuna da kuma Auwwa?._
_Shin, wani hali kuke tunanin Halima za ta shiga idan aka sallameta a aiki?._
_Me zai faru tsakanin Mariya da Faruk?._
_Sannan Mu'az, dan shi kam ya fi Faruk fusata._
_Yaya Mariya za ta yi domin wanke kanta a idon yayanta da kuma mijinta, da ma sauran jama'ar duniya da za su sani?._
_Shin, kuna ganin cewa, kisan Munira zai zama kisa na ƙarshe da Mariya za ta aikata?. Ko za ta ci gaba da zama a ƙungiyarsu ta bayin Shaiɗan!?._
_Hummm!_
_Akwai magana. To, ga duk wanda yake son sanin amsoshin waɗannan tambayoyin, sai ya biya ₦300. Tun kafin tafiyar nan ta wuce ku._
_Kun san daga ganin tafiyar nan ba ta wasa ba ce, dan har yanzu ba mu yi komai ba. Kuma ina me muku tabbacin ba za ku yi da na sanin siyan wanna littafi ba. Kun san alƙalamin Candy akwai suger._
••• ••• •••
*Zan yi amfai da wannan damar, wurin gode muku, SALMANIANS. Kun san da cewa ku ne on top a ƙalbina. I love you like wujiga-wujiga. Ina sonku fiye da irin son da kuke min*
Ga duk wanda ya shirya dan ayi tafiyar nan da shi, zai ₦300 kacal. Ta wannan account details ɗin da zan rubuta. Idan kuma har ya zama complete document sai dai ku biya ₦500.
5487270431
Salma Isah
Moniepoint
Shaidar biya kuma via.
08130172702.
Sai na ji ku SALMANIANS.
Best regards.
*SALMA AHMAD ISAH*
*(CANDY🦋)*
2024...