← Book details Kaddara Ce Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 22

Sashe 19

Kaddara Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hannunta na rawa ta nuna Mariya da shi. Sannan ta kalli gawar Vishal dake ƙasa. Ita ma Mariyan ta ganeta. Kuma ganetan da ta yi ya sa ta nufo bakin ƙofar ɗakin da gudu. Ita ma Munira sai ta ranta a na kare.

Ta fita daga hotel ɗin a kiɗime, ko motarta da ta zo da ita bata ɗauka ba. Ganin ta fita ya sa Lawan da Mariya bin bayanta a mota. Amma saboda ta iya gudu sosai ya sa ta musu nisa. Dan har wayarta ta ɗaga ta kira Faruk da ita. Sai dai kafin ta kai ga faɗa masa abin da ke bakinta tunaninta da komai nata ya tsaya cak. Har Mariya da Lawal suka ɗauketa bata cikin hayyacinta...

~~~

Munira ce yashe a tsakiyar wani ɗaki. Hannunta da ƙafarta duka a ɗaure. Sannan idonta a rufe. Idan ka kalleta ba ka ce tana numfashi ba...

Daga wajen ɗakin aka turo ƙofar ɗakin ciki, ƙaran buɗewar ƙofar ya sa ta motsa. A hankali kuma sai ta shiga buɗe idonta. Tun tana gani dishi-dishi har ganinta ya dawo dai-dai. Shiru ta yi tana kallon Mariya da ta shigo ɗakin.

Da ƙyar ta iya yinƙurawa ta miƙe zaune, duk da ƙafafuwanta da hannayenta a ɗaure suke. A dai-dai lokacin kuma Mariya ta durƙusa a gabanta tana murmushi. Yayin da ita kuma Munira take zubar da hawayen tausayin abokanta. Saboda ita bata ta kanta. Dan ta san ba lalle ta tsira a hannunsu ba.

“Mariya me ya sa?. Me ya sa kike cutar da Faruk da kuma MJ? Me ya sa?”

Ta tambaya hawaye na ƙara zubo mata. Amma ita Mariyan ba ta yi magana ba. Sai murmushi da take. Duk da haka Munira ba ta haƙura ba ta sake faɗin.

“Me zai sa ki kashe rai Mariya?. Mariya me zai sa ki zaɓi rayuwar da ba taki ba?...”

“Wa ye yace miki wannan rayuwar ba tawa ba ce?. Wannan rayuwata ce, rayuwa me daɗi a ƙarƙashin gata da tallafin shaiɗan!”

Mariya ta katseta tana faɗaɗa murmushinta. Munira ta yi shiru tana son gano inda zancen nata ya dosa.

“Mariya ke 'yar cult ce?”

Mariya ta lumshe idonta ta buɗe tana gyaɗa kai, hankalinta kwance.

“Ƙwarai kuwa Captain Munira Musa. Na bayar da ruhina ga shugaban mu shaiɗan. A yanzu ba ni da abin bauta sama da shaiɗan!...”

“Subhannallah! Subhannallah!. A'uzubillah! A'uzubillahi mina shaiɗanir-rajim!”

Wani duka da Mariya ta kaiwa bakinta ya sa ta faɗi gefe guda. Bakinta na zubar da jini. Mariya da fuskarta ta rikiɗa zuwa fushi ta sa hannu ta ta riƙo gaban rigar dake jikinta. Sannan ta janyota tana zare idonta a kanta.

“Idan kika kuskura kika sake buɗe bakinki kika faɗi wata ƙazamar kalma ɗaya a kan abin bautata shaiɗan sai na cinye namanki ɗanye!”

Bakin Munira na fitar da jini, idonta na zubar da ƙwalla ta girgiza kai.

“Ba ke ba ce Mariya!. Wallahi ba ke ba ce. Kowa ya na yabon kyan hali irin naki, kina da nutsuwa da kamala. Kina da sanin ya kamata da haƙuri, me ya sa yanzu kika sauya? Me ya sa? Innalillahi wa inna ialaihi raji'un!...”

Mariya ta saki gaban rigar tata. Sannan ta miƙe ta fice daga ɗakin a fusace. A wani ɗaki ta je ta samu Wahash.

“Shugaba! Wani kalar hukunci ya kamata mu mata?”

Mariya ta tambaya tana huci. Saboda an taɓa abin bautarta. Wahash ya dubeta.

(Wahalallu😒)

“Yanzu kun kashe Kunda (Vishal). Kuma za'a yi bincike a kai. Idan har aka kasheta ita ma zargi ne zai ƙara yawa. Dan haka dole mu jinkirta wurin kasheta!”

Mariya ta jinjina kai.

“Dole mutuwarta ta zama me tada hankali. Saboda ta taɓa abin bautarmu Wahash”

Wahash ya yi murmushi.

“Zamu ba ta irin mutuwar da hatta ahalinta ba lalle su ganeta ba”

Mariya ta jinjina kai. Kamar yanda suka tsara ba su kasheta a lokacin ba. Sun ajeta a masarautar shaiɗan na wasu satuka. Kuma a duk kwanan duniya da kalar azabar da ake ganawa Munira. Da haka har lokacin da za su sadaukar da jininta ga shiaɗan ya zo.

Sai da suka mata kisa irin na wulaƙanci. Kisan da duk wani me imani idan ya gani sai ya zubar da hawaye. Sun bata mutuwa irin wanda ko da fasiƙin mutum ne ba'a so ya yi. Haka suka cillar da abin da ya yi saura na gawarta a wata unguwa. Hankalinsu kwance...

*Present Day...*

MUKTAR POV.

Kamar kullum. Yau ma haka Ali ya sauƙe shi a unguwarsu. Sannan ya juya ya tafi da motar tasa. Saboda shi sam ba ya zama da motar a wurinsa. A ko da yaushe tana wurin Ali. Sai idan yana buƙatar zuwa wani wurin shi kaɗai zai sa Alin ya kawo masa ita.

Kamar jiya. Haka yau ma aka dalle shi da hasken fitilar mota, saɓanin jiya da ya kasance mashin. Cak ya tsaya da tafiyar da yake. Sannan a hankali ya juya bayansa ya kalli motar dake bayansa.

Duk da yanda aka haske shi da fitilar motar ya iya gane motar, har ma da mutum biyun dake cikin motar. Wannan motar ce da aka sace Munira a cikinta, sannan Mariya da crime partner ɗinta da ba su san sunansa ba ne zaune a ciki.

Kamar yanda yake tsaye haka ma motar tasu take tsaye a wuri ɗaya, duk da a kunne take. A hankali ya ja ƙafarsa ɗaya baya. Hakan ya bawa Lawan damar jan motar ma zuwa gaba kaɗan. Ganin haka ya sa Muktar ya sake jan ƙafarsa baya, Lawal ma ya ƙara jan motar gaba.

Muktar ya juya bayansa. Sannan ya ci gaba da tafiya a nutse, saboda ya ga abubuwan da suka ɗara wannan tayar da hankali. Ƙarewa har kan gadon baccinsa an zo an saka masa wuƙa a wuya an yi barazanar kasheshi. To ai su su Mariya ƙananun 'yan iska ne.

Kamar yadda yake tafiya a hankali, haka ma motar ta ci gaba da binsa a hankali. Can kuma sai ya fara tafiya da sauri, hakan ya sa Lawan ma ƙara gudun motar. Ganin haka ya sa Muktar ya fara gudu. Lawan ma ya taka motar da gudun bala'i.

Kuma ba'a je ko ina ba ya buge Muktar da motar. Ya faɗi ƙasa, hatta daƙaran da ya yi sun ji shi da Mariya. Kuma ya na buge shi sai ya tsayar da motar. Mariya ta dube shi.

“Ka taka shi ka bi ta kansa mana”

Ya kuwa taka motar, har sai da suka ji motar ta taka shi. Sannan suka ja motar da gudu suka bar unguwar, sun ɗauka cewa shikenan kuma, matsala ta mutu tare da mutuwar Muktar.

Sai da motasu ta bar unguwar, Sannan Muktar da ya kaucewa motar tasu ya tashi zaune da ƙyar. Dan a sanda suka bige shi bai kwanta a wurin ba. Ƙarfin hali ya yi ya murgina gefe. Su kuma suka taka dutse, har suna tunanin cewa shi suka taka.

Hannunsa da yake da tabbacin ya karye ya riƙe yana jin raɗaɗin azaba. Sannan ya yi ƙarfin halin ɗaukar wayarsa, ya kira Ali ya sanar masa da halin da yake ciki, sannan ya kira ƙaninsa Walid.

“Walid kana gida?”

Ya faɗi da ƙyar yana rsinte idonsa. Saboda yanda yake jin ko ina na jikinsa na ciwo, gaba ɗaya ma ya rasa takamemen ina ne yake masa ciwo. Daga ɗayan ɓangaren Walid yace.

“Eh Ya Mukhy. Ina nan, lafiya?”

“Ka fito ka zo kwanar gidan Alhaji Sadam. Ina wurin, na ɗan samu wani haɗari ne?”

Walid dake zaune a falo ya miƙe zumbur yana tambayarsa.

“Haɗari? Yaushe? A ina?”

“Stop asking just come and help me!”

“Okay”

Ya kashe wayar, sannan ya nufi ƙofar falo da gudu.

“Kai Walid! Ina za ka je?”

Mamansu da ta fito daga kitchen ta tambaya. Sai ya dakata, sannan ya juyo.

“Ya Mukhy ne ya kirani yace ya samu haɗari a kan kwanar gidan Alhaji Sadam. Shi ne zan je na duba”

“Haɗari?”

Mama ta tambaya a hargitse.

“Eh Mama. Bari in je na duba shi”

“To ka kula. Allah ya sa ba wani mummunan abin ne ya same shi ba.”

“Amin”

Ya amsa yana fita daga falon. Da yake shi ya fi kusa da Muktar ɗin sai ya riga Ali isa. Dan gidan Alhaji Sadam ɗin ɗan gaba kaɗan ne da nasu. Sai da Ali ya zo, tukkuna suka ɗauke shi zuwa asibiti.

-------------------

_Na lura da bana letter (M) ce ke zamani_

_Rabin 'yan wasanmu duka sunansu da ‘M’ ya fara_

_To gaba ɗaya babin yau ma a kan M ɗin ya ƙare. Ga Mariya fa Muktar._

_Sannan kun ji abin da ya faru tsakanin Munira da Mubarak_

_Kun kuma ji yanda aka yi Munira ta mutu_

_Mu je zuwa. Saboda yanzu muka fara sharar hanya😉_

_Share fi sabillilah❤️_

*Daga alƙalamin Salma Ahmad Isah✍️.*
*CANDY CE🦋.*

--------------------
_Kada a manta da biyan kuɗin littafi. Dan free page zai ƙare daga gobe in Allah ya kaimu. To subscribe pay ₦300 to._

5487270431
Salma Isah
Monie point.

And send the evidence of payment via.

08130172702

#Candy
#SalmaAhmadIsah
°°°°°°°°°°°°°°°°°°

*ƘADDARA CE!*

*©SALMA AHMAD ISAH.*
*CANDY🦋*

_ArewaBooks @SalmaAhmad_
_Wattpad @Salma_Ahmad_Isah_

*10*

MU'AZ POV.

Zaune suke a falo shi da, Mummy, Mima da Na'im. Abinci yake ci yana latsa wayarsa. A jima kaɗan sai ya yi murmushi. Kuma ba komai ke janyo hakan ba face cry cry baby Leemat da yake tunowa.

A duk sanda zai tuno haɗuwarsa da ita a yau sai ya yi murmushi me faɗi. Bai san me ya sa ba, amma haka kawai yanayin shagwaɓarta ke burge shi, da yanda take magana, da yanda kuka ba ya mata wuya. Kuma hakan ke nuna masa cewar shagwaɓa ɗabi'arta ce.

Mima da tun ɗazu take satar kallonsa ta gyara zama tana leƙa cikin wayarsa. Wai ko za ta ga abin da yake saka shi murmushi. Amma ba ta ga ba, dan chat kawai yake. Sai ta ƙara matsawa kusa da shi tana faɗin.

“Ya Mu'az!”

Kallonta ya yi ba tare da ya amsa ba.

“Ko dai da Yasmin kake chat?”

Nan da nan ya murtuke fuska ya soma harararta.
Chapter 19 · 0% Book details