Sashe 10
Kaddara Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Da yawa fa zan ɗiba”
“Ɗibi wanda zai isheki”
Ta miƙe ta fita da murnarta. Ta ɗauki kwano ta zubo tuwon shinkafa da miyar taushen da Hajja ta girka. Ta buɗe ɗan ƙaramin fridge ɗin Hajjan, ta ɗauki pure water. Ta dawo ɗakin ta zauna. Ta shiga ci tana bawa Hajja labarin abin da ya faru da ita yau, ciki har da haɗuwarta da Abba.
“To yanzu Maimuna. Da kika masa haka, idan kuma da gaske yake yana sonki fa?”
Maimuna ta dakata daga kai loma bakinta. Ta mayar da abincin da ta ɗebo cikin kwano. Sannan ta kalli Hajja.
“Hajja ban bari ya kai ga furta min hakan ba. Saboda na san ba zai min soyyaya tsakaninsa da Allah ba. A irin halin da nake ciki bana jin akwai namijin da zai soni”
Hajja ta girgiza kai.
“Ba komai Maimuna ƙaddara ce!. Ki ci gaba da haƙuri, Allah ya san da ke. Kuma zai kawo miki sauyin rayuwa”
Maimuna bata sake cewa komai ba. Har ta kamalla cin tuwonta. Ta fito da kwanon waje. Ta wanke hannunta ta dawo ta zauna kusa da Hajja.
“Ina Kawu ne? Tun da na shigo ban ji motsinsa ba”
“Ya tafi jajantawa Alhaji Babangida. Saboda asarar da ya yi a satin nan.”
Maimuna ta gyaɗa kai.
“Ah, Maimuna. Duba cikin jakar can tawa, za ki ga leda ki ɗauko”
Cewar Hajja. Maimuna ta miƙe ta nufi jakar. Sannan ta buɗe ta ɗauko ledar dake ciki. Ta dawo kusa da Hajja ta zauna.
“Hajja ga ledar”
Hajja ta karɓa ta buɗe, sannan ta fito da hijabai biyu dake ciki, da abonaki, da kuma audugar mata.
“Gasu nan. Duka naki ne na sai miki a bakin asibiti. Na san yanzu sanyi ya shigo, kina buƙatar abonaki... Kuma idan za ki tafi zan baki kwaki da ƙanzo. Ki ɓoye a ɗakinki idan kin koma. Duk ranar da Auwwa za ta hanaki abinci sai ki ɗauka ki ci”
Maimuna ta yi murmushi ta kwanta a jikin kakarta.
“Ina sonki Hajja”
Hajja na murmushi ta shafa kan gudaliyar jikarta.
“Allah ya ji ƙan Muhammadu da Asabe (iyayen Maimuna).”
“Amin Hajja”
Ta amsa tana jin kewarsu, duk kuwa da kaf cikinsu babu wanda ta sani. Sai dai a hoto ko ta ji labarinsu.
FARUK POV.
Tsaye ya yi a ƙofar ɗakin Mariya yana kallonta. Yayin da take yafa mayafi a kanta. Alamun ta shirya tsaf domin ziyartar gidansu. Idonsa ya zarce kan Hilal dake zaune a kan gado. A hankali ya saki handle ɗin ƙofar ya shiga ciki. Kallo ɗaya Mariya ta masa ta ɗauke kai. Shi kuma bai ma kalleta ba, Hilal kawai ya ɗauka, sai a sannan ya kalleta.
“Kin gama shiryawa ne?”
“Umm”
Amsarta ta fito a taƙaice kamar kullum. Kansa kawai ya gyaɗa, sannan ya nufi ƙofa yana faɗin.
“Ina jiranki a mota”
Sannan ya fita daga ɗakin. Kai tsaye ya sauƙa ƙasa, ya shige motarsa dake parking lot. Ya zauna a ciki, tare da zaunar da Hilal a kan cinyarsa. Yana jiran fitowar Mariya.
Ido kawai ya tsira mata a sanda ta fito daga ƙofar falo. Saboda kalar kwalliyar da ta yi. Wata kyakkyawar atamfa ce da ya sai mata a Khadeeja Candy store a jikinta. Atamfar me ratsin orange ta bala'in dacewa da fatar jikinta da take wani abu tsakani fari da baƙi.
Ta yafa wani orange gyale, fuskarta babu wata kwalliya ta a zo a gani. Amma she looks perfect. Murmushi ya yi yana binta da kallo har ta shiga cikin motar. Har ga Allah shi kam yana son matarsa. Kuma duk abin da take masa yana dannewa saboda darajar yayanta da ta mahaifinta, da kuma son da yake mata. Da ma an ce so hana ganin laifi.
“Mu je?”
Ta faɗi ganin bai ja motar ba har bayan da ta shiga. Idonsa ya ɗauke daga kanta, sannan ya tayar da motar ya fita daga gidan, gidan Hajiyarsu suka fara zuwa, kafin su nufi gidan su Mariyar.
A falo suka iske Hajiyarsa zaune tana cin abincin dare. A falon suka zauna, suka gaisheta cike da girmamawa. Har ta karɓi Hilal tana masa wasa. Kafin suka mata sallama suka fita a kan za su je gidan su Mariya ne.
Sai da suka fita daga falo ta janye idonta a kansu. Ta girgiza kai, halin damuwar auren ɗan nata na bata mamaki. Ba sai an faɗa ba, ta san cewa Faruk ba ya jin daɗin zama da Mariya.
Duk kuwa da bai taɓa faɗa mata ba, saboda ta san halin zurfin ciki irin nasa. Amma ko makaho ya shafa zai gane hakan. Sai dai kuma ita a matsayinta na uwa bai kamata ta saka musu baki a cikin al'amarin aurensu ba tare da sun sakota a ciki ba.
“Wa alaikassalam!”
Ta amsa sallamar ɗanta Adamu, yayan Faruk, kuma ƙanin Bara'atu 'yarta ta fari dake aure a mahaifarsu wato Haɗejia. Asalin mahaifinsu Alhaji Haruna haifaffen garin Hadejia ne. Wanda ya gaji sarautar Kaigaman Haɗejia tun daga kakkaninsa.
Kuma yana da mata biyu. Hajiya Ruƙayya ita ce matarsa ta fako, wadda ta haifa masa yara uku maza, wanda a yanzu babbansu Muhammad Bello shi ne yake riƙe da sarautar ta Kaigama. Hajiya Aisha, wato mahaifiyar su Faruk ita ce matarsa ta biyu. Wadda ta haifa masa yara uku, Bara'atu ita ce ta farko, sai kuma Adamu, sannan Faruk.
Kasancewar harkokin kasuwancinsa yana yinsu ne a garin Abuja ya sa ita Hajiya Aisha ya dawo da ita nan garin Abuja. Yayin da matarsa ta farko da yaranta ke gidansa na garin Haɗejia. Karatu ne ya sa Bara'atu ta koma Haɗejia. Kuma da Allah ya sa rabonta a can yake sai Allah ya haɗata da mijinta a can ɗin.
Wanda suka yi aure har suka hayyayafa, kafin Allah ya masa rasuwa, amma duk da haka bata bar garin Haɗejia ba, saboda aikinta da kuma yaranta da 'yan uwanta da suke can. Adamu kuma yana da mata ɗaya. Wadda yake zaune da ita a nan garin Abuja da yaransa biyu.
MARIYA POV.
Durƙushe suke ita da Faruk a gaban Daddy. Wanda ke musu nasihar hannunka me sanda. A nasihar tasa bai fito yace akwai ɗaya daga cikinsu da ya zo ya kawo ƙarar ɗan uwansa ba. Kuma bai nuna cewa ya san akwai matsala a tsakaninsu ba.
Ya yi amfani da hikima irin tasu ta manya. Wurin ganin ya nusar da su kurakuransu cikin ruwan sanyi. Tun da babu wanda ya san abin da ke tsakaninsu. Ko da Daddy ya kai ƙarshe sai Faruk yace inshallah za'a kiyaye. Mariya kuwa bata ce komai ba. Kuma da ma ba za ta ce ɗin ba.
Da Daddy ya sallame su ma ta riga shi fita daga falon na Daddy. Ta wuce sashin Mummy, yayin da shi kuma ya tsaya a wurin Mu'az dake compound. Sun daɗe a gidan. Kafin suka yiwa kowa sallama suka tafi.
Faruk ya ɗauka cewa Mariya ta ji nasihar Daddy, ta kuma ɗauketa kamar yanda Daddyn ke fata, amma sai ya ga saɓanin haka. Dan suna komawa gida ta wuce ɗakinta ɗauke da Hilal a hanunta, wanda ya yi bacci. A mamakance ya bita da kallo har ta shige ɗakin. Ji ya yi yau ba zai iya turewa ba kamar yanda ya saba, dan haka ya bita ɗakin dan ya mata magana. A bakin gado ya sameta tana kwantar da Hilal.
“Mariya”
Ya kira sunanta. Ta juyo ta kalleshi.
“Na ɗauka cewar ko da laifi na miki, za ki yafe min saboda nasihar da Daddy ya mana ɗazu. Na ɗauka cewar ko da kina jin haushina ne za ki sauƙo saboda maganar Daddy... Amma kuma kin tabbatar min da ba haka ba ne, tun da har kika dawo ɗakinki a maimakon nawa.”
Mariya ta yi shiru tana kallonsa. Wai da shi haka yake zaton tana da sauƙin kai?. Ai ko ya yaudari kansa da zuciyarsa. A ta waje ne jama'a ke mata kallon me sauƙin kai, amma a ta ciki sam Mariya bata da taushin zuciya.
“Faruk! A gaskiya ba na jin zan sake haɗa ɗaki da kai. Ballantana har na haɗa shimfiɗa da kai... Wannan a baya ne, ban da yanzu!”
Ta yi maganar tana juya masa baya, tare da nufar barthroom. Amma sai ya riƙo hannunta ya dawo da ita baya. Ta kalli hannunta da ya riƙe, sannan ya kalli fuskarsa.
“Faruk! Are you trying to hurt me?”
Ta tambaya a mamakance. Faruk ya kalli hannunta da ya matse. Da sauri ya saki hannun nata, sannan yace.
“Mariya, look, I don't want to hurt you or cause you any harm. I just want to know if you've stopped loving me. Just be honest with me!... A farkon aurenmu ba haka muke zaune ba. There is love and care. Me ya sa komai ya sauya yanzu? Could you explain to me why?”
Ko gezau ba ta yi ba ballantana ta ba shi amsa. Jin haka ya sa Faruk ya ɗora yatsun hannunsa biyu a kan karan hancinsa ya rintse ido. Sannan ya buɗe idonsa.
“Mariya!. Idan sona kika daina ya kamata ki faɗa min. Ni kuma a shirye nake domin sawwaƙe miki, da ace mun ci gaba da yin irin wannan zaman da za mu riƙa cutar da junanmu!...”
Jin yana batun rabuwa ya sa Mariya ta saka ƙwayar idonta cikin nasa. Sannan a hankali bakinta ya motsa cikin faɗin wata kalma. A take ƙwayar idonta ta sauya kala zuwa ja.
Wani irin jiri Faruk ya ji ya kwashe shi. Hakan ya sa ya yi saurin dafe kansa yana yin baya. Idonsa ya rintse gam, sannan ya buɗe yana jin wani irin juyawa da kansa yake. Juyowa ya yi ya kalli Mariya dake tsaye. A take ya ji tunaninsa ya birki ce. Sai ya kasa tuna sanda ya shigo ɗakinta. Ya kasa tuna maganar da yake, kamar kuma wani abu yake nema a wurin wani.
“Mary!”
Ya kira yana kallonta.
“Papi lafiyarka ƙalau?”
Sai ya sauƙe hannunsa daga kansa yana kallon ɗakin kamar baƙonsa. Gaba ɗaya ya kasa tuna abin da ya faru a ɗakin.
“Me nake yi a nan?”
Wani irin makirin murmushi ta yi na gefen baki. Sana ta nufe shi, ta tsaya a gabansa ta yanda har suna musayar numfashi.
“Baka da lafiya Papi. Mu je na kaika ɗakinka”
“Ɗibi wanda zai isheki”
Ta miƙe ta fita da murnarta. Ta ɗauki kwano ta zubo tuwon shinkafa da miyar taushen da Hajja ta girka. Ta buɗe ɗan ƙaramin fridge ɗin Hajjan, ta ɗauki pure water. Ta dawo ɗakin ta zauna. Ta shiga ci tana bawa Hajja labarin abin da ya faru da ita yau, ciki har da haɗuwarta da Abba.
“To yanzu Maimuna. Da kika masa haka, idan kuma da gaske yake yana sonki fa?”
Maimuna ta dakata daga kai loma bakinta. Ta mayar da abincin da ta ɗebo cikin kwano. Sannan ta kalli Hajja.
“Hajja ban bari ya kai ga furta min hakan ba. Saboda na san ba zai min soyyaya tsakaninsa da Allah ba. A irin halin da nake ciki bana jin akwai namijin da zai soni”
Hajja ta girgiza kai.
“Ba komai Maimuna ƙaddara ce!. Ki ci gaba da haƙuri, Allah ya san da ke. Kuma zai kawo miki sauyin rayuwa”
Maimuna bata sake cewa komai ba. Har ta kamalla cin tuwonta. Ta fito da kwanon waje. Ta wanke hannunta ta dawo ta zauna kusa da Hajja.
“Ina Kawu ne? Tun da na shigo ban ji motsinsa ba”
“Ya tafi jajantawa Alhaji Babangida. Saboda asarar da ya yi a satin nan.”
Maimuna ta gyaɗa kai.
“Ah, Maimuna. Duba cikin jakar can tawa, za ki ga leda ki ɗauko”
Cewar Hajja. Maimuna ta miƙe ta nufi jakar. Sannan ta buɗe ta ɗauko ledar dake ciki. Ta dawo kusa da Hajja ta zauna.
“Hajja ga ledar”
Hajja ta karɓa ta buɗe, sannan ta fito da hijabai biyu dake ciki, da abonaki, da kuma audugar mata.
“Gasu nan. Duka naki ne na sai miki a bakin asibiti. Na san yanzu sanyi ya shigo, kina buƙatar abonaki... Kuma idan za ki tafi zan baki kwaki da ƙanzo. Ki ɓoye a ɗakinki idan kin koma. Duk ranar da Auwwa za ta hanaki abinci sai ki ɗauka ki ci”
Maimuna ta yi murmushi ta kwanta a jikin kakarta.
“Ina sonki Hajja”
Hajja na murmushi ta shafa kan gudaliyar jikarta.
“Allah ya ji ƙan Muhammadu da Asabe (iyayen Maimuna).”
“Amin Hajja”
Ta amsa tana jin kewarsu, duk kuwa da kaf cikinsu babu wanda ta sani. Sai dai a hoto ko ta ji labarinsu.
FARUK POV.
Tsaye ya yi a ƙofar ɗakin Mariya yana kallonta. Yayin da take yafa mayafi a kanta. Alamun ta shirya tsaf domin ziyartar gidansu. Idonsa ya zarce kan Hilal dake zaune a kan gado. A hankali ya saki handle ɗin ƙofar ya shiga ciki. Kallo ɗaya Mariya ta masa ta ɗauke kai. Shi kuma bai ma kalleta ba, Hilal kawai ya ɗauka, sai a sannan ya kalleta.
“Kin gama shiryawa ne?”
“Umm”
Amsarta ta fito a taƙaice kamar kullum. Kansa kawai ya gyaɗa, sannan ya nufi ƙofa yana faɗin.
“Ina jiranki a mota”
Sannan ya fita daga ɗakin. Kai tsaye ya sauƙa ƙasa, ya shige motarsa dake parking lot. Ya zauna a ciki, tare da zaunar da Hilal a kan cinyarsa. Yana jiran fitowar Mariya.
Ido kawai ya tsira mata a sanda ta fito daga ƙofar falo. Saboda kalar kwalliyar da ta yi. Wata kyakkyawar atamfa ce da ya sai mata a Khadeeja Candy store a jikinta. Atamfar me ratsin orange ta bala'in dacewa da fatar jikinta da take wani abu tsakani fari da baƙi.
Ta yafa wani orange gyale, fuskarta babu wata kwalliya ta a zo a gani. Amma she looks perfect. Murmushi ya yi yana binta da kallo har ta shiga cikin motar. Har ga Allah shi kam yana son matarsa. Kuma duk abin da take masa yana dannewa saboda darajar yayanta da ta mahaifinta, da kuma son da yake mata. Da ma an ce so hana ganin laifi.
“Mu je?”
Ta faɗi ganin bai ja motar ba har bayan da ta shiga. Idonsa ya ɗauke daga kanta, sannan ya tayar da motar ya fita daga gidan, gidan Hajiyarsu suka fara zuwa, kafin su nufi gidan su Mariyar.
A falo suka iske Hajiyarsa zaune tana cin abincin dare. A falon suka zauna, suka gaisheta cike da girmamawa. Har ta karɓi Hilal tana masa wasa. Kafin suka mata sallama suka fita a kan za su je gidan su Mariya ne.
Sai da suka fita daga falo ta janye idonta a kansu. Ta girgiza kai, halin damuwar auren ɗan nata na bata mamaki. Ba sai an faɗa ba, ta san cewa Faruk ba ya jin daɗin zama da Mariya.
Duk kuwa da bai taɓa faɗa mata ba, saboda ta san halin zurfin ciki irin nasa. Amma ko makaho ya shafa zai gane hakan. Sai dai kuma ita a matsayinta na uwa bai kamata ta saka musu baki a cikin al'amarin aurensu ba tare da sun sakota a ciki ba.
“Wa alaikassalam!”
Ta amsa sallamar ɗanta Adamu, yayan Faruk, kuma ƙanin Bara'atu 'yarta ta fari dake aure a mahaifarsu wato Haɗejia. Asalin mahaifinsu Alhaji Haruna haifaffen garin Hadejia ne. Wanda ya gaji sarautar Kaigaman Haɗejia tun daga kakkaninsa.
Kuma yana da mata biyu. Hajiya Ruƙayya ita ce matarsa ta fako, wadda ta haifa masa yara uku maza, wanda a yanzu babbansu Muhammad Bello shi ne yake riƙe da sarautar ta Kaigama. Hajiya Aisha, wato mahaifiyar su Faruk ita ce matarsa ta biyu. Wadda ta haifa masa yara uku, Bara'atu ita ce ta farko, sai kuma Adamu, sannan Faruk.
Kasancewar harkokin kasuwancinsa yana yinsu ne a garin Abuja ya sa ita Hajiya Aisha ya dawo da ita nan garin Abuja. Yayin da matarsa ta farko da yaranta ke gidansa na garin Haɗejia. Karatu ne ya sa Bara'atu ta koma Haɗejia. Kuma da Allah ya sa rabonta a can yake sai Allah ya haɗata da mijinta a can ɗin.
Wanda suka yi aure har suka hayyayafa, kafin Allah ya masa rasuwa, amma duk da haka bata bar garin Haɗejia ba, saboda aikinta da kuma yaranta da 'yan uwanta da suke can. Adamu kuma yana da mata ɗaya. Wadda yake zaune da ita a nan garin Abuja da yaransa biyu.
MARIYA POV.
Durƙushe suke ita da Faruk a gaban Daddy. Wanda ke musu nasihar hannunka me sanda. A nasihar tasa bai fito yace akwai ɗaya daga cikinsu da ya zo ya kawo ƙarar ɗan uwansa ba. Kuma bai nuna cewa ya san akwai matsala a tsakaninsu ba.
Ya yi amfani da hikima irin tasu ta manya. Wurin ganin ya nusar da su kurakuransu cikin ruwan sanyi. Tun da babu wanda ya san abin da ke tsakaninsu. Ko da Daddy ya kai ƙarshe sai Faruk yace inshallah za'a kiyaye. Mariya kuwa bata ce komai ba. Kuma da ma ba za ta ce ɗin ba.
Da Daddy ya sallame su ma ta riga shi fita daga falon na Daddy. Ta wuce sashin Mummy, yayin da shi kuma ya tsaya a wurin Mu'az dake compound. Sun daɗe a gidan. Kafin suka yiwa kowa sallama suka tafi.
Faruk ya ɗauka cewa Mariya ta ji nasihar Daddy, ta kuma ɗauketa kamar yanda Daddyn ke fata, amma sai ya ga saɓanin haka. Dan suna komawa gida ta wuce ɗakinta ɗauke da Hilal a hanunta, wanda ya yi bacci. A mamakance ya bita da kallo har ta shige ɗakin. Ji ya yi yau ba zai iya turewa ba kamar yanda ya saba, dan haka ya bita ɗakin dan ya mata magana. A bakin gado ya sameta tana kwantar da Hilal.
“Mariya”
Ya kira sunanta. Ta juyo ta kalleshi.
“Na ɗauka cewar ko da laifi na miki, za ki yafe min saboda nasihar da Daddy ya mana ɗazu. Na ɗauka cewar ko da kina jin haushina ne za ki sauƙo saboda maganar Daddy... Amma kuma kin tabbatar min da ba haka ba ne, tun da har kika dawo ɗakinki a maimakon nawa.”
Mariya ta yi shiru tana kallonsa. Wai da shi haka yake zaton tana da sauƙin kai?. Ai ko ya yaudari kansa da zuciyarsa. A ta waje ne jama'a ke mata kallon me sauƙin kai, amma a ta ciki sam Mariya bata da taushin zuciya.
“Faruk! A gaskiya ba na jin zan sake haɗa ɗaki da kai. Ballantana har na haɗa shimfiɗa da kai... Wannan a baya ne, ban da yanzu!”
Ta yi maganar tana juya masa baya, tare da nufar barthroom. Amma sai ya riƙo hannunta ya dawo da ita baya. Ta kalli hannunta da ya riƙe, sannan ya kalli fuskarsa.
“Faruk! Are you trying to hurt me?”
Ta tambaya a mamakance. Faruk ya kalli hannunta da ya matse. Da sauri ya saki hannun nata, sannan yace.
“Mariya, look, I don't want to hurt you or cause you any harm. I just want to know if you've stopped loving me. Just be honest with me!... A farkon aurenmu ba haka muke zaune ba. There is love and care. Me ya sa komai ya sauya yanzu? Could you explain to me why?”
Ko gezau ba ta yi ba ballantana ta ba shi amsa. Jin haka ya sa Faruk ya ɗora yatsun hannunsa biyu a kan karan hancinsa ya rintse ido. Sannan ya buɗe idonsa.
“Mariya!. Idan sona kika daina ya kamata ki faɗa min. Ni kuma a shirye nake domin sawwaƙe miki, da ace mun ci gaba da yin irin wannan zaman da za mu riƙa cutar da junanmu!...”
Jin yana batun rabuwa ya sa Mariya ta saka ƙwayar idonta cikin nasa. Sannan a hankali bakinta ya motsa cikin faɗin wata kalma. A take ƙwayar idonta ta sauya kala zuwa ja.
Wani irin jiri Faruk ya ji ya kwashe shi. Hakan ya sa ya yi saurin dafe kansa yana yin baya. Idonsa ya rintse gam, sannan ya buɗe yana jin wani irin juyawa da kansa yake. Juyowa ya yi ya kalli Mariya dake tsaye. A take ya ji tunaninsa ya birki ce. Sai ya kasa tuna sanda ya shigo ɗakinta. Ya kasa tuna maganar da yake, kamar kuma wani abu yake nema a wurin wani.
“Mary!”
Ya kira yana kallonta.
“Papi lafiyarka ƙalau?”
Sai ya sauƙe hannunsa daga kansa yana kallon ɗakin kamar baƙonsa. Gaba ɗaya ya kasa tuna abin da ya faru a ɗakin.
“Me nake yi a nan?”
Wani irin makirin murmushi ta yi na gefen baki. Sana ta nufe shi, ta tsaya a gabansa ta yanda har suna musayar numfashi.
“Baka da lafiya Papi. Mu je na kaika ɗakinka”