Sashe 14
Kaddara Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ashe ita ma za ta wayi gari ta girka tuwon dawa, har ma ta ci shi dan maganin yunwa. Kamar yanda ta saba cin ko wani abincin gidan dan kashe yunwa yau ma haka ta ci. Saboda da ace ita take ɗaukan albashinta ba ta ga dalilin da zai sa ta ci wannan abincin ba.
Amma ita ko da wuƙa za'a ɗora a wuyanta ace nawa ne albashinta ba ta sani ba. Ko kalarsu ba ta gani, daga an yi albashi Kawu Sani yake zuwa ya karɓa da kansa. Tsakaninta da shi kawai shi ne kuɗin abin hawa.
Gaba ɗaya yau zuciyarta ta fi ko yaushe jagulewa. Na farko abin da Wannan koɗɗaɗen mugun sojan ya mata. Na biyu ga kumatunta da take jinsa kamar ba a jikinta yake ba. Sai kuma wannan tuwon da take cinsa a dole. Dan cusawa kawai take. Amma sam bakinta babu wani ɗanɗano.
*Efab metropolis Estate, Gwarinfa, Abuja.*
*10:18 na dare.*
MUKTAR POV.
Motar Ali ce ta yi parking a ƙofar gidan. Sannan a hankali ƙofar dake gefen driver ta buɗe. Ya fito daga cikin motar, sannan ya rage tsayinsa ya leƙa kansa ƙasan windown. Yana kallon Ali dake cikin motar.
“Gobe ka zo ka ɗaukeni da misalin karfe takwas!”
“Okay sir!”
Ali ya amsa.
“Sai da safe!”
“Sai da safe sir”
Daga haka ya miƙe, sanna ya juya ya nufi gate ɗin gidansu. Motarsa da Ali ke ja na barin wurin aka haske shi da fitilar babur. Hakan ya sa ya kare fuskarsa da hannunsa ɗaya. Sannan ya juyo yana son ganin mashin ɗin. Amma kuma yanda me mashin ɗin ya haske shi ya sa bai iya ganin mashin ɗin ballantana me shi.
A lokaci guda tunaninsa ya hasko masa lokacin da ya lura da wani me mashin da yake bibiyarsu. Sai ya yi murmushi, sannan ya juya bayansa yana sauƙe hannunsa da ya rufe fuskarsa da shi. Sannan hankali kwance ya ƙwanƙwasa ƙaramar ƙofar shiga gidansu.
Ganin haka ya sa me mashin ɗin ya tako mashin ɗin nasa da gudu. Ya iyo kan Muktar da shi. Sai dai kafin ya kai ga isa inda yake har me gadin gidan ya buɗe ƙofar, shi kuma Muktar sai ya yi amfani da wannan damar ya faɗa cikin gidan da sauri. Sanna ya datse ƙofar gidan.
“Yallaɓai lafiya?”
Me gadin da ya buɗe masa ƙofar ya tambaya. Amma Muktar bai amsa shi ba. Sai wayarsa da ya zaro ya aikawa da Ali kira.
“Hello Ali. Idan baka yi nisa ba ina so ka dawo da gaggawa. Wannan mutumin na kan mashin ne ya biyoni har gida ina so ka dawo ka tare min shi!”
Ya faɗi bayan da Ali ya ɗaga kiran.
“Okay sir”
Ali ya amsa daga cikin wayar. Muktar ya kashe wayar, sannan ya sauƙeta daga kunnensa. Ya ƙara matsawa jikin gate ɗin ya leƙa. Sai ya ga har yanzu mashin ɗin na nan. Ya dawo baya yana kaikawo. Shi ko me gadi ya sa shi a gaba yana kallo, dan ya kasa gane abin da yake faruwa.
Yana tsaye a wurin ya ji dirin motarsa da Ali ya dawo da ita. Hakan ya sa ya buɗe ƙofar da sauri ya fita. Amma sai ya ga me mashin ɗin ya tayar da shi ya ja shi da gudu. Kuma shi ma Alin sai ya bi bayansa da mota. Yana tsaye a wurin Ali ya dawo. Kuma tun da ya ga Alin ya dawo shi kaɗai ya san cewa bai samu damar kama shi ba.
“Sir ya kufce mana”
Faɗin Ali da ya fito daga mota. Ba tare da yace komai ba ya gyaɗa kansa. Sannan ya sallami Ali ya koma cikin gidan. Ya tsaya a wurin me gadi tare da faɗa masa cewar.
“Duk wanda ya zo kada ka kuskura ka buɗe masa gate ɗin nan.!”
Me gadi ya gyaɗa kai cike da bin umarni. Dan tun da ya ji haka to akwai matsala. Daga wannan umarnin Muktar ya juya ya nufi cikin gidan. A ƙofar shiga falo ya cire takalman ƙafarsa, sannan ya buɗe ƙofar falon ya sa kai, bakinsa ɗauke da sallama. Mahaifiyarsa da kuma ƙaninsa dake zaune a falon ne suka amsa masa. Kuma a tare suka dube shi.
“Ya Mukhy sannu da zuwa”
Ya yi murmushi yana kallon ƙaninsa.
“Sannu Walid... Karatu ake ne?”
Ya tambaya yana kallon littatafan dake gaban Walid ɗin. A lokaci guda kuma yana zama kusa da mahaifyarsa.
“Eh, muna da test on monday”
“To Allah ya taimaka... Mama ina wuni”
Ya ƙarashe yana gaida mahaifiyarsu. Mama ta amsa da murmushi.
“Lafiya Muktar. An dawo ke nan?”
“Eh Wallahi... Bari na je na ɗan watsa ruwa na zo na ci abinci”
Ya faɗa yana miƙewa tsaye.
“To sai ka fito”
Ya gyaɗa kansa. Sannan ya nufi corridorn dake ƙunshe da ɗakunansu shi da Walid. Ɗakinsa ya shiga. Kuma ya na shiga ya kulle ƙofar ɗakin. Sannan ya zaro wayarsa ya aikawa Kaigama ƙira. Bugu uku ya ɗaga da sallama.
“Wa alaikassalam. Kaigama!”
Daga ɗayan ɓangaren Faruk ya amsa.
“Na'am Mukhy... Fatan dai lafiya?”
“Lafiya, amma ba lau ba...”
Nan ya kwashe kaf abin da ya faru tun daga ranar da ya je BB hotel domin bincike har zuwa kan wanda ya faru yau. Ya zauna a bakin gadonsa yana ƙarawa da.
“... Duk yanda aka yi wannan mai laifin ba mutum ɗaya ba ne. Wata ƙila su biyu ne, ko uku, ko huɗu. Ko kuma ƙungiya garesu. Kuma ina da tabbacin suna da ƙarfin ikon yin duk abinda suke so. Saboda idan ba haka ba babu ta inda za ayi su shigo unguwarmu. Ka san yanda matakan tsaro suke da tsauri a nan. Ammz abin yana bani mamaki!”
Faruk ya sauƙe numfashi. Sannan yace.
“Mukhy! Idan har kana ganin wannan case ɗin zai iya shafar personal life ɗinka zai fi kyau ka aje shi. Ni da MJ za mu iya ƙarasa shi!”
Muktar ya girgiza kansa.
“Kaigama. A baya ban sanka ba, amma wannan binciken shi ne ya haɗani da kai. Kuma tun da na fara wannan binciken ba na jin zan aje shi ba tare da na kai ƙarshensa ba. Idan har zan ji tsoron abin da zai same ni ko ahalina a kan aikina to me ya sa zan fara?. Da ma can na riga na saba da irin wannan abin... So dan haka ba na so ka saka kanka a cikin damuwa, zan ci gaba da bincike a kan wannan case ɗin har sai na kama me laifin nan!...”
Faruk ya yi murmushi.
“Na gode sosai Muktar. Allah ya saka da alkairi”
“Kada ka damu. Da yardar Allah mun kusa kaiwa ƙarshen wannan binciken. Duk wani ci gaban da aka samu i will give you a touch!”
“Na gode sosai. Sai da safe”
“Okay sai da safe”
Muktar ya aje wayar, sannan ya shafa kansa. Ya yi shiru yana nazari, bisa ga dukkan alamu wanna case ɗin ba ƙarami ba ne kamar yanda suke tunani. Dan haka yana buƙatar faɗaɗa tunaninsa domin kaiwa ƙarshensa. Daga haka ya miƙe tsaye, sannan ya shiga barthroom dan ya watsa ruwa a jikinsa.
*No.53, off Justice Clara Ogunbiyi street, Asokoro, Abuja.*
MIMA POV.
Ita da wata cousin sisternsu ne zaune a falo suna gulmar Mu'az. Mima ta dage tana shararowa budurwar me suna Zulaihat labarin kalar cin abinci irin na Mu'az.
“... Kin ga fa waccan layyar haka bawan Allahnan ya cinye rabin ragon da ya yanka tun a ranar farko!”
Zulaihat ta zare ido cikin faɗin.
“Rabin rago fa Mima? Ban da sharri dai!”
Mima ta taɓe baki.
“Wallahi da gaske nake. Kin san ai ba zan miki ƙarya ba. Kin san Anti Maryama ce ta zo ta tayamu suya waccan layyar. To in faɗa miki Ya Mu'az zuwa ya yi compound ya aje kujera, ya hau ya zauna yana aika Na'im ya je ya ɗebo masa idan an soya. Ana soyawa yana ci, kan ki ce me har naman ya faɗa. Haka Anti Maryama ta yi ta mamakin ƙarewar naman. Da aka tambayi Gogan ina nama sai yace ai shi ya cinye kayansa. Anti Maryama har da cewa an yakuwa Mu'az mutum ne?”
Zulaihat ta kwashe da dariya Mima na tayata.
“Wallahi. Ai wannan mutumin da kika ganshi kura ma haka ta ga ta ƙyale a kan cin nama. Ya Mu'az? Humm!”
Bata kai ga rufe bakinta ba, Mu'az ɗin ya buɗe ƙofar falo ya shigo. Saurin gimtse bakinta ta yi. Ta shiga zara ido tana faɗin ta shiga uku a ranta. Dan ta ɗauka cewa ya ji abin da tace, idan kuwa har ya ji ai yau sai ɗan buzunta a gidan nan.
Amma kuma sai ta ga ko kallonta bai yi ba har ya zauna a kan sofa. Hakan ya sa ta gane cewa bai ji abin da tace ba. Ajiyar zuciya ta yi, dan ta san da ace ya ji babu abin da zai hana ya lakaɗa mata na jaki. Saboda Mu'az bai iya kauda kai a kan laifi ba. Daga zarar an masa yake mayar da martani.
Amma kuma ba shi da ruƙo. Dan daga zarar ka masa laifi ya amayar da abinda ka masa zai manta, mintuna kaɗan za ka ga ya dawo yana maka magana da kansa. Kuma da ma yawancin mutum mafaɗaci haka yake.
A sace ta ci gaba da kallonsa. Har ta lura da kamar akwai abin da yake damunsa. Ta riga da ta san halin yayanta. Abu ne mawuyaci ya ganta zaune a falo bai mata magana ba. Ko da ko ita bata fara masa maganar ba, ko tsokanarta ne zai yi.
“Ya Mu'az ina wuni”
Zulaihat ta gaida shi. Sai ya juyo ya kallesu da mamaki. Dan shi a sanda ya shigo kwata-kwata tunaninsa bai ba shi cewar akwai wani ɗan adam a falon ba.
Kuma ba komai ya ja hakan ba face wani halin damuwa da zuciyarsa ta shiga yau kaɗai. Gaba ɗaya tun bayan abin da ya faru a Ummul Banat boutique ya rasa nutsuwarsa. Zuciyarsa da gangar jikinsa na faɗa masa cewar ya aikata ba dai-dai ba.
Amma ita ko da wuƙa za'a ɗora a wuyanta ace nawa ne albashinta ba ta sani ba. Ko kalarsu ba ta gani, daga an yi albashi Kawu Sani yake zuwa ya karɓa da kansa. Tsakaninta da shi kawai shi ne kuɗin abin hawa.
Gaba ɗaya yau zuciyarta ta fi ko yaushe jagulewa. Na farko abin da Wannan koɗɗaɗen mugun sojan ya mata. Na biyu ga kumatunta da take jinsa kamar ba a jikinta yake ba. Sai kuma wannan tuwon da take cinsa a dole. Dan cusawa kawai take. Amma sam bakinta babu wani ɗanɗano.
*Efab metropolis Estate, Gwarinfa, Abuja.*
*10:18 na dare.*
MUKTAR POV.
Motar Ali ce ta yi parking a ƙofar gidan. Sannan a hankali ƙofar dake gefen driver ta buɗe. Ya fito daga cikin motar, sannan ya rage tsayinsa ya leƙa kansa ƙasan windown. Yana kallon Ali dake cikin motar.
“Gobe ka zo ka ɗaukeni da misalin karfe takwas!”
“Okay sir!”
Ali ya amsa.
“Sai da safe!”
“Sai da safe sir”
Daga haka ya miƙe, sanna ya juya ya nufi gate ɗin gidansu. Motarsa da Ali ke ja na barin wurin aka haske shi da fitilar babur. Hakan ya sa ya kare fuskarsa da hannunsa ɗaya. Sannan ya juyo yana son ganin mashin ɗin. Amma kuma yanda me mashin ɗin ya haske shi ya sa bai iya ganin mashin ɗin ballantana me shi.
A lokaci guda tunaninsa ya hasko masa lokacin da ya lura da wani me mashin da yake bibiyarsu. Sai ya yi murmushi, sannan ya juya bayansa yana sauƙe hannunsa da ya rufe fuskarsa da shi. Sannan hankali kwance ya ƙwanƙwasa ƙaramar ƙofar shiga gidansu.
Ganin haka ya sa me mashin ɗin ya tako mashin ɗin nasa da gudu. Ya iyo kan Muktar da shi. Sai dai kafin ya kai ga isa inda yake har me gadin gidan ya buɗe ƙofar, shi kuma Muktar sai ya yi amfani da wannan damar ya faɗa cikin gidan da sauri. Sanna ya datse ƙofar gidan.
“Yallaɓai lafiya?”
Me gadin da ya buɗe masa ƙofar ya tambaya. Amma Muktar bai amsa shi ba. Sai wayarsa da ya zaro ya aikawa da Ali kira.
“Hello Ali. Idan baka yi nisa ba ina so ka dawo da gaggawa. Wannan mutumin na kan mashin ne ya biyoni har gida ina so ka dawo ka tare min shi!”
Ya faɗi bayan da Ali ya ɗaga kiran.
“Okay sir”
Ali ya amsa daga cikin wayar. Muktar ya kashe wayar, sannan ya sauƙeta daga kunnensa. Ya ƙara matsawa jikin gate ɗin ya leƙa. Sai ya ga har yanzu mashin ɗin na nan. Ya dawo baya yana kaikawo. Shi ko me gadi ya sa shi a gaba yana kallo, dan ya kasa gane abin da yake faruwa.
Yana tsaye a wurin ya ji dirin motarsa da Ali ya dawo da ita. Hakan ya sa ya buɗe ƙofar da sauri ya fita. Amma sai ya ga me mashin ɗin ya tayar da shi ya ja shi da gudu. Kuma shi ma Alin sai ya bi bayansa da mota. Yana tsaye a wurin Ali ya dawo. Kuma tun da ya ga Alin ya dawo shi kaɗai ya san cewa bai samu damar kama shi ba.
“Sir ya kufce mana”
Faɗin Ali da ya fito daga mota. Ba tare da yace komai ba ya gyaɗa kansa. Sannan ya sallami Ali ya koma cikin gidan. Ya tsaya a wurin me gadi tare da faɗa masa cewar.
“Duk wanda ya zo kada ka kuskura ka buɗe masa gate ɗin nan.!”
Me gadi ya gyaɗa kai cike da bin umarni. Dan tun da ya ji haka to akwai matsala. Daga wannan umarnin Muktar ya juya ya nufi cikin gidan. A ƙofar shiga falo ya cire takalman ƙafarsa, sannan ya buɗe ƙofar falon ya sa kai, bakinsa ɗauke da sallama. Mahaifiyarsa da kuma ƙaninsa dake zaune a falon ne suka amsa masa. Kuma a tare suka dube shi.
“Ya Mukhy sannu da zuwa”
Ya yi murmushi yana kallon ƙaninsa.
“Sannu Walid... Karatu ake ne?”
Ya tambaya yana kallon littatafan dake gaban Walid ɗin. A lokaci guda kuma yana zama kusa da mahaifyarsa.
“Eh, muna da test on monday”
“To Allah ya taimaka... Mama ina wuni”
Ya ƙarashe yana gaida mahaifiyarsu. Mama ta amsa da murmushi.
“Lafiya Muktar. An dawo ke nan?”
“Eh Wallahi... Bari na je na ɗan watsa ruwa na zo na ci abinci”
Ya faɗa yana miƙewa tsaye.
“To sai ka fito”
Ya gyaɗa kansa. Sannan ya nufi corridorn dake ƙunshe da ɗakunansu shi da Walid. Ɗakinsa ya shiga. Kuma ya na shiga ya kulle ƙofar ɗakin. Sannan ya zaro wayarsa ya aikawa Kaigama ƙira. Bugu uku ya ɗaga da sallama.
“Wa alaikassalam. Kaigama!”
Daga ɗayan ɓangaren Faruk ya amsa.
“Na'am Mukhy... Fatan dai lafiya?”
“Lafiya, amma ba lau ba...”
Nan ya kwashe kaf abin da ya faru tun daga ranar da ya je BB hotel domin bincike har zuwa kan wanda ya faru yau. Ya zauna a bakin gadonsa yana ƙarawa da.
“... Duk yanda aka yi wannan mai laifin ba mutum ɗaya ba ne. Wata ƙila su biyu ne, ko uku, ko huɗu. Ko kuma ƙungiya garesu. Kuma ina da tabbacin suna da ƙarfin ikon yin duk abinda suke so. Saboda idan ba haka ba babu ta inda za ayi su shigo unguwarmu. Ka san yanda matakan tsaro suke da tsauri a nan. Ammz abin yana bani mamaki!”
Faruk ya sauƙe numfashi. Sannan yace.
“Mukhy! Idan har kana ganin wannan case ɗin zai iya shafar personal life ɗinka zai fi kyau ka aje shi. Ni da MJ za mu iya ƙarasa shi!”
Muktar ya girgiza kansa.
“Kaigama. A baya ban sanka ba, amma wannan binciken shi ne ya haɗani da kai. Kuma tun da na fara wannan binciken ba na jin zan aje shi ba tare da na kai ƙarshensa ba. Idan har zan ji tsoron abin da zai same ni ko ahalina a kan aikina to me ya sa zan fara?. Da ma can na riga na saba da irin wannan abin... So dan haka ba na so ka saka kanka a cikin damuwa, zan ci gaba da bincike a kan wannan case ɗin har sai na kama me laifin nan!...”
Faruk ya yi murmushi.
“Na gode sosai Muktar. Allah ya saka da alkairi”
“Kada ka damu. Da yardar Allah mun kusa kaiwa ƙarshen wannan binciken. Duk wani ci gaban da aka samu i will give you a touch!”
“Na gode sosai. Sai da safe”
“Okay sai da safe”
Muktar ya aje wayar, sannan ya shafa kansa. Ya yi shiru yana nazari, bisa ga dukkan alamu wanna case ɗin ba ƙarami ba ne kamar yanda suke tunani. Dan haka yana buƙatar faɗaɗa tunaninsa domin kaiwa ƙarshensa. Daga haka ya miƙe tsaye, sannan ya shiga barthroom dan ya watsa ruwa a jikinsa.
*No.53, off Justice Clara Ogunbiyi street, Asokoro, Abuja.*
MIMA POV.
Ita da wata cousin sisternsu ne zaune a falo suna gulmar Mu'az. Mima ta dage tana shararowa budurwar me suna Zulaihat labarin kalar cin abinci irin na Mu'az.
“... Kin ga fa waccan layyar haka bawan Allahnan ya cinye rabin ragon da ya yanka tun a ranar farko!”
Zulaihat ta zare ido cikin faɗin.
“Rabin rago fa Mima? Ban da sharri dai!”
Mima ta taɓe baki.
“Wallahi da gaske nake. Kin san ai ba zan miki ƙarya ba. Kin san Anti Maryama ce ta zo ta tayamu suya waccan layyar. To in faɗa miki Ya Mu'az zuwa ya yi compound ya aje kujera, ya hau ya zauna yana aika Na'im ya je ya ɗebo masa idan an soya. Ana soyawa yana ci, kan ki ce me har naman ya faɗa. Haka Anti Maryama ta yi ta mamakin ƙarewar naman. Da aka tambayi Gogan ina nama sai yace ai shi ya cinye kayansa. Anti Maryama har da cewa an yakuwa Mu'az mutum ne?”
Zulaihat ta kwashe da dariya Mima na tayata.
“Wallahi. Ai wannan mutumin da kika ganshi kura ma haka ta ga ta ƙyale a kan cin nama. Ya Mu'az? Humm!”
Bata kai ga rufe bakinta ba, Mu'az ɗin ya buɗe ƙofar falo ya shigo. Saurin gimtse bakinta ta yi. Ta shiga zara ido tana faɗin ta shiga uku a ranta. Dan ta ɗauka cewa ya ji abin da tace, idan kuwa har ya ji ai yau sai ɗan buzunta a gidan nan.
Amma kuma sai ta ga ko kallonta bai yi ba har ya zauna a kan sofa. Hakan ya sa ta gane cewa bai ji abin da tace ba. Ajiyar zuciya ta yi, dan ta san da ace ya ji babu abin da zai hana ya lakaɗa mata na jaki. Saboda Mu'az bai iya kauda kai a kan laifi ba. Daga zarar an masa yake mayar da martani.
Amma kuma ba shi da ruƙo. Dan daga zarar ka masa laifi ya amayar da abinda ka masa zai manta, mintuna kaɗan za ka ga ya dawo yana maka magana da kansa. Kuma da ma yawancin mutum mafaɗaci haka yake.
A sace ta ci gaba da kallonsa. Har ta lura da kamar akwai abin da yake damunsa. Ta riga da ta san halin yayanta. Abu ne mawuyaci ya ganta zaune a falo bai mata magana ba. Ko da ko ita bata fara masa maganar ba, ko tsokanarta ne zai yi.
“Ya Mu'az ina wuni”
Zulaihat ta gaida shi. Sai ya juyo ya kallesu da mamaki. Dan shi a sanda ya shigo kwata-kwata tunaninsa bai ba shi cewar akwai wani ɗan adam a falon ba.
Kuma ba komai ya ja hakan ba face wani halin damuwa da zuciyarsa ta shiga yau kaɗai. Gaba ɗaya tun bayan abin da ya faru a Ummul Banat boutique ya rasa nutsuwarsa. Zuciyarsa da gangar jikinsa na faɗa masa cewar ya aikata ba dai-dai ba.