Sashe 48
Jarabta Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ko hanunta bata iya dagawa da kyau sabida wahala, sallama adaddafe da taimakon shi tayi, ya kwanta agefenta sai dariya yakemata hakan yace "hukuncin ki kenan" aiko ta dinga rusamai kukan shagwaba hakadai ya dinga aikin lallashi har wuraren bayan sallan la'asar ganin taji sauki yasa ya shirya ta sukaje gidansu Abba nan aka zauna aka dinga hira har saida sukaci abincin dare sanan Abba yace sutashi sutafi gidansu.
Suna shiga gidan tafara kukan shagwaba dan batason yakara bata wuya irin najiya, aiko share ta yayi yawuce daki ganin taki zuwa yasa yazo ya dauketa kaman baby yasa taje tai wanka, bayan tafito da kanshi ya shiryata yadawo da ita kan gadon ya zauna tareda sanya kanta akan kirjinshi yana shafawa ahankali ya shiga bata labarin Eesha, dayazo wurin mutuwarta da abubuwan daya sameshi bayan ta rasu yasa ta dinga kuka dan bakaramin tausayi yabataba tai taima Eesha addu'a sosai sanan ta cigaba da hawaye, da kyar yasamu ya lallabata tai bacci yana girgiza ta akirjinshi. Washegari da sassafe Yusuf yakaisu airport sukabi jirgi suka tafi Abuja sabida yanada aiki da safen agida ya ijiyeta sanan yawuce office, da yamma yadawo yasami gidan tsaf sai kamshin turaren wuta yake dadi hakan yamai yasameta a dakinta yace "shirya mufita" da sauri ta tashi tana murna ta shirya tai kyau da ita, hanunta yakama yarike suka fita compound mota yabude mata ta shiga shima ya zagaya ya shiga anguwan su taga sunje tanata murna tazaci gidansu zashi saitaga yay parking agaban wani gida dake kusa da nasu yafito yabude mata suka shiga compound din tare, sallama yayi abakin kofa Mum ta amsa tace "muryan Khaleel nakeji, ga ango ga ango, Auta jeka cemai ya shigo" tashi Auta yay da gudu yazo yabude kofa turus ya tsaya yana nuna Islam yace "Anty aita" yajuya da sauri yakoma wajen Mum yace "Mumy Anty aita tadawo daga tafiyan da kikace tayi" ahankali ta daga kai ta kalli Khaleel da jikinshi yay sanyi sosai dan murmushi yamata yace "nanne gidansu Eesha, mu shiga" hanunta yarike suka shiga ciki sai yanzu Mum tagane mai Auta ke nufi, tsayawa turus tayi tana kallon Islam ko kwakkwaran motsi takasa, hanunta Khaleel yasaki yamata alamu taje dadan saurin ta Islam taje tafada jikin Mum tawani fashe da kuka dan wani irin mugun tausayi da son matan taji tanaji, kanen Eesha su Ibrahim da Faty da Auta yaje yakira duk tsayawa sukayi suna kallon Mum da Islam yanda Islam ta kankameta tana kuka, da kyar Mum ta tattaro karfinta taciro ta daga jikinta hannu tasa ta sharemata hawayen datake itama ta share nata murmushi tayi ta kama hanunta ta zaunar da ita akan kujera ta kalli faty tace "kuje ku kawo musu abun sha" tajuyo ta kalli Islam tace "ya sunanki baiwar Allah kina mugun kama da marigayiya Aisha badadan nasan tariga tarasu ba da sainace kece wlh" kwalla Islam takara sharewa ahankali tace "Allah jikanta da rahama Mumy" dukan su sukace amin, Khaleel yay murmushi yace "Mum sunanta Islam, lokacin dana fara ganinta a yola haka nadinga binta nima" murmushi Mum tayi tana kara kallon Islam din hatta yanayin sanyinta irin na Eesha ne ahankali tace "ikon Allah kenan gaskiyar kakan mu tana yawan cewa mutum bibbiyu bibbiyu ake hallittar su aduniya, Allah sa mucika da imani" haka suka zauna dasu Mum da kanin Eesha dasuka zagaye Islam sunata mata labarai wani irin son yaran taji tanaji hakanan sai taji kaman kanninta najini ne, bayana sallan isha ma tareda Abba suka dawo shima yay mamakin ganin Islam, basu bar gidanba saida mum ta cikasu da alkairai gidansu suka biya sanan suka wuce gida.
Bayan wata hudu
Rayuwa sai tafiya take yayinda bikin Yusuf yau saura sati daya dawata yar abokin Abban su aka hadashi yana ganin yarinyar kuma yaji ta kwanta mai. Farida kuma hakanan ta yardar ma wani guy daya nace mata badan tadaina son superman dinta ba, nan Abba ya binciko halin yaron yarone nagari barrister ne hakan yasa Abba yace yaturo akasa biki wata biyu.
Akai akai Mum ke turo kanin Eesha suzo sumata wuni, hakan bakaramin dadi yake mata ba, tana mugun son yaran dan suna da hankali ga ilimin addini.
Ranan Friday da yamma suka sauka ayola kasancewa gobe ne daurin auren Yusuf, adaddafe tai sallan isha sabida yanda zazzabi duk yabi yarufe ta hakan yasa Khaleel yadamu da kyar taci abinci yabata paracetamol tasha yace inhar zazzabin bai kwanta ba asibiti xasu gobe nan bacci yay gaba da ita ya gyaramata kwanciya, koda safiya da karfinta ta tashi ta shirya da sauri cikin ankon su na family miji wani blue atampa ba karamin kyau yamata ba yafito da hasken fatanta sosai, gashi tai bulbul da ita, sai kallonta yake ganin yanda ta cicciko, shiryawa shima yayi cikin fara shaddan ankon dasukayi da angon yadauko hijabi yasaka mata sanan yakama hanunta suka fito har gidansu sassan goggo ya kaita ya kalli Goggo yace "kuma kar asamin mata aiki dan batajin dadi" harara goggo ta watsamai tace "nikake ma fi'ili munafiki mtswwe" taja tsaki tareda rike hanun Islam tajata zuwa uwar dakanta, murmushi yayi yajuya yafita ganin Yusuf na kiranshi, gidan yacika makil da mutane itadai tana taredasu Ihsan a bangaren goggo zuciyar ta sai tashi yake sabida yanda kamshi turare kala kala na mutane ke shiga hancin ta, yatsine fuska tayi ta kwanta akan gado tana juye juye Ihsan tace "lpy ki Islam" bata iya amsata ba sabida wani irin amai dayazo mata da gudu tai bayi ta dinga kwararawa hankalin su Ihsan dukya tashi, haka ta dinga amai tun suna zatan maybe batasan mutane ne ko hayaniya hardai Fa'iza da gudu taje ta kira su Mumy da Goggo dake waje wajen baki, Koda suka iso tana kwance kan gado kaman numfashin ta zai dauke Ihsan na fifitata, Ammi ne ta dagota zaune ta taba kanta tace "meke miki ciwo daughter" kasa magana tayi ta fashe musu da kuka tana wani irin mikewa tana yunkurin amai amma babu abinda ke fita sabida dukta amaayar da abin cikinta ga jikinta zafi, arikice goggo tace "na shiga uku, uban mekuka bata taci?" yanda goggo tai maganan yasa su Ihsan duk suka rude mu bamu bata komiba, Umma ta kalli Fa'iza tace "daukomin car key mu kaita asibiti tunda duk mazan suna wajen daurin aure" da kyar ta iya tashi da taimakon Ammi suka riketa suka sakata amota akai asibiti da ita, gado aka bata akamata allurai a drip na tsayar da amai, gwajin farko ya nuna ciki gareta na kimanin wata daya aiko zokaga murna wurin su Ammi da Umma dan subiyu kawai suka kawota sukabar Goggo dasu Ihsan agida, nan dai Dr yace "bari inta tashi zasu iya tafiya, zai rubuta mata wasu magunguna" arude Khaleel ya shigo asibitin daga wurin daurin aure danhar Ihsan takira ta fesamai, ganin su Umma namai wani irin kallo yasa ya dauke kai yawani shamur ya kalli Dr dake mikamai hannu yace "kaine mijin wacce suka kawo" Khaleel ya gyadamai kai yana waige waige dan neman ta yake "congratulations Matar ka nada juna biyu" juyowa Khaleel yayi ya kalli Dr baisan lokacin daya daga Dr samaba abunku damai karfi yana wani jujjuya shi, dakin dayaga Ammi ta shiga tana tabe baki ya ijiye Dr yace "am coming" da sauri yabi bayan Ammi ya shiga bacci yaga tanayi ga drip ansamata wani irin dadine ya lullube shi ya dinga godema Allah ranan dai Khaleel yay kyauta dayawa, Yusuf sai iskanci yakemai yana "ka godemin ranan bikina ne kasami gud news dinan" , harara ya ballamai yace "anjima dai zamu kaika kaima ka wurga kwallon cikin ragan ka ai" , baki Yusuf yarike yana kallon shi yace "ikon Allah damafa ance idan namiji yay aure fitsararre yake zama" tabe baki yayi yace "kaga tafiyata" yawuce abinshi, dan fita nemo mata goriba anyi anyi da ita mezataci tace zuciyarta tashi take wai goriba takeso 😂
Ba karamin kulawa Khaleel yake bataba itama dudda cikin nabata wahala bai hanata zakewa wurin bama mijin nata kulawa ba da nunamai tsantsan so, haka bayan wata biyu suka dawo bikin Farida sosai sukamata alkairai takuma musu godiya, Mum dai ko kala batace ma, koda zaakai Farida bai bari tajeba sabida batada wani cikakken lpy bayan kwana biyu suka dawo Abuja.
Farida ta rungumi mijinta dudda har yanzu son Mk na nan daram aranta amma tariga ta rungumi kaddara ta nunama zuciyar ta ba komi kakeso kasamu ba, saidai fa! Son superman dinta wani irin sone da Allah yasa ya shigeta lokaci daya dan haka shi kadai zai iya zare mata son nan lokacin daya.
Abba duk ran Friday yake kiran duk yaran nashi yaji lafiyar su tareda musu addu'a. Tsakanin Mum da Islam kuwa babu abinda ya chanza dama ance ba kowa bane zaisoka a duniyar nanba, takan kirata awaya ta gaisheta dudda sama sama take amsata, Anty Hindu kuwa har Abuja takan zo ta duba Islam din.
Bayan shekara biyar.
Suna shiga gidan tafara kukan shagwaba dan batason yakara bata wuya irin najiya, aiko share ta yayi yawuce daki ganin taki zuwa yasa yazo ya dauketa kaman baby yasa taje tai wanka, bayan tafito da kanshi ya shiryata yadawo da ita kan gadon ya zauna tareda sanya kanta akan kirjinshi yana shafawa ahankali ya shiga bata labarin Eesha, dayazo wurin mutuwarta da abubuwan daya sameshi bayan ta rasu yasa ta dinga kuka dan bakaramin tausayi yabataba tai taima Eesha addu'a sosai sanan ta cigaba da hawaye, da kyar yasamu ya lallabata tai bacci yana girgiza ta akirjinshi. Washegari da sassafe Yusuf yakaisu airport sukabi jirgi suka tafi Abuja sabida yanada aiki da safen agida ya ijiyeta sanan yawuce office, da yamma yadawo yasami gidan tsaf sai kamshin turaren wuta yake dadi hakan yamai yasameta a dakinta yace "shirya mufita" da sauri ta tashi tana murna ta shirya tai kyau da ita, hanunta yakama yarike suka fita compound mota yabude mata ta shiga shima ya zagaya ya shiga anguwan su taga sunje tanata murna tazaci gidansu zashi saitaga yay parking agaban wani gida dake kusa da nasu yafito yabude mata suka shiga compound din tare, sallama yayi abakin kofa Mum ta amsa tace "muryan Khaleel nakeji, ga ango ga ango, Auta jeka cemai ya shigo" tashi Auta yay da gudu yazo yabude kofa turus ya tsaya yana nuna Islam yace "Anty aita" yajuya da sauri yakoma wajen Mum yace "Mumy Anty aita tadawo daga tafiyan da kikace tayi" ahankali ta daga kai ta kalli Khaleel da jikinshi yay sanyi sosai dan murmushi yamata yace "nanne gidansu Eesha, mu shiga" hanunta yarike suka shiga ciki sai yanzu Mum tagane mai Auta ke nufi, tsayawa turus tayi tana kallon Islam ko kwakkwaran motsi takasa, hanunta Khaleel yasaki yamata alamu taje dadan saurin ta Islam taje tafada jikin Mum tawani fashe da kuka dan wani irin mugun tausayi da son matan taji tanaji, kanen Eesha su Ibrahim da Faty da Auta yaje yakira duk tsayawa sukayi suna kallon Mum da Islam yanda Islam ta kankameta tana kuka, da kyar Mum ta tattaro karfinta taciro ta daga jikinta hannu tasa ta sharemata hawayen datake itama ta share nata murmushi tayi ta kama hanunta ta zaunar da ita akan kujera ta kalli faty tace "kuje ku kawo musu abun sha" tajuyo ta kalli Islam tace "ya sunanki baiwar Allah kina mugun kama da marigayiya Aisha badadan nasan tariga tarasu ba da sainace kece wlh" kwalla Islam takara sharewa ahankali tace "Allah jikanta da rahama Mumy" dukan su sukace amin, Khaleel yay murmushi yace "Mum sunanta Islam, lokacin dana fara ganinta a yola haka nadinga binta nima" murmushi Mum tayi tana kara kallon Islam din hatta yanayin sanyinta irin na Eesha ne ahankali tace "ikon Allah kenan gaskiyar kakan mu tana yawan cewa mutum bibbiyu bibbiyu ake hallittar su aduniya, Allah sa mucika da imani" haka suka zauna dasu Mum da kanin Eesha dasuka zagaye Islam sunata mata labarai wani irin son yaran taji tanaji hakanan sai taji kaman kanninta najini ne, bayana sallan isha ma tareda Abba suka dawo shima yay mamakin ganin Islam, basu bar gidanba saida mum ta cikasu da alkairai gidansu suka biya sanan suka wuce gida.
Bayan wata hudu
Rayuwa sai tafiya take yayinda bikin Yusuf yau saura sati daya dawata yar abokin Abban su aka hadashi yana ganin yarinyar kuma yaji ta kwanta mai. Farida kuma hakanan ta yardar ma wani guy daya nace mata badan tadaina son superman dinta ba, nan Abba ya binciko halin yaron yarone nagari barrister ne hakan yasa Abba yace yaturo akasa biki wata biyu.
Akai akai Mum ke turo kanin Eesha suzo sumata wuni, hakan bakaramin dadi yake mata ba, tana mugun son yaran dan suna da hankali ga ilimin addini.
Ranan Friday da yamma suka sauka ayola kasancewa gobe ne daurin auren Yusuf, adaddafe tai sallan isha sabida yanda zazzabi duk yabi yarufe ta hakan yasa Khaleel yadamu da kyar taci abinci yabata paracetamol tasha yace inhar zazzabin bai kwanta ba asibiti xasu gobe nan bacci yay gaba da ita ya gyaramata kwanciya, koda safiya da karfinta ta tashi ta shirya da sauri cikin ankon su na family miji wani blue atampa ba karamin kyau yamata ba yafito da hasken fatanta sosai, gashi tai bulbul da ita, sai kallonta yake ganin yanda ta cicciko, shiryawa shima yayi cikin fara shaddan ankon dasukayi da angon yadauko hijabi yasaka mata sanan yakama hanunta suka fito har gidansu sassan goggo ya kaita ya kalli Goggo yace "kuma kar asamin mata aiki dan batajin dadi" harara goggo ta watsamai tace "nikake ma fi'ili munafiki mtswwe" taja tsaki tareda rike hanun Islam tajata zuwa uwar dakanta, murmushi yayi yajuya yafita ganin Yusuf na kiranshi, gidan yacika makil da mutane itadai tana taredasu Ihsan a bangaren goggo zuciyar ta sai tashi yake sabida yanda kamshi turare kala kala na mutane ke shiga hancin ta, yatsine fuska tayi ta kwanta akan gado tana juye juye Ihsan tace "lpy ki Islam" bata iya amsata ba sabida wani irin amai dayazo mata da gudu tai bayi ta dinga kwararawa hankalin su Ihsan dukya tashi, haka ta dinga amai tun suna zatan maybe batasan mutane ne ko hayaniya hardai Fa'iza da gudu taje ta kira su Mumy da Goggo dake waje wajen baki, Koda suka iso tana kwance kan gado kaman numfashin ta zai dauke Ihsan na fifitata, Ammi ne ta dagota zaune ta taba kanta tace "meke miki ciwo daughter" kasa magana tayi ta fashe musu da kuka tana wani irin mikewa tana yunkurin amai amma babu abinda ke fita sabida dukta amaayar da abin cikinta ga jikinta zafi, arikice goggo tace "na shiga uku, uban mekuka bata taci?" yanda goggo tai maganan yasa su Ihsan duk suka rude mu bamu bata komiba, Umma ta kalli Fa'iza tace "daukomin car key mu kaita asibiti tunda duk mazan suna wajen daurin aure" da kyar ta iya tashi da taimakon Ammi suka riketa suka sakata amota akai asibiti da ita, gado aka bata akamata allurai a drip na tsayar da amai, gwajin farko ya nuna ciki gareta na kimanin wata daya aiko zokaga murna wurin su Ammi da Umma dan subiyu kawai suka kawota sukabar Goggo dasu Ihsan agida, nan dai Dr yace "bari inta tashi zasu iya tafiya, zai rubuta mata wasu magunguna" arude Khaleel ya shigo asibitin daga wurin daurin aure danhar Ihsan takira ta fesamai, ganin su Umma namai wani irin kallo yasa ya dauke kai yawani shamur ya kalli Dr dake mikamai hannu yace "kaine mijin wacce suka kawo" Khaleel ya gyadamai kai yana waige waige dan neman ta yake "congratulations Matar ka nada juna biyu" juyowa Khaleel yayi ya kalli Dr baisan lokacin daya daga Dr samaba abunku damai karfi yana wani jujjuya shi, dakin dayaga Ammi ta shiga tana tabe baki ya ijiye Dr yace "am coming" da sauri yabi bayan Ammi ya shiga bacci yaga tanayi ga drip ansamata wani irin dadine ya lullube shi ya dinga godema Allah ranan dai Khaleel yay kyauta dayawa, Yusuf sai iskanci yakemai yana "ka godemin ranan bikina ne kasami gud news dinan" , harara ya ballamai yace "anjima dai zamu kaika kaima ka wurga kwallon cikin ragan ka ai" , baki Yusuf yarike yana kallon shi yace "ikon Allah damafa ance idan namiji yay aure fitsararre yake zama" tabe baki yayi yace "kaga tafiyata" yawuce abinshi, dan fita nemo mata goriba anyi anyi da ita mezataci tace zuciyarta tashi take wai goriba takeso 😂
Ba karamin kulawa Khaleel yake bataba itama dudda cikin nabata wahala bai hanata zakewa wurin bama mijin nata kulawa ba da nunamai tsantsan so, haka bayan wata biyu suka dawo bikin Farida sosai sukamata alkairai takuma musu godiya, Mum dai ko kala batace ma, koda zaakai Farida bai bari tajeba sabida batada wani cikakken lpy bayan kwana biyu suka dawo Abuja.
Farida ta rungumi mijinta dudda har yanzu son Mk na nan daram aranta amma tariga ta rungumi kaddara ta nunama zuciyar ta ba komi kakeso kasamu ba, saidai fa! Son superman dinta wani irin sone da Allah yasa ya shigeta lokaci daya dan haka shi kadai zai iya zare mata son nan lokacin daya.
Abba duk ran Friday yake kiran duk yaran nashi yaji lafiyar su tareda musu addu'a. Tsakanin Mum da Islam kuwa babu abinda ya chanza dama ance ba kowa bane zaisoka a duniyar nanba, takan kirata awaya ta gaisheta dudda sama sama take amsata, Anty Hindu kuwa har Abuja takan zo ta duba Islam din.
Bayan shekara biyar.