← Book details Hauwa Kulu Part 4 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 23

Sashe 7

Hauwa Kulu Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sarham bai san sanda ya kankame Hauwa yana groaning kamar ransa zai fita ba. Yayi rantsuwa bai taba jin abinda yake ji a halin yanzu akan kowacce mace kafin yau ba. don ya san in soyayya tana kisa a yau zata kasheshi ne kowa ya huta Mama ta huta Hauwanma ta huta Madinar ma ta rasa

Alamarin da ya tsoratar da Hauwa don ta dauka Sarham suma yayi, amma jin yana gab da samun abinda yake hari da zafin da taji ya ankarar da ita abin da ke shirin faruwa a lokacin.
Janyewa ta soma yi cikin kokarin dawowa hayyacinta, Sarham kuwa a wannan lokacin ba ka jin komai a bakinsa sai “janye kalamansa na baya”, wani ma in ka ji sai ya ba ka dariya ya ce, Na ce miki I am not your brother, Im your loving husband, ki barni in nuna miki hakan yanzunnan, na rantse na fi ki shiga wahala a shekara dayan nan, ba mantawa na yi da ke ba, tunanin hanyar da zan nema miki lafiya nake yi.
Hauwa ta rikice da kuka da razanar alamarin da ke shirin faruwa da ita. Ta ce,
Don Allah Yaya Doctor ka bar ni in koma wa Mama lafiya wallahi wani abu ya same ni za ta gane. Ni ban taba yin wannan rashin kunyar ba. Ka rufa min asiri yadda Allah ya rufa maka.
Jikinsa ya yi mugun sanyi ganin tana neman shidewa don kuka da razana. Ya kifa kai a kan kirjinta ya yi shiru, kuzarin jikinsa ya ragu, ya daina duk abin da yake yi. Ya soma maida mata sitturun jikinta.
Ya kama hannunta ya dago ta ya dora ta bisa cinyoyinsa, fuskarsa a saman kafadunta ya sumbaci dogon wuyanta a hankali ya ce,
Does this make a difference? Daga yau za ki daina ce min Yaya Doctor?
Hauwa kamar ta ce kasar wajen ta tsage ta shige haka ta sa tafuka tana rufe fuska, shi kuwa ya kara rungume ta tsaf a jikinsa.
Sun dauki lokaci a haka, ba ka jin komai sai bugun zuciyoyinsu a kirjin junansu.

Karar wayarsa ce ta dawo dasu daga wata duniya mai ban mamaki da suka samu kawunansu cikin abinda bai gaza mintuna talatin ba. Yana dubawa ya ga Abba ke kira.
Kasa dagawa yayi, sai ga kiran Mama ita ma. Itama bai daga ba ya sauke Hauwa daga jikinsa bayan ya sumbaci kirjinta son ransa, ya kuma sake fidda su a hayyacinsu. Karar kiran wayar akai-akai duk ya dagawa Hauwa hankali, amma shi ko a jikinsa. Da kyar da lallashi da kalaman yarda da daukar alkawarin cewa,
Ni Hauwa na yarda Yaya Doctor ba Yayana ba ne, mijina ne na sunnah, kuma na janye kalmar a SAKE NI!.
Sarham ya kyale Hauwa yana murmushi da godiyar Ubangiji a fili, ya ce,
Saura mu je gaban Mama ki canza magana, wallahi sai kin san sauran, don a gidanta zaa yi komai kuma a dakin yar ta, don wallahi na gaji da bata hakuri, inyaso in ta ganki da ciki a gabanta ta janye kalmar saki, ta yarda auren Sarham da Hauwa;
Mutu ka raba ne..
Hauwa ta ce cikin dimuwa da tsoron wai zai iya irin wannan a dakin Sumayyah a gidan Mama, da sauri tace Na yarda, wallahi in ta ce ko inaso a yi saki? Zan ce aah.
Shi har dariya Hauwa ta ba shi, ya dara sosai yana bubbuga bayanta, domin ba karamin tsorata da alamarinsa ta yi ba.
Ko break fast din da ya sayo musu ba ta yarda ta ci ko loma daya ba, shi kuwa sai da ya ci abinsa cikin kwanciyar hankali kamar bashi ake ta kira a waya ba, sannan ya yarda suka fito.
Suna shiga mota ya yi reverse ya hau kan titi, sai a lokacin Hauwa ta ji wani irin kukan kunyar Mama ya zo mata.
Ta rasa da wace fuska za ta je wa Mama yau? Gani ta ke duk abin da suka yi din nan da Yaya Doctor is written on her forehead (a rubuce yake a kan goshinta). Sarham tuki yake yau wani irin tuki cikin nishadi. Kamar tayar motarsa ta samu matsala, ya dora hannunsa bisa nata, ya ce,
Cry more! Its all in LOVE! Wani kukan ma yarinya sai an je Jeddah.

Hauwa ta ce, cikin kuka Ni kam na shiga uku yau, Yaya Doctor ka jawo min nayi rashin kunya nayi rashin gaskiya na yi butulci, za ka jawo Mama ta daina tattalina, ka shiga tsakanin Uwa da yar ta.

My dear Jeddah, in ta daina tattalinki, ni zan yi kin ji?

Da sauri tace wallahi ba irin nata ba, dame zaka yi tattalin nawa? In dai irin wannan tattalin na rashin kunya ne wallahi ni na yafe. Dariya kamar ta kashe Sarham ya kara manne hannunsa cikin taushin fatar hannunta.
Suna isowa gidan dankam da yan daurin aure don nan ne meeting point inda daga nan zaa wuce Kofar Gadon kaya, sabida an cika kofar gidan su ba hanya sai ta kofar kitchen suka zaga ya bi da Hauwa zuwa cikin gidan, nan ya hadu da Nancy a hanya ya damka mata ita, ya ce ta kai ta dakinta. Sannan ya ce,
To Maijidda sai na zo zancen dare.
Ta yi saurin daga kafa tana gode Allah da Nancy ba ta jin Hausa. Kuma da ita suka fara haduwa
Jamaa kam sun dauke hankalin Mama, don haka har suka kai dakin Hauwa Mama tana falonta da kawayenta yan chamber dinsu, sau biyu tana shiga neman Hauwa, Mardiyyah na cewa tana wanka. Har a shigowa ta biyu Mama tace to wannan wankan na sake fata ne kenan?
Aka yi daurin auren Surayyah aka zarce da reception a ‘Niima Guest Palace, so sai ya zamanto har dare gidan ana kai kawo Mama uwar amarya kanta ya dinke da hidimar bakin da suka gayyato daga bangarenta dana Abba Prof. da suka zo daga Shanono.
Mardiyyah ce ta je ta karbo musu abinci, sai Mama ta ce mata ta je ta zo da Antinta ta gaida su Barr. Hannatu.
Hauwa ta sauke wata wahalalliyar ajiyar zuciyar hayewa tudun muntsira, bayan ta ji ta kwance a kan gadon dakinta ba tareda Mama ta san dawowarta ba, sannan ta biyo Mardiyyah suka fito.
Falon cike yake kuma duk manyan lauyoyi mata ne kawayen Mama.
Mama ta ce, Hauwa, yau wane irin wanka ki ke tun dazu kamar mai wankan jego? Shigata biyu ana cewa baki fito ba”.
Cikin in-ina ta ce,
Yiyi hakuri Mama.
Mama ta kada kai, ta ce, Kawayena ne na ce ki zo ku gaisa.
Suna ta kallon Hauwa da mamaki ban da Barr. Hannatu, tunda ita ba yau ta san Hauwa ba. Hauwa ta tsugunna tana gaishe su cikin ladabi ba tare da ta kalli sashen da kowacce ta ke ba. wannan ya tabbatar musu da cewa surukar Maishariah din bata gani.

Barr. Shafaatu ta kasa shiru, ta ce,
Ita ce second wife din Sarham da aka ce ba ta gani ko?
Barr. Habiba ta ce, So beautiful masha Allah, and so pathetic!.
Mama ta san halin yan kayanta, tuni Hauwa har ta fara kumburowa, ta ce da Mardhiyyah, Mardiyyah maza ku je falo cikin yan Shanono, ku daina kulewa a daki ku kadai bayan ga yan uwa duk sun zo, ki kai ta ta gaida kowa ki gabatar da ita kinji kafin nazo?.
Suna fita ta kama hanyar komawa daki wato bazata gun yan Shanonon ba. Mardiyyah ta ga Antinta na share hawaye. Yau an tabo ta, tunda an mata gorin ido. Cikin ikon Allah suna shiga dakin Sarham na shigowa. Ta kifa kai a jikin gado tana rusa kuka.
Ba karamin kaduwa yayi ba ya iso gareta da sauri, ya manta da Mardhiyyah a wajen yayi maza ya rungumota barin jikinsa na dama.
Mardiyya lafiya? Me aka yi mata? Ko kin fadawa Mama mun fita ne? Ya tambaya a dan rikice da damuwa.
Mardiyyah ta ce, Yaya Likita ba abinda aka yi mata, Mama kawai ta ce in raka ta ta gaida yan Shanono, kada ka dada kada ka rage shikenan fa!.
Hauwa ta dago ido tana hararar inda Mardiyya ta ke tsaye, ta ce, yi min shiru. Ba a kunnenki aka yi min GORIN IDO ba? Har tana ce mun abun tausayi, wani so pathetic?
Sarham ya zauna a gefen gadon yana hadiye dariya ce, nagode, je ki abinki Mardiyyah.
Ita dai bata ga abin kuka ba tunda ba da tozarci suka fada ba. Dukkansu manya ne. haka Mardhiyyah ta sa kai ta fita tana yar dariyar shagwabar Antin nata.
Ya sake kankameta yace, Kin ga Mardiyya ma dariya ta ke miki.
Eh, da yake ba ita aka cewa MAKAUNIYA ba.
To karya suke? Ina idon yake?

Ai kuwa Hauwa ta balle da sabon kuka riri-ririiiiii.
Sarham ya sa hannu a kwibinta yana mata cakulkuli, ta zame da mugun zafin nama.
Tashi ka fita, kafin a ce maka mijin makauniya kaima.
Sarham ya lumshe ido ya nuna kansa da dan alinsa kamar Hauwa na ganinsa, ya ce, Sai in ba su amsa da ni na makantar da matar tawa saboda rashin iya aiki na, daga cire hakiya. Ya kara rungumo ta ya manne bakinsu wuri guda yana sumbata hungrily, ta haka ya hana sautin kukan fitowa.

Ya salamu sallim, Ya jamilal Munzar (Ya mafi kyawun masu gani).
Chapter 7 · 0% Book details