← Book details Hauwa Kulu Part 4 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 23

Sashe 15

Hauwa Kulu Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Madinah dai na jin motsi a kitchen ba ta san waye ba, don haka ta fito don ganin waye a kitchen dinta kada ayi mata barna tunda ta san dai amaryar ba gani take ba.
Sarham ta gani ya yi kace-kace yana aikin girki. Yana hada zufa na rashin sabo. Ko iblis ce ita, dole ta ji ba dadi a ranta, zuciyarta kuma ta kara gasgata abubuwan da ya fada mata na matsayin da shi Sarham ya baiwa Hauwa-Kulu a rayuwarsa.
Yana kallonta ta zo kofar kitchen din ta koma cikin sauri, ga jin kishin mijinta na dafawa kishiyarta abinci ga guilty conscience daya hanata sakat, na cewa bata kyautawa, ta kasa zaune ta kasa tsaye, a tsakar dakinta, ta yaya ita za ta dinga dafawa miji abinci? Shi kuma ya zage kwanji yasa ‘apron’ ya dafawa kishiyarta?
Kuka wiwi Madina ta soma, abu goma da ashirin ya damu Dr. Madinah Sorondinki, a karshe ta yanke wa ranta fita sabgar Sarham da matarshi Hauwa-Kulu take ko Kululu! Gara ta saka su a gefe kafin su manna mata ciwon hauka.
Don cikin abubuwan da ya lissafa bakidaya wato abubuwanda ya bata zabi ciki har dana zama da shi ko aah? Ko yin muamala mai kyau da matarsa Hauwau, ko ta dinga dafa abinci tana bata ita tana kwana da miji, ko ta zauna da matarsa cikin aminci, babu wanda za ta iya aikatawa a cikinsu gabadaya.
Don haka ta yanke shawarar yin abinda take ganin ya fiye mata aala, wato komawa aikin asibiti, in yaso ta dauke ido daga kansu ta bar musu filin gidan ya cinye matarsa Hauwa-Kulu makauniya Kulu don soyayya.
Amma ita kam ta gama hada jiki da Sarham! Don zuciyarta ba za ta jure sharing miji da makauniya ba. Sannan ba za ta zabi zuwa gida ta yi rayuwar zawarci da yi masa rainon Waheedah a gidan iyayenta saboda kishiya ba.
A take ta dauki waya ta buga zuwa Dr. Siddiqah Hospital Jeddah. Zuciyarta a matukar kuntace. Hakika kishin mijin da kake matukar so abu ne mai matukar ciwo da sai wanda aka yiwa ne kawai zai iya bada labari. Amma abu daya zamu tuna mu kwantar da hankulanmu cewa auren mazajenmu sunnar Annabi ne, umarnin Ubangiji ne, na su aura daga abinda yayi musu dadi daga daya-daya ko biyu-biyu ko uku-uku har hur-hudu, don kare kansu daga dattin zina.
Abinda ya kamata Madinah da sauran mata irinta mu duba kenan, mu sassautawa zukatanmu.
Ta tabbatar musu da amsar aikinta da ta ce a dakatar sai ta yi yayen Waheedah, Dr. Madinah dai ta yi kyakkyawan kudiri na fita harkar mijinta a dalilin kishiyar da ta ke ganin ba ta isa zama kishiyarta ba, saboda makasar ido da Allah ya dora mata da kuma da asalinta.
Har gobe tana son Sarham dinta, kuma matsayinsa bai canza a zuciyarta ba, amma ta yanke shawarar jingine shi a kan dai ta yi sharing dinsa da Hauwa.
Maganar da ya yi na bata zabi na zama da shi ko aah ya girgiza ta, tabbas namiji ya baka option na zama da shi ko barinsa to hakika ya kasa jure drama dinka ne. Yanaso ya kawo karshen ta ya huta.
A rayuwarsu bata taba yi wa mijinta horon yunwa ba amma yau kishi ya koya mata, bata taba kwararsa a shimfidar auren su ba, amma yau duk kishi ya koya mata har ta kware da hakan, ta jingine komai na hidimar mijin, wato shi kansa Sarham din ta yafe, da ita kanta soyayyarsa da ke ranta duk ta basu baya, da bukatuwarta da shi a matsayinsa na mijin da ta ke matukar so wanda suka gama gina rayuwarsu tare duk ta yafe, tunda har ya iya rufe ido ya yi mata kishiyar da bata kai ta komai ba, a lokacin da bata taba tsammani ba, don haka duk ta hakura da su ta barwa yar cikin Badala, watakila ta hakan ne zai gano muhimmancinta da bambancin da ke tsakaninta da Hauwa.
Asibitin sun tabbatar mata ko a gobe ne ta zo ta yi reporting don suna matukar bukatarta dama. Don haka tun a daren ta ce ma Hajjah Ramlah gobe za ta kawo mata Waheedah zata fara zuwa aiki a Dr. Siddiqah.
Hajjah Ramlah da tausayi Madinah ke bata yanzu, don ta fahimci son da take ma Sarham ya zama jarabta ga rayuwarta, tunda har ya iya yi mata wannan tozarcin, amma ta kasa barinsa.
Ta ce, Ki kawo ta, bayan aiki ma ki kara da ayyukan sa-kai a asibitin gwamnati da philanthropic ayyuka duka, kuma ki ci gaba da tafiya programs da ki ke zuwa na marriage coaches rana daya kika daina yanzu, ki bar musu gidan tun safe har dare, in yaso ki barshi da makauniyar ya ci uwar da zai ci da ita, fitinannen yaro kawai marar godiyar Allah, ina ganinsa mai kirki ashe macijin sari ka noke ne, in ki ka daina wuni a gidan na ga wanda zai kula masa da makauniya.
Tunda aurensa ya zame miki jaraba kema dai kamar aka ce shi ne autan maza.
Murmushi Madinah ta yi, Hajjah ba za ta gane ba. Tabbas Sarham shi ne autan maza, amma a wurinta da duniyarta kadai, don ita kadai ta san ko waye shi, da darajojin da Allah ya yi masa, wadanda ba duka maza ya yi wa alfarmarsu ba.
Za ta ci gaba da zama karkashin aurensa har karshen rayuwarta, ko da ya sake ta ne a kan karan kansa to kuwa za ta ci gaba da zaman rainon Waheedah don ba za ta iya auren kowa in ba shi ba, Sarham is her life, her happiness, amma dole ta jingine shi yanzu, tunda ya ki zame mata namiji dan goyo.
Sannan maganganunsa na yau sun kara kashe jikinta daga tunanin rabuwa da shi haihata-haihata, amma dole ta janye masa.
Tayi zurfi a wannan tunanin lokaci mai tsaho, tana jin sanda ya gama girkinsa ya rufo kitchen din, gidan duk ya bade da kamshin farfesun kayan ciki da jallop din cous-cous da Sarham yayi, don su suka fi masa saukin hadawa. Ya dauka da kansa akan ‘tray’ ya jera duk abinda zasu bukata ya dauka zuwa dakin Hauwa.
Sai Madinah ta yi mishi ‘text messege wanda bata da tabbacin ya gani ko ya karanta, cewa gobe in Allah ya kaimu za ta yi reporting fara aiki da Dr. Siddiqah hospital.
A karshe ta ce masa “tana neman yardarsa”.

Yana dakin Hauwa sakon nata ya shigo wayarsa don haka bai duba da wuri ba.
Maijidda barcin bayan isha ba shi da kyau, tashi ga abinci na hada mana.
Jin muryarsa ya sa Hauwa tashi zaune daga kwanciyarta, yace ba kya ko cigiyar mijinki cikin gidannan. Hauwa ta ji kunya na mijinta da ya ce din don dai ita har yau ta kasa sabawa. Wai Likitan Innane miji agareta.
Ya ajiye abincin akan ‘center table’. Ya zauna daidai kafafunta, idanunsa na bin yatsunta da suka sha adon baki da jan lalle a hade da Mardiyyah ta yi mata da wani nisantaccen kallo na yabawa. Sai ya ji motsin shigowar sakon Madinah a wayarsa.
Fiddo wayar ya yi, ya karanta sakon nata. Girgiza kai ya yi, ya kuma mayar mata da gajeruwar amsar cewa,

Allah ya yi jagora.

Daga haka ya kishingide abinsa a gadon Hauwa, ya dora kansa bisa cinyoyinta, ita kuma tana zaune tsakiyar gadon ta mike sambala-sambalan kafafunta, ta bar masa cinyar yana shan raba, ya ce kasa-kasa kamar cikin rada.
Ba ni labarin rayuwar makarantarku BUK, da yadda ki ke coping a aji kullum, I know it will not be easy for you at all.
Sannan kuma dai an gayamin wai har da samari da Farfesoshin jamia ke bin layi gun Abba, duk da aure na? Ya fada (with a little bitterness) a muryarsa. Hauwa dai bata tanka ba sabida a lokacin hannunsa ya kai bisa lallausar tafin kafar ta, ya ja babban yatsanta da wani irin salo, mai bayyana manufa ingantacciya.
Kafin ya mirgina ya kai bakinsa tsakiyar tafin kafar tata ya sumbata. Tsigar jikin Hauwa ta tashi yarrr! Gabadaya, ta kasa ce masa komai, tana jin sanda Dr. Sarham ya janyo ta bakidaya jikinsa ya ce,
Maijiddah, zo ki samu lada kinji, wannan yunwar da ke ji tafi wadda nake ji ta abincin dana dafa mana.
Nan ma shiru ta yi, jikinta ya soma bari, don ba duka ta gama healing ba, kamshin jikinsa da niimar numfashinsa su suka agaza mata tsoron yake raguwa, lokacin da ya fara sarrafata son ransa, bakidaya ya hautsina Hauwa-Kulu. Yayi sama da bakinshi a hankali ya bata kyakkyawar sumba a kuncinta da lips dinta hannunsa sarke cikin yatsunta.
Daga nan yace. “wannan barin jiki haka? Ki yi hakuri zan yi a sannu, I promised I will not hurt you kamar jiya.
Hauwa ta rasa inda za ta saka kanta don kunya, gabadaya Sarham ya shige cikin jikinta, ga numfashinsu ya sarke wuri guda, wato ya zamanto numfashi guda suke shaka nasa kadai sabida kusancin da ya assassawa fuskokinsu, da lips dinsu daya sarke wuri guda yana caressing dinsu softly. Hannunsa ya kai ga zip din rigarta kuma ba tare da ta samu sukunin rikewa ko gardamawa ba, ya kai zip din kasa. Cewa yake cikin gigicewa.

Na kara janye kalamaina, na kara janye su daga gareki Maijidda, YOU ARE MY LOVE! My true love and eternal happiness. Not a sister!.

Hauwa ji ta yi hawayen farin ciki na sauko mata ta koina saboda yadda Dr. Sarham ya himmatu wajen fassara son nan a aikace, by caressing her tears da tsinin halshensa. Ya hanata kowanne irin katabus, nauikan sumbar yau daban suke, sumbace yake mata kala-kala naui-nauI data kassara dukkan gabbanta, ta kuma fahimtar da ita irin yadda Dr. Sarham yake da matukar son sumbatar matarsa har fiyeda ya tara da ita.
Wayyo Inna! Hauwa ta furta cikin son kasar ta tsage ta hadiye ta kawai ta huta da kunyar da Sarham yake jefa ta a yau.
Chapter 15 · 0% Book details