Sashe 20
Hauwa Kulu Part 4 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Ya kara kawata gidansa tun kafin Inna ta dawo ya zuba musu komai na bukatar rayuwa yadda suke rayuwarsu a gidan su na Ghana.
Ina rijiyar farin ciki take Hauwa ta fada da jin wannan labari da Sarham ya bata. Hauwa tafi kowa murnar dawowar iyayenta cikin Badala ba don komai ba sai don cewa har gobe ruhin HAUWA-KULU yana nan cikin gidajen Badala. Don haka walima sosai Sarham ya shiryawa su Inna don kowa dake Kofar Naisa ya san sun dawo, inda aka gayyato dukkan makwabtansu na kusa dana nesa. Baka jin komai a Badalar Kofar Naisa ranar walimar nan sai labarin Malam Bilyaminu, batansa da abinda Zakari yayi masa, da labarin Innar Hauwa da Hauwa data makance Allah yayi mata ludufin rayuwa tayi a aure a Saudiyyah da makanta da komai ta haifi yan biyu son kowa. Ai an ance ma gawurtaccen likitan ido take aure acan din.
Wai wacce Hauwar kuke nufi? Ba dai yarinyar nan mai ciwon ido na apolo Hauwar Inna ta lokonsu Malam Isa ba? Ita fa, wadda Salele yake yiwa jagora”.
Ai kuwa wqadanda aka gayyata dama wadanda baa gayyata ba a kofar Naisa duk sun taho walima da gulmar gani da ido gidan Malam Bilyaminu dan kofar Naisa. Mama da wasu daga cikin yan uwanta dana Abba da ke Shanono da Mardiyya sun samu halarta. Mardiyya da Salele sune masu rabon abinci da abin sha natake away ga mahalarta taron. An ci an sha anyi hanian an yi hotuna da vedio na tarihi yan biyu kowa ya gansu ya daukesu ya musu addua.
Sunje wa Mama zasuyi sati a wurinta nan Mama ta koma gyaran haihuwa, wanan karon wane gyaran amarci don Maman Farida guda ta yiwa waya tace tayiwa Hauwa gyaran haihuwa ko nawa ne zata biya.
yan biyu kuwa kusan tsakiyarMama da Abba Prof.suke kwana suna lelensu da shafesu da addua. Ana I gobe zasu koma Jiddah Abbah ya sa Sarham a gaba yace sai ya gaya masa ina zancen karatun Hauwa ya kwana, da yanzu ta gama year two dinta a wanda ta jingine. Sarham yace ya samar mata makarantar da suke Inclusive Education wato jamiar DAAR EL-HIKMAH UNIVERSITY da sun koma zata fara don haka wanna karon Sarham da kansa ya bukaci tafiya tareda Mardhiyyah don ta taimakawa Hauwa da rainon yan biyu da sauransu.
Dakin Sumayyah aka baiwa Mardiyyah take hidimar ta da yan biyun ta, tana taimakawa Hauwa su in zata shayar dasu ta rike mata daya. In kaga yadda Hauwa ke hidimar yayanta wajen saka musu diaper da yi musu tsarkin kashi da goge tumbidi da bada madarar jarirai abun zai matukar baka mamaki, haka duk kuka idan dayansu tayi ta san me take bukata. Sarham in yana gida tareda shi ake komai duka da yanata shirye-shiryen makarantar Hauwa a lokacin amma kuma tunda ya kyalla yaga ta fara sallah a wani dare abubuwa suka canza. Baiwar Allah tayi kokarin nuna masa cewa yan biyunta basu yi kwari ba Sarham yace Allah yasa jiya aka haife su, nima tun haihuwarsu banida kwari, Allah shine mai rayawa kuma shine mai kashewa kin ji ko? In kuma wannan yarinyar ce ta kara yi miki huduba sai in bar ki da ita in karo ta uku. Ya fada yana saita alamuran yadda yake son su Hauwa na kwallah har da tsane hawaye tana fushin da Sarham bai san tana yi ba a lokacin sabida ya tafi da yawa, bai nutsu ba sai da ya kwashe gyaran Mama tsaf a daren yau. Da aikin tukudin Inna. Ya bar Mardhiyya da yan biyu tana ta fama, duk sun rikice mata da kuka sun ki kama madarar da take basu a feeder.
Shiyasa ake cewa Uwa tafi tausayi yayan ta, sai da ya koma Sarhamun sa sannan ya koma lallashi. Yace Maijidda abun alfaharinki ne ace mijin ki cannot do without you. Ni kadai nasan manejin danayi har kwanakinnan arbain, kiyi hakuri ni bana gudun kaddarar yaya karewa ma son su nake yi, so nake ki cika min gida dasu son samu duk shekara ki juye min yan biyu. Bari in gaya miki abinda bai kamata in gaya miki ba nafi samun duk wani contentment da duk nutsuwar aure idan ina tare da ke. Soyayya daban, sexual satisfaction shima daban. Madinah ina mata soyayya ke ina miki so da kauna wanda yafi gaban ina ganin ki in iya kauda kwadayina sai dai in bakida lafiya to wannan kuwa zanjure har ki samu lafiya. Ni likita ne na san yadda zan kula da lafiyar yaya na kin ji ko?
Ta gyada kai cikin sanyin jiki, yana daura mata tawul a jikin ta yace karbo su ki basu nono kukan su ya dame ni.
Anan ne tayi magan cikin hararar sa.
wallahi bai dameka ba, da ya dameka da ka hakura sai sun yi shiru. Yace to sai me? Ba da hakan ba da an same su? Yanzunma kannen su nake hari shiyasa ban sauraresu ba ta zuba jallabiyya a jikin ta zata fita bata saurare shi ba yace dakata, tsofaffi sun ce sai kin yi wanka zaki taba su kada ki shafa masu datti, kodayake ni na san jiki na ba datti sai albarka ta dan dakata jimmm a bakin kofa, ai kuwa Innama ta gaya mata haka wai in taje dakin miji kada gta yarda ta taba su sai tayi tsarki, sai kawai ta juya ta nufi toilet. Ya ce ai kya tsaya in gama hada miki ruwan mai zafi sosai ance baki gama jegon ba har gobe. Tace don Allah don annabi kaje ka basu madara zan kula da kaina ka cika ni da magana ga kukan su yana ruda ni. Tausayi ta bashi sosai yace to ai nima ban yi wankan ba ko inzo muyi tare? Kin ga daga nan in cuda miki baya da dogon wuyanki. Hauwa takaicinsa ya isheta ta shige toilet dinta harda saka key. Sarham yayi jifa da filo ya mike yana saka jallabiyyarsa yana rero baitukan sa na ;
-Addua nake Allah ya taimakeki HAUWA-HAUWA!.
Daga cikin toilet Hauwa tana zuba ruwa mai zafi cikin gashin kanta, take jin sa tana sakin murmushi daga zuciya zuwa ruhi. Ta ce a hankali;
Nima Adduaa nake Allah ya ja da ran maigidana Lelen Abba a dade ana aikin lada.. shi da HAUWA!.
Ina rijiyar farin ciki take Hauwa ta fada da jin wannan labari da Sarham ya bata. Hauwa tafi kowa murnar dawowar iyayenta cikin Badala ba don komai ba sai don cewa har gobe ruhin HAUWA-KULU yana nan cikin gidajen Badala. Don haka walima sosai Sarham ya shiryawa su Inna don kowa dake Kofar Naisa ya san sun dawo, inda aka gayyato dukkan makwabtansu na kusa dana nesa. Baka jin komai a Badalar Kofar Naisa ranar walimar nan sai labarin Malam Bilyaminu, batansa da abinda Zakari yayi masa, da labarin Innar Hauwa da Hauwa data makance Allah yayi mata ludufin rayuwa tayi a aure a Saudiyyah da makanta da komai ta haifi yan biyu son kowa. Ai an ance ma gawurtaccen likitan ido take aure acan din.
Wai wacce Hauwar kuke nufi? Ba dai yarinyar nan mai ciwon ido na apolo Hauwar Inna ta lokonsu Malam Isa ba? Ita fa, wadda Salele yake yiwa jagora”.
Ai kuwa wqadanda aka gayyata dama wadanda baa gayyata ba a kofar Naisa duk sun taho walima da gulmar gani da ido gidan Malam Bilyaminu dan kofar Naisa. Mama da wasu daga cikin yan uwanta dana Abba da ke Shanono da Mardiyya sun samu halarta. Mardiyya da Salele sune masu rabon abinci da abin sha natake away ga mahalarta taron. An ci an sha anyi hanian an yi hotuna da vedio na tarihi yan biyu kowa ya gansu ya daukesu ya musu addua.
Sunje wa Mama zasuyi sati a wurinta nan Mama ta koma gyaran haihuwa, wanan karon wane gyaran amarci don Maman Farida guda ta yiwa waya tace tayiwa Hauwa gyaran haihuwa ko nawa ne zata biya.
yan biyu kuwa kusan tsakiyarMama da Abba Prof.suke kwana suna lelensu da shafesu da addua. Ana I gobe zasu koma Jiddah Abbah ya sa Sarham a gaba yace sai ya gaya masa ina zancen karatun Hauwa ya kwana, da yanzu ta gama year two dinta a wanda ta jingine. Sarham yace ya samar mata makarantar da suke Inclusive Education wato jamiar DAAR EL-HIKMAH UNIVERSITY da sun koma zata fara don haka wanna karon Sarham da kansa ya bukaci tafiya tareda Mardhiyyah don ta taimakawa Hauwa da rainon yan biyu da sauransu.
Dakin Sumayyah aka baiwa Mardiyyah take hidimar ta da yan biyun ta, tana taimakawa Hauwa su in zata shayar dasu ta rike mata daya. In kaga yadda Hauwa ke hidimar yayanta wajen saka musu diaper da yi musu tsarkin kashi da goge tumbidi da bada madarar jarirai abun zai matukar baka mamaki, haka duk kuka idan dayansu tayi ta san me take bukata. Sarham in yana gida tareda shi ake komai duka da yanata shirye-shiryen makarantar Hauwa a lokacin amma kuma tunda ya kyalla yaga ta fara sallah a wani dare abubuwa suka canza. Baiwar Allah tayi kokarin nuna masa cewa yan biyunta basu yi kwari ba Sarham yace Allah yasa jiya aka haife su, nima tun haihuwarsu banida kwari, Allah shine mai rayawa kuma shine mai kashewa kin ji ko? In kuma wannan yarinyar ce ta kara yi miki huduba sai in bar ki da ita in karo ta uku. Ya fada yana saita alamuran yadda yake son su Hauwa na kwallah har da tsane hawaye tana fushin da Sarham bai san tana yi ba a lokacin sabida ya tafi da yawa, bai nutsu ba sai da ya kwashe gyaran Mama tsaf a daren yau. Da aikin tukudin Inna. Ya bar Mardhiyya da yan biyu tana ta fama, duk sun rikice mata da kuka sun ki kama madarar da take basu a feeder.
Shiyasa ake cewa Uwa tafi tausayi yayan ta, sai da ya koma Sarhamun sa sannan ya koma lallashi. Yace Maijidda abun alfaharinki ne ace mijin ki cannot do without you. Ni kadai nasan manejin danayi har kwanakinnan arbain, kiyi hakuri ni bana gudun kaddarar yaya karewa ma son su nake yi, so nake ki cika min gida dasu son samu duk shekara ki juye min yan biyu. Bari in gaya miki abinda bai kamata in gaya miki ba nafi samun duk wani contentment da duk nutsuwar aure idan ina tare da ke. Soyayya daban, sexual satisfaction shima daban. Madinah ina mata soyayya ke ina miki so da kauna wanda yafi gaban ina ganin ki in iya kauda kwadayina sai dai in bakida lafiya to wannan kuwa zanjure har ki samu lafiya. Ni likita ne na san yadda zan kula da lafiyar yaya na kin ji ko?
Ta gyada kai cikin sanyin jiki, yana daura mata tawul a jikin ta yace karbo su ki basu nono kukan su ya dame ni.
Anan ne tayi magan cikin hararar sa.
wallahi bai dameka ba, da ya dameka da ka hakura sai sun yi shiru. Yace to sai me? Ba da hakan ba da an same su? Yanzunma kannen su nake hari shiyasa ban sauraresu ba ta zuba jallabiyya a jikin ta zata fita bata saurare shi ba yace dakata, tsofaffi sun ce sai kin yi wanka zaki taba su kada ki shafa masu datti, kodayake ni na san jiki na ba datti sai albarka ta dan dakata jimmm a bakin kofa, ai kuwa Innama ta gaya mata haka wai in taje dakin miji kada gta yarda ta taba su sai tayi tsarki, sai kawai ta juya ta nufi toilet. Ya ce ai kya tsaya in gama hada miki ruwan mai zafi sosai ance baki gama jegon ba har gobe. Tace don Allah don annabi kaje ka basu madara zan kula da kaina ka cika ni da magana ga kukan su yana ruda ni. Tausayi ta bashi sosai yace to ai nima ban yi wankan ba ko inzo muyi tare? Kin ga daga nan in cuda miki baya da dogon wuyanki. Hauwa takaicinsa ya isheta ta shige toilet dinta harda saka key. Sarham yayi jifa da filo ya mike yana saka jallabiyyarsa yana rero baitukan sa na ;
-Addua nake Allah ya taimakeki HAUWA-HAUWA!.
Daga cikin toilet Hauwa tana zuba ruwa mai zafi cikin gashin kanta, take jin sa tana sakin murmushi daga zuciya zuwa ruhi. Ta ce a hankali;
Nima Adduaa nake Allah ya ja da ran maigidana Lelen Abba a dade ana aikin lada.. shi da HAUWA!.