Sashe 18
Hauwa Kulu Part 4 Complete Hausa Novel · about 9 min read
Ya dawo gida yau da wuri than usual ya samu Sumayyah ta zo gidan, suna falo itada Hauwa. Lokacin an kai kudin auren su itada Usman Kano. Duk basu ji shigowarsa ba daga ita har Sumayyah sun baiwa kofa kofa baya. Sumayya na mata famfo irin na yaran likitoci.
Wallahi Aunty Hauwa kin bari kinyi saurin samun ciki, maimakon ki bari sai nan da yan shekaru biyu haka kina sa shi kuna yan dabaru da bazasu cutar da lafiyarki ba, not necessarily family planning na asibiti ai kin gane, amma kawai kika bari kika dau ciki as early as six month da zuwanki ko amarcin baku ci yadda ya kamata ba. Ga zancen aikin idon ki ya shantakar dashi tunda ya lura kinada ciki, kuma ke kullum yazo shikenan sai ki amsa kira ba dan jan ajin nan namu na mata koyaushe yake so zai samu, ai ni wallahi sai mun shekara uku nida Usman kafin mu fara tunanin tara yara, kuma sau biyu ko sau uku a sati zan ke yarda, ba kya ko tunanin yaya ake haihuwa, bafa sauki ne da ita ba, ke kinga yadda mata ke gumurzu a dakin haihuwar? Alhalin in kin haife shi ke ba ganin dan zaki yi ba, maimakon ki bari sai bayan aikin idonki muga abinda Allah zai yi.
I am imagining yadda zaki raini yaro a hannunki without seeing him, it will not be easy for you a halin yanzu, ga Bhaiya ba hakuri kullum yana like dake ko zama a office baya yi sosai yanzu, baya barinki ki huta ko kadan ki maida jikinki, bayan ana son gap don a maida ruwan jiki, shiyasa sanda Madinah ta tafi bai damu da tafiyar ta ba, ya san yana hutawa sosai, har fiyeda in tana gidan. Na tabbata ita ba haka take barinsa yana caskalar ta kullum ba, duk kin wani rame kamar ba luscious Hauwar Mama ba.
Yanzu da kin haihu baby yana tsotseki, shima ba hakura zai yi ba, duk su taru su tsofar dake (at twetieth) dinki. Maganar karatunki ma naga alama ta bi ruwa, Mama tayi tayi ya dawo dake in bazai saki a makaranta ba har ta gaji ta zuba masa ido.
Sarham ya yi maza ya koma da baya ya bar gidan, yana lissafa irin yadda zai ci uban Sumayyah laada waje.
Asibiti ya koma ransa a mugun bace da Sumayyah. Ya kirata a waya lokacin tana dakinta ita kadai ta bar Hauwa cikin zurfin tunanin, kome Summy ta fada haka ne Sarham baya tausayinta ta wannan fannin kuma ta tabbata ba haka yakewa Madina wannan rashin tausayin ba, kullum ba hutu kamar ya samu engine har gashi mutane sun soma noticing tana ramewa. Dole ta sake lale itama ta koyi jan aji kamar yadda Sumayya tace.
Sumayyah na dagawa da sallama yace Summy! Tace naam Bhaiyana
Ba wani nan. I am no more your Bhaiya daga yau. Fito ki bar min gidana kada ki lalata min tarbiyyar matata.
Na rantse da Allah in sha Allah wata mai kamawa zaa tattaraki ki tafi naki gidan mijin, shi ki je ki ja masa ajin ki gane in zai yi tolerating iskancin ki, kada in kara ganin kafarki a gidana sai kin haihu kinsan ciwon haihuwa da darajar mijin aure.
Sumayyah ta bude ido da baki a tare, nan ta gane ya ji gulmarta. Ta soma afi tana hurwar kayimin rai na tuba Bhaiya, kayimin aikin gafara Bhaiya, subutar baki ne, I dont really mean it. Yace subutar baki ko raayin banza na mata yan duniya kike son cusa mata, naki nayi mata aikin idon, da can ke kika sani? Ko kuwa mace na fama da kanta sai in kwantar da ita in fede mata ido wani abu ya samu Baby na? Wallahi Sumayyah kilbibinki ya isheni dama nasan kina kaita Saloon a cikin estate kuma na gaya miki tun na farko bana so, tunda ina sayo mata shampoo na wanke kai dana zaba mata, wanda bazai canza mata launin gashin kanta daga asalin na hausawa ba.
Sannan ina sane da cewa kin kawo mata wasu mayuka da sabulai na banza da hofinki, wai irin wadanda kike shafawa, kina so ki koya mata bleaching ne? Na taba ce miki kina da kyau ko shafe-shafen yammata yana burgeni? Itada ko ido babu!
I am observing you Summy, ke shaidaniya ce wasa-wasa, duk abinda kike yi wai ke a dole sai kin mayar min da mata yar duniya ko, na ce bansan kalarta bane sanda na aureta?
Ko bansan yadda gashinta yake ba? Ko nace miki in farin fata nake so na Madinah bai ishe ni ba? Ke dai wallahi Usman ya shiga uku, Maijiddah ki bar min kayata yadda nake sonta, muna zaman mu lafiya cikin fahimtar juna da kula da bukatun juna zaki hargitsa mu ko, kema kuma zuwanki kasar nan ne duk kika fara wadannan duniyancin. A da ba haka kike ba wallahi Sumayyah.
I love my wife and her natural beauty, dont dare try to change her for me.
Haka ya cashewa Sumayyah son ransa, har saida ta fidda kwallah. Cewa take In sha Allahu Bhaiya bazan sake ba. na tuba nabi Allah na bi ka.
Kafin in dawo ki tabbbatar kin bar min gida na, tunda ba nida ke muka hada kudi muka auri Hauwa ba.
Jikin Sumayyah na rawa ta shiga dakin Hauwa ta dau jakarta tace Anti Hauwa wannan mijin naki hummm! Sai Allah ya baki hakuri, kinsan Allah mijin ki aljani ne wajen jin magana, Mama tace haka yake da zuqo zance a kunnuwansa tun yana yaro, na tafi, sai an kwana biyu.
Bata kuma gaya mata yaji komai data fada ba. Ta bar Hauwa cikin sake-sake tayi tafiyarta tana cewa Summy kiyi min bayani mana? Daga can bakin kofa ta ce in yazo yayi miki fashin bakin da kansa kuma bazan kara baki shawarar komai ba, daga yau ba ruwana da sabgarku, mijin ki ya maida ke duk yadda yake son ganinki, ni dama nawa shawara.
Murmushi Hauwa tayi tana fadi cikin ranta Sumayyah da Bhaiyanta ba dama ne, ayi fada ayi dadi. Inama itama Zulkifl yana raye da haka zasu zama kamar Sumayyah da Bhaiya, yau fada gobe shiri. In suna shiri kuma sun fi kowa ji da juna.
Sarham bai dawo gidan ba sai dare, yana hanya ma Madina ta kira shi tace motarta ta baci yazo ya dauketa a asibiti sai ya biya ya dauketa sannan suka wuce gida, suka tsaya suka yi take away na pizza da KFC don yau girkin Hauwa ne bana Madina ba ko ya saya ne ko ya girka musu, don har bayan Madina ta dawo bata karbi yiwa Hauwa girkin abinci ba saidai in ta dafa yanzu tana zuba musu ranar nata girkin.
Suna shiga gida ya nufi dakin Hauwa, ta sha wankanta tana shafa mai ga hoda a gefe. Yayi salama ta amsa, ya bata peck a kumatu, ya shafa cikin ta wanda zuwa yanzu ya soma turowa cikin zani, yace hope hes kikcking well? cikin rashin fahimta tace waye? yace baby! Mai sunan Innata. Ta kare fuska da tafin hannunta ta ce aa gaskiya mai sunan Mama ce Yaya doctor. Nan suka hau gardama yace sai an fara saka Inna ita kuma tace sai an fara da Mama.
Daman jiranka nake ka dawo, in shafa hoda ka gayamin ko tayi daidai? Shiyasa tun dazu ban shafa ba yana fesa turare ya juyo ya ce ba na ce ki dinga shafa abarki ko yaya ba? in tayi yawa inna dawo na gani zan gyara miki? ta soma shafawa ya koma daga bayan ta ya dora kai a masangalin wuyanta fuskar shi da tata cikin mudubin hannun ta sun yi kyau har sun gaji, sun yi matching dukkan su choculate incomplexion da wani irin annuri da hasken imani a fuskokinsu. Daga nan Sarha ya kama hannun ta ya cirata tsaye ya soma kokarin kai mata sumba, nan da na ta noke ta ja baya, ya sake rikota yace lafiya? idonta narai narai tace wai mu bazamu dinga hutawa bane? Ina laifin sau biyu a sati ni gaskiya.. Nan da nan ya gane hudubar Sumayyah tayi aiki ta wanke mata kwakwalwa, yace ok. Ok to bari kiji in gaya miki daga yau Sumayyah na koreta kada ta kara zuwar min gida. Ya suri mukullin dakin shi ya bar dakin, yayi fushi sosai, kuma gashi girkinta ne bana Madinah ba don haka ya koma dakinsa ya kunna laptop ya hau aikin da bai yi a asibiti ba.
Hauwa duk taji guilt ya dameta data tuna tafiyar Summy ba shiri da abinda ta fada mata sai ta gane yaji hirar su ne. ai kuwa kunya tayi balain kama Hauwa da sauri ta saka doguwar rigar barci mai kyau ta bi bayan sa zuwa dakinsa don ta san hanyar dakin. Ta kwankwasa ya amsa da yes daga ciki sai ta shiga.
Ya kalleta ya dauke kai zuwa aikin sa, tace Baban Waheedah please kayi hakuri wallahi ba zan sake ba yayi shiru yana cigaba da operating system dinsa, ta taho kamar zata bi ta kansa yace in kika fasa min laptop sai kin biya ni ta muryarsa ta san inda yake zaune ta laluba ta zauna akan cinyarsa shikuma ya hau kokarin zillewa amma Hauwa bata bashi wannan damar ba.
Sosai ta inganta mishi daren yau kamar babu ciki a jikin ta, kamar babu lalurar ido a tare da ita, yau Sarham shi ya koma dan gata sai yadda Hauwa tayi da shi. Sun farantawa juna rai kamar bazasu ragewa gobe ba kafin su koma maida numfashi manne da juna. Saida ya koma Sarham din sa ya ce mata Maijidda, naji hudubar da kawar ki tayi miki, amma ki sani ni ba daya nake da sauran maza ba.
Ba wani canjin halitta ko tsofewa da zai sa in daina son matata.
Sannan barin ain samu abinda nake so a lokacinda nake so shi yake kara ninka wannan son yake kuma kara kusantoki da zuciyata.
Hauhuwa da wuri kuwa kuwa in duk sati ake yin ta ni kulllum nake so kiyi min.
Makaranta kuma ina sane na barki sai wata shekarar don bana son kiyi jigilar karatu da yaron ciki.
Maganar aikin ido kuma ban gama abinda nake tattarawa ba sannanba zan miki aiki alhalin kinada ciki ba sai Allah ya saukeki lafiya kinji?
The more you give me access to it, the more I addittionally love you.
Don haka ba Sumayyah kadai ba, duk wani wanda zai baki shawara akaina ko akan abinda zai amafni jikinki yabi bayan ni. Ban ce kada kiyi kawance da kowa ba amma ina so ya zama nine amininki sama da kowa, feel free to discuss everything about our marital life with me kin ji? Not the third party wadanda ba lallai bane su san meye sexual likes and likes dina ba.
Kunya sosai ta kama Hauwa, ta roki gafara, ta dauki alkawarin bazata sake yi masa rowar wannan ba, sannan bazata zancen mijin ta da kowa ba sai da shi kansa. Kuma daga wannan ranar ne, HAUWA BILYAMINU, ta fara kiransa da suna MY PACESETTER!!!.
Wallahi Aunty Hauwa kin bari kinyi saurin samun ciki, maimakon ki bari sai nan da yan shekaru biyu haka kina sa shi kuna yan dabaru da bazasu cutar da lafiyarki ba, not necessarily family planning na asibiti ai kin gane, amma kawai kika bari kika dau ciki as early as six month da zuwanki ko amarcin baku ci yadda ya kamata ba. Ga zancen aikin idon ki ya shantakar dashi tunda ya lura kinada ciki, kuma ke kullum yazo shikenan sai ki amsa kira ba dan jan ajin nan namu na mata koyaushe yake so zai samu, ai ni wallahi sai mun shekara uku nida Usman kafin mu fara tunanin tara yara, kuma sau biyu ko sau uku a sati zan ke yarda, ba kya ko tunanin yaya ake haihuwa, bafa sauki ne da ita ba, ke kinga yadda mata ke gumurzu a dakin haihuwar? Alhalin in kin haife shi ke ba ganin dan zaki yi ba, maimakon ki bari sai bayan aikin idonki muga abinda Allah zai yi.
I am imagining yadda zaki raini yaro a hannunki without seeing him, it will not be easy for you a halin yanzu, ga Bhaiya ba hakuri kullum yana like dake ko zama a office baya yi sosai yanzu, baya barinki ki huta ko kadan ki maida jikinki, bayan ana son gap don a maida ruwan jiki, shiyasa sanda Madinah ta tafi bai damu da tafiyar ta ba, ya san yana hutawa sosai, har fiyeda in tana gidan. Na tabbata ita ba haka take barinsa yana caskalar ta kullum ba, duk kin wani rame kamar ba luscious Hauwar Mama ba.
Yanzu da kin haihu baby yana tsotseki, shima ba hakura zai yi ba, duk su taru su tsofar dake (at twetieth) dinki. Maganar karatunki ma naga alama ta bi ruwa, Mama tayi tayi ya dawo dake in bazai saki a makaranta ba har ta gaji ta zuba masa ido.
Sarham ya yi maza ya koma da baya ya bar gidan, yana lissafa irin yadda zai ci uban Sumayyah laada waje.
Asibiti ya koma ransa a mugun bace da Sumayyah. Ya kirata a waya lokacin tana dakinta ita kadai ta bar Hauwa cikin zurfin tunanin, kome Summy ta fada haka ne Sarham baya tausayinta ta wannan fannin kuma ta tabbata ba haka yakewa Madina wannan rashin tausayin ba, kullum ba hutu kamar ya samu engine har gashi mutane sun soma noticing tana ramewa. Dole ta sake lale itama ta koyi jan aji kamar yadda Sumayya tace.
Sumayyah na dagawa da sallama yace Summy! Tace naam Bhaiyana
Ba wani nan. I am no more your Bhaiya daga yau. Fito ki bar min gidana kada ki lalata min tarbiyyar matata.
Na rantse da Allah in sha Allah wata mai kamawa zaa tattaraki ki tafi naki gidan mijin, shi ki je ki ja masa ajin ki gane in zai yi tolerating iskancin ki, kada in kara ganin kafarki a gidana sai kin haihu kinsan ciwon haihuwa da darajar mijin aure.
Sumayyah ta bude ido da baki a tare, nan ta gane ya ji gulmarta. Ta soma afi tana hurwar kayimin rai na tuba Bhaiya, kayimin aikin gafara Bhaiya, subutar baki ne, I dont really mean it. Yace subutar baki ko raayin banza na mata yan duniya kike son cusa mata, naki nayi mata aikin idon, da can ke kika sani? Ko kuwa mace na fama da kanta sai in kwantar da ita in fede mata ido wani abu ya samu Baby na? Wallahi Sumayyah kilbibinki ya isheni dama nasan kina kaita Saloon a cikin estate kuma na gaya miki tun na farko bana so, tunda ina sayo mata shampoo na wanke kai dana zaba mata, wanda bazai canza mata launin gashin kanta daga asalin na hausawa ba.
Sannan ina sane da cewa kin kawo mata wasu mayuka da sabulai na banza da hofinki, wai irin wadanda kike shafawa, kina so ki koya mata bleaching ne? Na taba ce miki kina da kyau ko shafe-shafen yammata yana burgeni? Itada ko ido babu!
I am observing you Summy, ke shaidaniya ce wasa-wasa, duk abinda kike yi wai ke a dole sai kin mayar min da mata yar duniya ko, na ce bansan kalarta bane sanda na aureta?
Ko bansan yadda gashinta yake ba? Ko nace miki in farin fata nake so na Madinah bai ishe ni ba? Ke dai wallahi Usman ya shiga uku, Maijiddah ki bar min kayata yadda nake sonta, muna zaman mu lafiya cikin fahimtar juna da kula da bukatun juna zaki hargitsa mu ko, kema kuma zuwanki kasar nan ne duk kika fara wadannan duniyancin. A da ba haka kike ba wallahi Sumayyah.
I love my wife and her natural beauty, dont dare try to change her for me.
Haka ya cashewa Sumayyah son ransa, har saida ta fidda kwallah. Cewa take In sha Allahu Bhaiya bazan sake ba. na tuba nabi Allah na bi ka.
Kafin in dawo ki tabbbatar kin bar min gida na, tunda ba nida ke muka hada kudi muka auri Hauwa ba.
Jikin Sumayyah na rawa ta shiga dakin Hauwa ta dau jakarta tace Anti Hauwa wannan mijin naki hummm! Sai Allah ya baki hakuri, kinsan Allah mijin ki aljani ne wajen jin magana, Mama tace haka yake da zuqo zance a kunnuwansa tun yana yaro, na tafi, sai an kwana biyu.
Bata kuma gaya mata yaji komai data fada ba. Ta bar Hauwa cikin sake-sake tayi tafiyarta tana cewa Summy kiyi min bayani mana? Daga can bakin kofa ta ce in yazo yayi miki fashin bakin da kansa kuma bazan kara baki shawarar komai ba, daga yau ba ruwana da sabgarku, mijin ki ya maida ke duk yadda yake son ganinki, ni dama nawa shawara.
Murmushi Hauwa tayi tana fadi cikin ranta Sumayyah da Bhaiyanta ba dama ne, ayi fada ayi dadi. Inama itama Zulkifl yana raye da haka zasu zama kamar Sumayyah da Bhaiya, yau fada gobe shiri. In suna shiri kuma sun fi kowa ji da juna.
Sarham bai dawo gidan ba sai dare, yana hanya ma Madina ta kira shi tace motarta ta baci yazo ya dauketa a asibiti sai ya biya ya dauketa sannan suka wuce gida, suka tsaya suka yi take away na pizza da KFC don yau girkin Hauwa ne bana Madina ba ko ya saya ne ko ya girka musu, don har bayan Madina ta dawo bata karbi yiwa Hauwa girkin abinci ba saidai in ta dafa yanzu tana zuba musu ranar nata girkin.
Suna shiga gida ya nufi dakin Hauwa, ta sha wankanta tana shafa mai ga hoda a gefe. Yayi salama ta amsa, ya bata peck a kumatu, ya shafa cikin ta wanda zuwa yanzu ya soma turowa cikin zani, yace hope hes kikcking well? cikin rashin fahimta tace waye? yace baby! Mai sunan Innata. Ta kare fuska da tafin hannunta ta ce aa gaskiya mai sunan Mama ce Yaya doctor. Nan suka hau gardama yace sai an fara saka Inna ita kuma tace sai an fara da Mama.
Daman jiranka nake ka dawo, in shafa hoda ka gayamin ko tayi daidai? Shiyasa tun dazu ban shafa ba yana fesa turare ya juyo ya ce ba na ce ki dinga shafa abarki ko yaya ba? in tayi yawa inna dawo na gani zan gyara miki? ta soma shafawa ya koma daga bayan ta ya dora kai a masangalin wuyanta fuskar shi da tata cikin mudubin hannun ta sun yi kyau har sun gaji, sun yi matching dukkan su choculate incomplexion da wani irin annuri da hasken imani a fuskokinsu. Daga nan Sarha ya kama hannun ta ya cirata tsaye ya soma kokarin kai mata sumba, nan da na ta noke ta ja baya, ya sake rikota yace lafiya? idonta narai narai tace wai mu bazamu dinga hutawa bane? Ina laifin sau biyu a sati ni gaskiya.. Nan da nan ya gane hudubar Sumayyah tayi aiki ta wanke mata kwakwalwa, yace ok. Ok to bari kiji in gaya miki daga yau Sumayyah na koreta kada ta kara zuwar min gida. Ya suri mukullin dakin shi ya bar dakin, yayi fushi sosai, kuma gashi girkinta ne bana Madinah ba don haka ya koma dakinsa ya kunna laptop ya hau aikin da bai yi a asibiti ba.
Hauwa duk taji guilt ya dameta data tuna tafiyar Summy ba shiri da abinda ta fada mata sai ta gane yaji hirar su ne. ai kuwa kunya tayi balain kama Hauwa da sauri ta saka doguwar rigar barci mai kyau ta bi bayan sa zuwa dakinsa don ta san hanyar dakin. Ta kwankwasa ya amsa da yes daga ciki sai ta shiga.
Ya kalleta ya dauke kai zuwa aikin sa, tace Baban Waheedah please kayi hakuri wallahi ba zan sake ba yayi shiru yana cigaba da operating system dinsa, ta taho kamar zata bi ta kansa yace in kika fasa min laptop sai kin biya ni ta muryarsa ta san inda yake zaune ta laluba ta zauna akan cinyarsa shikuma ya hau kokarin zillewa amma Hauwa bata bashi wannan damar ba.
Sosai ta inganta mishi daren yau kamar babu ciki a jikin ta, kamar babu lalurar ido a tare da ita, yau Sarham shi ya koma dan gata sai yadda Hauwa tayi da shi. Sun farantawa juna rai kamar bazasu ragewa gobe ba kafin su koma maida numfashi manne da juna. Saida ya koma Sarham din sa ya ce mata Maijidda, naji hudubar da kawar ki tayi miki, amma ki sani ni ba daya nake da sauran maza ba.
Ba wani canjin halitta ko tsofewa da zai sa in daina son matata.
Sannan barin ain samu abinda nake so a lokacinda nake so shi yake kara ninka wannan son yake kuma kara kusantoki da zuciyata.
Hauhuwa da wuri kuwa kuwa in duk sati ake yin ta ni kulllum nake so kiyi min.
Makaranta kuma ina sane na barki sai wata shekarar don bana son kiyi jigilar karatu da yaron ciki.
Maganar aikin ido kuma ban gama abinda nake tattarawa ba sannanba zan miki aiki alhalin kinada ciki ba sai Allah ya saukeki lafiya kinji?
The more you give me access to it, the more I addittionally love you.
Don haka ba Sumayyah kadai ba, duk wani wanda zai baki shawara akaina ko akan abinda zai amafni jikinki yabi bayan ni. Ban ce kada kiyi kawance da kowa ba amma ina so ya zama nine amininki sama da kowa, feel free to discuss everything about our marital life with me kin ji? Not the third party wadanda ba lallai bane su san meye sexual likes and likes dina ba.
Kunya sosai ta kama Hauwa, ta roki gafara, ta dauki alkawarin bazata sake yi masa rowar wannan ba, sannan bazata zancen mijin ta da kowa ba sai da shi kansa. Kuma daga wannan ranar ne, HAUWA BILYAMINU, ta fara kiransa da suna MY PACESETTER!!!.