Sashe 13
Hauwa Kulu Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya kama hannunta zuwa dakinta duk a kan idon Madinah. Wani zazzafan hawaye ya feso wa Madinah. Suka shige ya rufo kofar harda key. A can baya idan wani ya gaya mata cewa Sarham zai iya kama hannun wata mace a duniya bayan ita, za ta karya ta ne da babbar murya. Yau dai ga shi tana ganin halin maza, ganin idanunta. Shin me ta yiswa Sarham data cancanci haka? Tabbas duk wadda ta ce namiji uba ne ko abin yarda da baiwa amana akan SOYAYYAH ita Madinah za ta kwana tana gaya mata itace marainiyar da ta fi kowa maraici.
Sanin cewa hankalin Madina yana kansu sai bai jima sosai a dakin Hauwa ba ya fito ya jawo mata kofar ya ce ina zuwa.
Ya tadda Madina a kitchen ta hada custard da madara a kofi mug ta dauka za ta wuce daki, sai ya dakata a bakin kofar kitchen din, wato ya tare mata hanyar ficewa.
Ya ce da ita (authoritatively), Munauwarah, abincin da ki ka kwashe daga dining wa zai ci? Ina ki ka kai shi, ko zubarwa ki ka yi?
Madinah ta yi banza da shi.
Ya ce, Ina soki sani ni ba mai kudi ba ne da zan zubar da abinci a shara wai don kada wani ya ci, sannan bana son almubazzaranci, kin dafa abinci amma sai fita na yi na sa kudi na saya, mene ne hujjarki ta yin hakan?
A da dai ban sanki da wadannan baudaddun halayen ba, ko kusa wannan ba Munawwarar da na sani ba ce ba Giwar Sarham..bace.
Kamar jira ta ke ya fadi hakan, hawayen da ta ke ta tattali tun dazu da ta fito ta ganshi yana kula da makauniyar matarsa, suka samu yancin kansu yanzu.
Ta ce, Kada ka kara ce min wata giwarka daga yau. Ita giwar miji ita ce matar da ta ishe shi ta kowanne bangare, ta kuma ke satisfying dukkan bukatunsa, har ta hana shi hango kyalkyalin wasu matan.
Wato wadda ta dusar da hasken sauran mata a idanunsa, amma ni fa?
Nawa mijin ban ishe shi ba, karewar ban ishe shi ba musaka ya dauko min ya zama bawanta, ya daidaita matsayina da nata.
Na tsane ka Sarham. Wallahi na tsane ka, ka tafi daga idona kada in yi furucin da Allah zai yi fushi da ni, wato in ce ka sake ni in koma gidanmu ya fi min alkhairi a kan ganin fuskarka yanzu.
Murmushi ya yi ciki-ciki, ya dauki kofin glass ya zuba ruwan gora ya sha ya juya ya bar mata kitchen din. Wannan shirun da ya yi mata ya fi komai kara fusatata.
Tun yana tsammanin abin na Madina mai karewa ne amma har zuwa wayewar garin ranar da shi ya tashi cikin farin ciki mara misaltuwa, na karbar ragamar rayuwar HAUWA-KULU. Hauwa kuma aka bi sahun sauran mata ya soma jinyar barnar da yayi a matsayin sa na likita bai wahalar da ita fiyeda kima ba, bai kara ganin kyallin Madinah ba.
Ta kulle kanta da yarta a dakinta, ta daina fitowa kwata-kwata, shi kuma tunanin cewa yau din girkin Hauwa ne a bisa tsari na musulunci daga nan har kwanaki bakwai masu zuwa ya sa bai kara shiga dakin Madinah ba har washegari duk da ya san ta kulle kanta amma yayi niyyar duba lafiyarsu.
Da safe yana so ya tafi asibiti, amma yana tunanin yadda Hauwa za ta yi coping cikin gidan, sababbin halayen da Madinah ta tsuro da su na yin biris da alamarinsa balle yayi tunanin za ta taimaki Hauwa ya daga masa hankali, da ma ya yi niyyar fita tare da ita yau ya kai ta top ten ta yi sayayyar abubuwan da ta ke da bukata, duk da yasan Mama ba abinda ba ta hado ta da shi na amfanin ta ba.
Gyaran muryarsa a kofar dakinta ya sa Hauwa da ke idar da sallar walha juyowa da hanzari don dama a kage ta ke da ganin nasa, tunda ya tafi dakinsa don ya shiryo take jin yunwa.
Ya karaso har inda take ya dagata daga kan dardumar suka karasa gefen gadon, ya zaunar da ita bisa cinyoyinsa yana wani irin sunsuna ta, yace cikin taushin murya,
Maijidda ya ki ka tashi, ya kwanan bakunta? Hope babu pain din sosai yanzu?
Dan murmushi ta yi. Tana sunne kanta a kirjinsa.
Ya ce, naga kamar ba ki yi sallah daidai ba, nan din ba nan ne gabas ba, let me adjust.
Ya gyara mata inda za ta fuskanta a dakin yayin sallah, ya zauna nan makale da ita ya kasa tafiya asibiti, ya ce, Ba ni labarin yadda ki ka kwana a gidanki? How do you feel the night? I know its hurting a little, amma da kinsan rahma da gafarar dana roka miki daren jiya bakidayansa da kin san cewa kin rabauta da albarkar aure.
Aljannarki in dai har tana kasan dugadugaina, ni Sarham na daga miki ki shiga cikin amincewa ta udkhuluha bissalam.
Hauwa dai murmushi take tayi ba ta amsa ba.
To zan tafi asibiti, ko za ki bi ni mu je in fara kai ki ki sayi abin da ki ke so kafin na wuce?
A nan ne ta yi magana, ta ce,
Ba ni da bukatar komai, Mama ta hado ni da komai na bukatata, ka je lafiya ka dawo lafiya Yaya Doctorau! Baban Waheedah.
Yana jiyo bude kofar Madinah ta fito cikin shiri dauke da Waheedah, sai ya ajiye Hauwa a gefensa ya tashi ya fita, yana cewa cikin ransa, zai yi maganin Madinah.
Yana fitowa daga dakin hauwa suka hada ido shida ita, Madinah ta hadiye wani bakin ciki da ya taso mata, ta juyar da kai gefe tace.
Zan fita neman aiki.
Har ya kai bakin kofar nasa dakin sai ya dakata, kafin ya juyo ya yi mata wani irin kallo na gargadi. Madinah ta kauda kai ta ce,
Ah toh, dole in fara aiki yanzu, don ba zan zauna jire maka musakar da ka ajiye a gida ba, ko in zama yar jagora.
Allah ya tsare ni aikin wahalar da babu lada wai aikin kishiya.
Wallahi da ma don kai da yarka ne bana aiki, don in samu lokacin kula da gidana da iyalina, a yanzu na gane ba abin da mace za ta yi ta mallaki namiji da sunan kyautatawa da kiyaye hakkokinsa don hana shi hango wata, sai dai kawai ta bata wa kanta lokaci.
Ya gyada kai yana kallonta da budadden ido, Shi ya sa yanzu ki ka zabi fita gantali, tunda ba ki mallake ni din ba kuma don na yi aure cika sunnar Manzo SAW? Don dai na san ba za ki ce neman na kai ne ya saka ki yin aikin ba.
Ai kamar ba ka ji ba Dr. Sarham, in zauna yi maka gadin mata ne ba zan yi ba, sabida ni dai duk danginmu babu makaho, ban iya yar jagorar zuwa bandaki da kitchen ba.
Sarham ya shige dakinsa da sauri gudun kada ya yi loosing temper ya kai mata mari again irin jiya, yana cewa,
I can relate. Lalura dai ba ta wuce kan kowa ba. Kuma Hauwa ba ta dora wa kanta ba, ni din dai ni na jawo mata.
Haka ko da ya je office din kasa zama yayi ya jima yadda ya saba saboda tunanin halin da Hauwa ke ciki. Don haka karfe biyun rana na bugawa wato lokacin cin lunch dinsa ya baro Saudi-German zuwa Estate dinsu.
Yana hanya Sumayya ta kira shi, yana ganin kiran nata ya ki dagawa, ya shiga gida kenan ya yi parking. Sumayya ta sake kira, tsaki ya yi ya daga kiran nata, bai ce komai ba, Sumayya sai ta sa kuka.
Da kyar ta soma magana jin Yayan bai katse ta ba, bai kuma tambayi dalilin kukan nata ba, saida ta gaji don kanta tace.
Ni dama na san Aunty Madinah ce ajalin zumuncinmu, Bhaiya, na san dama sai ta raba mu, tunda har yau ka ki daga kirana da gangan, kuma ka ce kada in kara zuwa gidanka har abada.
Sarham takaici goma da ashirin ya ishe shi.
Sumayya, wace irin yarinya ce ne ke fitinanniya mai kishi da matar Yayanta?
Sumayya ta zaro ido, kamar Sarham yana kallonta, ya ce, Yes, na gaji da korafinki a kan Madinah, na gaji da gaya miki ba ta isa ta sa ni ba, ba ta isa ta hana zumuncina da kowa nawa ba.
Kada ki koma daukan alhakinta, na yi karin auren ma don dai ku yarda Madinah ba ta fi karfina ba bata mallakeni irin yadda kuke zato ba shima ban tsira ba.
To yau na dauko Hauwa na hada da Madinah, za ku daina yi min kallon sakarai a son matarsa ko?
Ba tun yau ba na gane ke irin kannen mijin nan ne fitinannu marasa adalci, yadda ki ka dauki Madinah ita ko kusa ba haka ta dauke ki ba.
Ki bi rayuwa a sannu Sumayyah, ki daina saka wa kowanne dan Adam kahon zuka, babu mai bai wa wani numfashi ke da ita, kuma ba ki san ranar da Madinah za ta iya yi miki a rayuwa ba.
Ina yi miki nasihar nan ne a matsayina na dan uwanki ba a matsayin mijin Madina ba.
Change your behaviour Sumayyah da duk kannen miji masu irin halinki, don kuma mata ne, gidan aure za ku je, kada kaddara ta kai ku gidan masu irin halinku abubuwa su cabalbale muku. Ki sa a ranki the more ki ka bar matar Yayanki ta zauna lafiya da shi, the more kema za ki samu zaman lafiya da naki yan uwan mijin, tarihi maimaita kansa yake Sumayyah.
Sumayyah na kuka ta ce, Na daina, wallahi Bhaiya na daina kinta babu dalili, ni na ga ishara Bhaiya don yanzu ga shi tana ramawa, farin cikina duka yana hannunta tunda ta yi rantsuwa ko ni na saura ya mace a duniya Usman ba zai aure ni ba.
Bhaiya mu kuma, nida Usman, muna matukar son juna.
Sanin cewa hankalin Madina yana kansu sai bai jima sosai a dakin Hauwa ba ya fito ya jawo mata kofar ya ce ina zuwa.
Ya tadda Madina a kitchen ta hada custard da madara a kofi mug ta dauka za ta wuce daki, sai ya dakata a bakin kofar kitchen din, wato ya tare mata hanyar ficewa.
Ya ce da ita (authoritatively), Munauwarah, abincin da ki ka kwashe daga dining wa zai ci? Ina ki ka kai shi, ko zubarwa ki ka yi?
Madinah ta yi banza da shi.
Ya ce, Ina soki sani ni ba mai kudi ba ne da zan zubar da abinci a shara wai don kada wani ya ci, sannan bana son almubazzaranci, kin dafa abinci amma sai fita na yi na sa kudi na saya, mene ne hujjarki ta yin hakan?
A da dai ban sanki da wadannan baudaddun halayen ba, ko kusa wannan ba Munawwarar da na sani ba ce ba Giwar Sarham..bace.
Kamar jira ta ke ya fadi hakan, hawayen da ta ke ta tattali tun dazu da ta fito ta ganshi yana kula da makauniyar matarsa, suka samu yancin kansu yanzu.
Ta ce, Kada ka kara ce min wata giwarka daga yau. Ita giwar miji ita ce matar da ta ishe shi ta kowanne bangare, ta kuma ke satisfying dukkan bukatunsa, har ta hana shi hango kyalkyalin wasu matan.
Wato wadda ta dusar da hasken sauran mata a idanunsa, amma ni fa?
Nawa mijin ban ishe shi ba, karewar ban ishe shi ba musaka ya dauko min ya zama bawanta, ya daidaita matsayina da nata.
Na tsane ka Sarham. Wallahi na tsane ka, ka tafi daga idona kada in yi furucin da Allah zai yi fushi da ni, wato in ce ka sake ni in koma gidanmu ya fi min alkhairi a kan ganin fuskarka yanzu.
Murmushi ya yi ciki-ciki, ya dauki kofin glass ya zuba ruwan gora ya sha ya juya ya bar mata kitchen din. Wannan shirun da ya yi mata ya fi komai kara fusatata.
Tun yana tsammanin abin na Madina mai karewa ne amma har zuwa wayewar garin ranar da shi ya tashi cikin farin ciki mara misaltuwa, na karbar ragamar rayuwar HAUWA-KULU. Hauwa kuma aka bi sahun sauran mata ya soma jinyar barnar da yayi a matsayin sa na likita bai wahalar da ita fiyeda kima ba, bai kara ganin kyallin Madinah ba.
Ta kulle kanta da yarta a dakinta, ta daina fitowa kwata-kwata, shi kuma tunanin cewa yau din girkin Hauwa ne a bisa tsari na musulunci daga nan har kwanaki bakwai masu zuwa ya sa bai kara shiga dakin Madinah ba har washegari duk da ya san ta kulle kanta amma yayi niyyar duba lafiyarsu.
Da safe yana so ya tafi asibiti, amma yana tunanin yadda Hauwa za ta yi coping cikin gidan, sababbin halayen da Madinah ta tsuro da su na yin biris da alamarinsa balle yayi tunanin za ta taimaki Hauwa ya daga masa hankali, da ma ya yi niyyar fita tare da ita yau ya kai ta top ten ta yi sayayyar abubuwan da ta ke da bukata, duk da yasan Mama ba abinda ba ta hado ta da shi na amfanin ta ba.
Gyaran muryarsa a kofar dakinta ya sa Hauwa da ke idar da sallar walha juyowa da hanzari don dama a kage ta ke da ganin nasa, tunda ya tafi dakinsa don ya shiryo take jin yunwa.
Ya karaso har inda take ya dagata daga kan dardumar suka karasa gefen gadon, ya zaunar da ita bisa cinyoyinsa yana wani irin sunsuna ta, yace cikin taushin murya,
Maijidda ya ki ka tashi, ya kwanan bakunta? Hope babu pain din sosai yanzu?
Dan murmushi ta yi. Tana sunne kanta a kirjinsa.
Ya ce, naga kamar ba ki yi sallah daidai ba, nan din ba nan ne gabas ba, let me adjust.
Ya gyara mata inda za ta fuskanta a dakin yayin sallah, ya zauna nan makale da ita ya kasa tafiya asibiti, ya ce, Ba ni labarin yadda ki ka kwana a gidanki? How do you feel the night? I know its hurting a little, amma da kinsan rahma da gafarar dana roka miki daren jiya bakidayansa da kin san cewa kin rabauta da albarkar aure.
Aljannarki in dai har tana kasan dugadugaina, ni Sarham na daga miki ki shiga cikin amincewa ta udkhuluha bissalam.
Hauwa dai murmushi take tayi ba ta amsa ba.
To zan tafi asibiti, ko za ki bi ni mu je in fara kai ki ki sayi abin da ki ke so kafin na wuce?
A nan ne ta yi magana, ta ce,
Ba ni da bukatar komai, Mama ta hado ni da komai na bukatata, ka je lafiya ka dawo lafiya Yaya Doctorau! Baban Waheedah.
Yana jiyo bude kofar Madinah ta fito cikin shiri dauke da Waheedah, sai ya ajiye Hauwa a gefensa ya tashi ya fita, yana cewa cikin ransa, zai yi maganin Madinah.
Yana fitowa daga dakin hauwa suka hada ido shida ita, Madinah ta hadiye wani bakin ciki da ya taso mata, ta juyar da kai gefe tace.
Zan fita neman aiki.
Har ya kai bakin kofar nasa dakin sai ya dakata, kafin ya juyo ya yi mata wani irin kallo na gargadi. Madinah ta kauda kai ta ce,
Ah toh, dole in fara aiki yanzu, don ba zan zauna jire maka musakar da ka ajiye a gida ba, ko in zama yar jagora.
Allah ya tsare ni aikin wahalar da babu lada wai aikin kishiya.
Wallahi da ma don kai da yarka ne bana aiki, don in samu lokacin kula da gidana da iyalina, a yanzu na gane ba abin da mace za ta yi ta mallaki namiji da sunan kyautatawa da kiyaye hakkokinsa don hana shi hango wata, sai dai kawai ta bata wa kanta lokaci.
Ya gyada kai yana kallonta da budadden ido, Shi ya sa yanzu ki ka zabi fita gantali, tunda ba ki mallake ni din ba kuma don na yi aure cika sunnar Manzo SAW? Don dai na san ba za ki ce neman na kai ne ya saka ki yin aikin ba.
Ai kamar ba ka ji ba Dr. Sarham, in zauna yi maka gadin mata ne ba zan yi ba, sabida ni dai duk danginmu babu makaho, ban iya yar jagorar zuwa bandaki da kitchen ba.
Sarham ya shige dakinsa da sauri gudun kada ya yi loosing temper ya kai mata mari again irin jiya, yana cewa,
I can relate. Lalura dai ba ta wuce kan kowa ba. Kuma Hauwa ba ta dora wa kanta ba, ni din dai ni na jawo mata.
Haka ko da ya je office din kasa zama yayi ya jima yadda ya saba saboda tunanin halin da Hauwa ke ciki. Don haka karfe biyun rana na bugawa wato lokacin cin lunch dinsa ya baro Saudi-German zuwa Estate dinsu.
Yana hanya Sumayya ta kira shi, yana ganin kiran nata ya ki dagawa, ya shiga gida kenan ya yi parking. Sumayya ta sake kira, tsaki ya yi ya daga kiran nata, bai ce komai ba, Sumayya sai ta sa kuka.
Da kyar ta soma magana jin Yayan bai katse ta ba, bai kuma tambayi dalilin kukan nata ba, saida ta gaji don kanta tace.
Ni dama na san Aunty Madinah ce ajalin zumuncinmu, Bhaiya, na san dama sai ta raba mu, tunda har yau ka ki daga kirana da gangan, kuma ka ce kada in kara zuwa gidanka har abada.
Sarham takaici goma da ashirin ya ishe shi.
Sumayya, wace irin yarinya ce ne ke fitinanniya mai kishi da matar Yayanta?
Sumayya ta zaro ido, kamar Sarham yana kallonta, ya ce, Yes, na gaji da korafinki a kan Madinah, na gaji da gaya miki ba ta isa ta sa ni ba, ba ta isa ta hana zumuncina da kowa nawa ba.
Kada ki koma daukan alhakinta, na yi karin auren ma don dai ku yarda Madinah ba ta fi karfina ba bata mallakeni irin yadda kuke zato ba shima ban tsira ba.
To yau na dauko Hauwa na hada da Madinah, za ku daina yi min kallon sakarai a son matarsa ko?
Ba tun yau ba na gane ke irin kannen mijin nan ne fitinannu marasa adalci, yadda ki ka dauki Madinah ita ko kusa ba haka ta dauke ki ba.
Ki bi rayuwa a sannu Sumayyah, ki daina saka wa kowanne dan Adam kahon zuka, babu mai bai wa wani numfashi ke da ita, kuma ba ki san ranar da Madinah za ta iya yi miki a rayuwa ba.
Ina yi miki nasihar nan ne a matsayina na dan uwanki ba a matsayin mijin Madina ba.
Change your behaviour Sumayyah da duk kannen miji masu irin halinki, don kuma mata ne, gidan aure za ku je, kada kaddara ta kai ku gidan masu irin halinku abubuwa su cabalbale muku. Ki sa a ranki the more ki ka bar matar Yayanki ta zauna lafiya da shi, the more kema za ki samu zaman lafiya da naki yan uwan mijin, tarihi maimaita kansa yake Sumayyah.
Sumayyah na kuka ta ce, Na daina, wallahi Bhaiya na daina kinta babu dalili, ni na ga ishara Bhaiya don yanzu ga shi tana ramawa, farin cikina duka yana hannunta tunda ta yi rantsuwa ko ni na saura ya mace a duniya Usman ba zai aure ni ba.
Bhaiya mu kuma, nida Usman, muna matukar son juna.