Sashe 5
Hauwa Kulu Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A daren yau dai da Mama ta yanke masa wannan hukuncin, jinsa yake kamar mai nakuda, musamman data zo har gabansa ta dauke Hauwa zuwa dakinta mai nufin bata amince da kebewarsu ba, ya yarda da gaske Mama take ba barazana take masa kamar yadda ya dauka ba, don haka duk ya kasa zaune ya kasa tsaye, ya kasa kwanciya, ya rasa ta ina zai bi ya lallashi Mama. Shi kansa ya san abin da zai yi ya bata wa Mama rai har ta zubar da hawaye a kai, ba karamin abu bane. Ya fahimci Mama ta saka Hauwa a ranta fiye da yadda ta saka Madina a ranta ta kowane bangare, ta amshi Hauwa ne wholeheartedly sabanin Madina da dama tana kullace da abinda Babanta yayi musu, na rainin arziki, da auren da Madinah ta fara yi kafin shi ashe bata yafe ba, wannan abu kwarai ya ba shi mamaki don ya dauka tuni ta manta, ya kuma jinjina wa Mama don wani abu ne da a farko bai yi tsammani ba wato cewa zata so Hauwa ta karbeta.
**** ***** ****
SELF-EVALUATION
A
bu daya Sarham yake so ya tantance a ransa da kwakwalwarsa daga yau zuwa gobe kadai, wato he has to evaluate himself in 24 hours kafin cikar awannin da Maisharia ta bashi, he has to find-out; shin YANA SON HAUWA-KULU???
Wannan wata tambaya ce da Sarham bai san amsarta tuntuni ba, sai yau da yake cikin tsaka mai wuya, wato a sanda aka bashi zabi tsakanin cigaba da zama da Hauwa da kwace ta don ta koma ga wani wanda yafi shi sonta, wato ranar da ya samu kansa tsakanin samu da rashinta cikin rayuwarsa ne kadai ya gane Hauwa nada matukar muhimmanci a zuciyarsa da rayuwarsa kuma ya damu da ita fiyeda yadda zai iya bayyanawa. Sannan zamanta matsayin matarsa ta sunnan shi ya bashi kwanciyar hankalin da yake ciki a yanzu, wanda a baya ya rasa da ya nemeta a rayuwarsa da fadin garin Kano ya rasa.
So yake ya tursasa wa ransa ya yarda cewa, har gobe Madinah kadai yake yi wa so na soyayyah, to amma me? Sai ya gane cewa yau Mama ta bankado sirrin dake kwance dankam shekara da shekaru a kasan zuciyarsa game da Hauwa. Bayan duk wasu self-examination ya yarda YES! Hauwa-Kulu tana da wani gurbi bayan na kanwar jini a tare dashi ko ya ki Allah, ko ya ki Annabi (she has a special place in his heart), wanda acan baya yake (underestimating) dinsa da gangan, in ba haka ba me ya kai shi saka wa first daughter dinshi WAHEEDAH sunanta? Shin soyayyarsa ga Inna ce kadai ta yi attaching dinsa gare su irin haka b tareda soyayyar mace ba? Shin Inna ce ta saka shi aiko da kudi duk wata daga Jeddah (for their survival) ko kuwa tunanin karatun Hauwa-Kulu? Shin Inna ta taba yi masa tayin auren Hauwa ko ta taba ce masa tana masa shaawar aurar da yarta? Shin an taba yi wa namiji (matured) kamarsa auren da baya so?
Shin me ya sa yake kishin Jamilu, kishin nasa kuma ya tunzura shi ga auren Hauwa hajaran-majaran ganin cewa Jamilu da gaske yake? Shi dai ya san babu kishi ga maza a inda babu SO, kuma babu wanda ya yi masa dole ya auri Hauwa.
Iyayensa suna zaman-zamansu shi ya dauko Hauwa ya kawo musu har ta shiga ransu, bai kuma san dalilin da ya sayo mata soyayyah har haka a zuciyarsu ba, amma ya yarda sun amince da ita wanda babban abun farin ciki da alfahari ne a gareshi.
Ya laluba, ya bincika, ko ta ina bai ga da abin da zai lallashi Mama ta janye takunkumin saki ba, ban da ya dauki Hauwa ya tafi da ita Jeddah.
To amma ya zai yi da ita a Jeddah? A nan kam ba ta da matsalar komai, ya san Madinah ba za ta yi maraba da zuwanta ba kamar yadda kuma ba za ta hana shi yin abin da ya zame masa haqqi ba, sannan ba za ta yi wa Hauwa kowacce irin mugunta ba don keta da mugunta ba halinta bane, kai dai barta da kishinta wanda ya wuce kima, amma tabbas daga shi har Hauwa suka sake suka shiga gonarta sai ta dafa su ta ruwan sanyi babu duka babu zagi. Hakan kuma ba zai hana shi faranta wa Mama rai ba, da ceton igiyoyin aurensa dake reto, da mutuncinsa a idon su Inna ba.
Don haka barcin Dr. Sarham a wannan daren bakidaya bai fi na awanni biyu ba, shi ma sai goshin asubahi ya same shi. Abin da ya kwana mafarki kuma bakidaya a daren bai wuce Hauwan da ya kwana da ita a ransa ba.
Kusan sai da ya makara tashi sallar asubahi, abin da ba halinsa ba, Abba na hanyar dawowa daga masallaci suka hade a kofa, ya ce, Lelen Abba, ya da makara?
Ya sunkuyar da kai.
Abba ya ga har wani ramewa ya yi cikin kwana daya, yayi murmushi a ransa shikadai yace yaro wa ya gaya maka ana raina mace? Ya wuce shi yana cewa, A dinga kula da lokacin sallah, damuwoyin duniya ba masu karewa ba ne, balle su hana dan Adam barci a kan lokaci. Wani lokacin ma mu muke sayo wa kanmu damuwar da kudin mu. Ni ban ga laifin Mai Sharia ba, shes in judiciary, dole ta kasance mai adalci ga dan kowa.
Maganar nan mai sauki ce in baka son ta ka saki ka baiwa maso sonta dama, short and simple, ban ga name zaka sa damuwa a cikinta ba. Ka tabbatar kafin ta tashi daga barci ka aiwatar da umarninta don wallahi ba barazana take maka ba, iyakar gaskiyarta kenan da hukuncin da zata iya dauka a matsayinta na uwa ga kowannenku. Annan mai tabbatar da adalci a cikin alumma.
Ya sa kai ya yi wucewarsa cikin gida.
Kai! Yau hatta karatun sallah ba daidai Sarham ya karanta shi ba, astagfirullah. Ko da ya idar kuma ya kasa dawowa gida gudun haduwa da Mama. Ya ci gaba da zama a masallaci har sai da gari ya yi haske, sai a lokacin ya tuna yau ne daurin auren Surayyah, kuma karfe tara za a hallara a gadon kaya. Dole ya koma dakinsa wajen karfe bakwai na safe, yana shiga wanka ya fara yi, ya fito yana tsane kansa da tawul da wani daure a kugunsa ya hau kiran lambar Hauwa. Shi kansa bai san me zai ce mata ba. Kawai ya samu kansa da son jin muryarta.
Anyi saa Mama ta bar wayar gun Mardiyyah ita kuma tana sassan Abba, baccin safe dole ne ga Mama in dai ta san bata kwanta da wuri ba, to muddin tayi sallahr asubah zata koma barci, sai inda ‘alarm’ din data saita ya tashe ta, duk da kuwa ta san yau tana da hidimar jamaa amma jiya bata samu barci da wuri ba, bayan ta tabbatar Sarham ya tafi ta maida Hauwa dakinta kwana tayi tana rokon Allah da nafilfili akan Allah ya daidaita tsakanin su.
Mardiyya na zaune tana karanta morning azkar a cikin hisnul muslim kiran Yaya Sarham ya shigo. Tana dagawa ta gaida shi a ladabce, ya amsa, sannan yace, Me ku ke yi yanzu Mardiyya?
Ta ce, Anti tana shafa mai ne ta fito wanka, ni kuma ina azkar.
Ya ce, Mardiyyah maza ba ta wayar kafin Mama ta shigo kinji kanwata?.
Mardiyyah ta tashi ta kai wa Hauwa waya, wadda fitowarta kenan daga wanka tana shafa. Ta yi sallama a nutse, ya yi ajiyar zuciya ya ce, Maijiddah kanwar Sarham, autar Inna da Baba, yar gatan Mamanta, ki shirya maza yanzu ina jiranki kafin daurin aure zamu dan fita, don Allah bana so Mama ta sani, kiyi sauri.
Hauwa ta zaro manyan idon kamar yana kallonta cikin tsoro, Yaya Sarham! Ta yaya za mu fita Mama ba ta sani ba bata yi izni ba?
Ya ce, In ci darajar Inna, in ci albarkacin Malam, yau tana cikin hidima, ba ganewa za ta yi ba.
Musamman in muka bar Mardiyyah a dakin. Zan roke ta in ta shigo ta ce, kina toilet.
Hauwa duk ta tsure, ita ba ta saba abun rashin gaskiya ba, besides mutumin nan ina zai kai ta???
In kuma ya je ya sayar da ita fa duk a cikin rashin SO? Ta tabbata Maman ta fi shi sonta, ita ba ta da wani ‘hope’ a kansa yanzu. Dadin bakinsa na jiya bai wani dadata da kasa ba. Wallahi yanzu za ta iya zabar Mama sau dubu ta bar likitan Inna.
Hauwa ta nisa, jin wata kwalla ta taru a idonta da ta tuna yau shekara guda fa mutumin nan bai kara bi ta kanta ba, bai neme ta ba, bai damu da ita ba sai yanzu da aka ba shi yancin da yake nema ne zai bi ya kalallame ta? Hauwa ta bude manyan idanun nan ta kada su harr! Kaman Sarham yana gabanta, ta ce,
Ni kam babu inda zani Yaya Doctor ba izinin Mama.
Za ta kashe wayar kamar ya sani ya ce, Kada ki sake ki kashe min waya!.
Hauwa ta yi shiru, cikin fushin ban mamaki ya ce, Kuluwa! Na ce ko ba da Kuluwa nake magana ba?
Umarni na za ki bi ko na Mama? Shin ni da Mama wa ya biya sadakin aurenki? Kuma wa ya kawo ki cikin rayuwarsa?”
Hauwa ta sake yin shiru, kamar ta saki kuka.
Ya ce, To idan ni nake auren ki ba Mama ba, na yi miki umarnin Mardiyyah ta kawo ki mota ta yanzu-yanzu kafin Mama ta fito daga turakar Abba, ko two hours ba za mu yi ba, za mu dawo, I promised!.
Za ta yi magana ya ce,
Umarni ne ba jin raayi ba. Ya kashe wayarsa.
Hauwa har da wani gumi dake tsatstsaafo mata a goshinta ta yarfe shi da hannu, ta ce cikin yanayi na shiga rudu.
Mardiyyah na shiga uku!!!”
**** ***** ****
SELF-EVALUATION
A
bu daya Sarham yake so ya tantance a ransa da kwakwalwarsa daga yau zuwa gobe kadai, wato he has to evaluate himself in 24 hours kafin cikar awannin da Maisharia ta bashi, he has to find-out; shin YANA SON HAUWA-KULU???
Wannan wata tambaya ce da Sarham bai san amsarta tuntuni ba, sai yau da yake cikin tsaka mai wuya, wato a sanda aka bashi zabi tsakanin cigaba da zama da Hauwa da kwace ta don ta koma ga wani wanda yafi shi sonta, wato ranar da ya samu kansa tsakanin samu da rashinta cikin rayuwarsa ne kadai ya gane Hauwa nada matukar muhimmanci a zuciyarsa da rayuwarsa kuma ya damu da ita fiyeda yadda zai iya bayyanawa. Sannan zamanta matsayin matarsa ta sunnan shi ya bashi kwanciyar hankalin da yake ciki a yanzu, wanda a baya ya rasa da ya nemeta a rayuwarsa da fadin garin Kano ya rasa.
So yake ya tursasa wa ransa ya yarda cewa, har gobe Madinah kadai yake yi wa so na soyayyah, to amma me? Sai ya gane cewa yau Mama ta bankado sirrin dake kwance dankam shekara da shekaru a kasan zuciyarsa game da Hauwa. Bayan duk wasu self-examination ya yarda YES! Hauwa-Kulu tana da wani gurbi bayan na kanwar jini a tare dashi ko ya ki Allah, ko ya ki Annabi (she has a special place in his heart), wanda acan baya yake (underestimating) dinsa da gangan, in ba haka ba me ya kai shi saka wa first daughter dinshi WAHEEDAH sunanta? Shin soyayyarsa ga Inna ce kadai ta yi attaching dinsa gare su irin haka b tareda soyayyar mace ba? Shin Inna ce ta saka shi aiko da kudi duk wata daga Jeddah (for their survival) ko kuwa tunanin karatun Hauwa-Kulu? Shin Inna ta taba yi masa tayin auren Hauwa ko ta taba ce masa tana masa shaawar aurar da yarta? Shin an taba yi wa namiji (matured) kamarsa auren da baya so?
Shin me ya sa yake kishin Jamilu, kishin nasa kuma ya tunzura shi ga auren Hauwa hajaran-majaran ganin cewa Jamilu da gaske yake? Shi dai ya san babu kishi ga maza a inda babu SO, kuma babu wanda ya yi masa dole ya auri Hauwa.
Iyayensa suna zaman-zamansu shi ya dauko Hauwa ya kawo musu har ta shiga ransu, bai kuma san dalilin da ya sayo mata soyayyah har haka a zuciyarsu ba, amma ya yarda sun amince da ita wanda babban abun farin ciki da alfahari ne a gareshi.
Ya laluba, ya bincika, ko ta ina bai ga da abin da zai lallashi Mama ta janye takunkumin saki ba, ban da ya dauki Hauwa ya tafi da ita Jeddah.
To amma ya zai yi da ita a Jeddah? A nan kam ba ta da matsalar komai, ya san Madinah ba za ta yi maraba da zuwanta ba kamar yadda kuma ba za ta hana shi yin abin da ya zame masa haqqi ba, sannan ba za ta yi wa Hauwa kowacce irin mugunta ba don keta da mugunta ba halinta bane, kai dai barta da kishinta wanda ya wuce kima, amma tabbas daga shi har Hauwa suka sake suka shiga gonarta sai ta dafa su ta ruwan sanyi babu duka babu zagi. Hakan kuma ba zai hana shi faranta wa Mama rai ba, da ceton igiyoyin aurensa dake reto, da mutuncinsa a idon su Inna ba.
Don haka barcin Dr. Sarham a wannan daren bakidaya bai fi na awanni biyu ba, shi ma sai goshin asubahi ya same shi. Abin da ya kwana mafarki kuma bakidaya a daren bai wuce Hauwan da ya kwana da ita a ransa ba.
Kusan sai da ya makara tashi sallar asubahi, abin da ba halinsa ba, Abba na hanyar dawowa daga masallaci suka hade a kofa, ya ce, Lelen Abba, ya da makara?
Ya sunkuyar da kai.
Abba ya ga har wani ramewa ya yi cikin kwana daya, yayi murmushi a ransa shikadai yace yaro wa ya gaya maka ana raina mace? Ya wuce shi yana cewa, A dinga kula da lokacin sallah, damuwoyin duniya ba masu karewa ba ne, balle su hana dan Adam barci a kan lokaci. Wani lokacin ma mu muke sayo wa kanmu damuwar da kudin mu. Ni ban ga laifin Mai Sharia ba, shes in judiciary, dole ta kasance mai adalci ga dan kowa.
Maganar nan mai sauki ce in baka son ta ka saki ka baiwa maso sonta dama, short and simple, ban ga name zaka sa damuwa a cikinta ba. Ka tabbatar kafin ta tashi daga barci ka aiwatar da umarninta don wallahi ba barazana take maka ba, iyakar gaskiyarta kenan da hukuncin da zata iya dauka a matsayinta na uwa ga kowannenku. Annan mai tabbatar da adalci a cikin alumma.
Ya sa kai ya yi wucewarsa cikin gida.
Kai! Yau hatta karatun sallah ba daidai Sarham ya karanta shi ba, astagfirullah. Ko da ya idar kuma ya kasa dawowa gida gudun haduwa da Mama. Ya ci gaba da zama a masallaci har sai da gari ya yi haske, sai a lokacin ya tuna yau ne daurin auren Surayyah, kuma karfe tara za a hallara a gadon kaya. Dole ya koma dakinsa wajen karfe bakwai na safe, yana shiga wanka ya fara yi, ya fito yana tsane kansa da tawul da wani daure a kugunsa ya hau kiran lambar Hauwa. Shi kansa bai san me zai ce mata ba. Kawai ya samu kansa da son jin muryarta.
Anyi saa Mama ta bar wayar gun Mardiyyah ita kuma tana sassan Abba, baccin safe dole ne ga Mama in dai ta san bata kwanta da wuri ba, to muddin tayi sallahr asubah zata koma barci, sai inda ‘alarm’ din data saita ya tashe ta, duk da kuwa ta san yau tana da hidimar jamaa amma jiya bata samu barci da wuri ba, bayan ta tabbatar Sarham ya tafi ta maida Hauwa dakinta kwana tayi tana rokon Allah da nafilfili akan Allah ya daidaita tsakanin su.
Mardiyya na zaune tana karanta morning azkar a cikin hisnul muslim kiran Yaya Sarham ya shigo. Tana dagawa ta gaida shi a ladabce, ya amsa, sannan yace, Me ku ke yi yanzu Mardiyya?
Ta ce, Anti tana shafa mai ne ta fito wanka, ni kuma ina azkar.
Ya ce, Mardiyyah maza ba ta wayar kafin Mama ta shigo kinji kanwata?.
Mardiyyah ta tashi ta kai wa Hauwa waya, wadda fitowarta kenan daga wanka tana shafa. Ta yi sallama a nutse, ya yi ajiyar zuciya ya ce, Maijiddah kanwar Sarham, autar Inna da Baba, yar gatan Mamanta, ki shirya maza yanzu ina jiranki kafin daurin aure zamu dan fita, don Allah bana so Mama ta sani, kiyi sauri.
Hauwa ta zaro manyan idon kamar yana kallonta cikin tsoro, Yaya Sarham! Ta yaya za mu fita Mama ba ta sani ba bata yi izni ba?
Ya ce, In ci darajar Inna, in ci albarkacin Malam, yau tana cikin hidima, ba ganewa za ta yi ba.
Musamman in muka bar Mardiyyah a dakin. Zan roke ta in ta shigo ta ce, kina toilet.
Hauwa duk ta tsure, ita ba ta saba abun rashin gaskiya ba, besides mutumin nan ina zai kai ta???
In kuma ya je ya sayar da ita fa duk a cikin rashin SO? Ta tabbata Maman ta fi shi sonta, ita ba ta da wani ‘hope’ a kansa yanzu. Dadin bakinsa na jiya bai wani dadata da kasa ba. Wallahi yanzu za ta iya zabar Mama sau dubu ta bar likitan Inna.
Hauwa ta nisa, jin wata kwalla ta taru a idonta da ta tuna yau shekara guda fa mutumin nan bai kara bi ta kanta ba, bai neme ta ba, bai damu da ita ba sai yanzu da aka ba shi yancin da yake nema ne zai bi ya kalallame ta? Hauwa ta bude manyan idanun nan ta kada su harr! Kaman Sarham yana gabanta, ta ce,
Ni kam babu inda zani Yaya Doctor ba izinin Mama.
Za ta kashe wayar kamar ya sani ya ce, Kada ki sake ki kashe min waya!.
Hauwa ta yi shiru, cikin fushin ban mamaki ya ce, Kuluwa! Na ce ko ba da Kuluwa nake magana ba?
Umarni na za ki bi ko na Mama? Shin ni da Mama wa ya biya sadakin aurenki? Kuma wa ya kawo ki cikin rayuwarsa?”
Hauwa ta sake yin shiru, kamar ta saki kuka.
Ya ce, To idan ni nake auren ki ba Mama ba, na yi miki umarnin Mardiyyah ta kawo ki mota ta yanzu-yanzu kafin Mama ta fito daga turakar Abba, ko two hours ba za mu yi ba, za mu dawo, I promised!.
Za ta yi magana ya ce,
Umarni ne ba jin raayi ba. Ya kashe wayarsa.
Hauwa har da wani gumi dake tsatstsaafo mata a goshinta ta yarfe shi da hannu, ta ce cikin yanayi na shiga rudu.
Mardiyyah na shiga uku!!!”