Sashe 16
Hauwa Kulu Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wato wannan din ita ce rayuwar da Mama ke mata fighting mata don ta samu, shima kuma akan karan-kansa ita ce irin soyayyar da yake ikirarin ita baya yi mata a can baya?
Tana iya jin amon sautin muryarsa har zuwa lokacin cikin kwanyarta, a sanda yake cewa, ya janye kalamansa na baya.
Yau kam ta gasgata cewa Mama Uwa ce ta gari kuma mai sonta da alkhairin da kowacce mace ke samu a gidan aure, ta yarda Mama Uwar kowa ce ba ta Sarham kadai ba, domin yau ne ita ma ta san tana da wani boyayyen feeling mara fassaruwa a kan Sarham da ba ta san da shi ba sai yau. Kuma yau ne ta san mecece soyayyar kanta.
Da kyar ta roke shi kan yayi hakuri tana jin yunwa kuma bata yi sallah ba. Abincin da sai da ya sandare Sarham da Hauwa suka samu cin sa. Kasancewar dama a bowl na tangaran ya zuba musu baa warmers ba.
Da ya dawo sallah ya samu itama tana sallah, sai ya dauki abincin ya ajiye a kan ‘center-table’ ya jira har ta idar, shi ya zuba musu abincin suka ci a bowl guda.
Tun kafin ma ta gama cin abincin ya karkade gadon ya sake shimfida da sabon zanin gado hade da duvet dinsa, ya dauke wancan ya saka a kayan wanki, ya gyara dakin ya kimtsa komai da ta bata a dakin ya fesa room fresh, ya kuma hada mata ruwan wanka.
Hauwa na kammala cin abinci ta ji ta dauke a hannun Sarham. Bai direta ko a ina ba sai cikin ruwan wankan da ya hada ya saka ta da kayan jikinta da komai gaba daya, yace I wish you could see.. cewa yau tare Sarham da Hauwa zasuyi wanka abinsu. Gadaya ya sukurkuta Hauwa, ya kidimata da abinda yake fada. Daga bisani ta dauka marfi take yi saboda alamuran da yake gudanawar a gare ta masu ruda kwakwalwa ne da kidima masoyi, Hauwa-Kulu za ta iya cewa a cikin kwamin wankannan ta kara amsa sunan matar Sarham ba tare da ta ankara da yadda hakan ta faru ba. Amma hakika ta yi dauriyar da shikansa ya yaba mata. Don ba ta yi wani hobbasa don hana shi samun nutsuwar da ya nemi samu daga gare ta ba don ganin cewa a toilet ne, ta jure duk ta faranta masa rai a yadda ya bukata.
Shi ma kuma ya biyar da ita ne ta hanyar da ya kara mamaye zuciyarta da so da matsanancin so da kaunarsa.
Tun daga ranar Sarham da Hauwa suka dinke suka zama abu guda, musamman da Madinah ta ba su fili ta hanyar fita sabgar mijin kwatakwata, sai hakan ya bashi damar samun wani irin kusanci da Hauwa-Kulu, Madinah ta fara zuwa aikin dole datasa kanta, su kuma sun zama tantabaru don soyayya a gida. Wani lokacin yana office da ya samu sararin aiki kawai zai tuko motarshi ya dawo gida, ya kuma samu Hauwa matan da ake shuara bata nuna gazawa bata korafi akan dukkan bukatunsa, Hauwa sai yadda yake so ta ke yi, wato sai abin da ya koyar da ita.
Madinah na tunanin bar musu filin gidan da ta yi shi zai sa Sarham ya yi marmarinta, ya gane banbancinta da Hauwa, wato ya gane bambancin da ke tsakanin musaka da mai aji, bata san cewa a fannin matantaka duk mace sunanta mace ba, in dai tanada koshin lafiya kuma tana kula da jikinta, bata san hakan ya bai wa Sarham da Hauwa damar dinkewa ba suka manne wa juna suka like kamar tip da taya cikin morar niimar da Allah ya halatta a tsakaninsu, da wata irin soyayyar auratayya mai wuyar fassaruwa.
Kusan kullum ne Sarham sai ya sato jiki daga office ya dawo gida, don dai ya tabbatar da lafiyar Hauwa dama kuma Mama ta gama shirya yar ta tsaf, fiye da tsammanin dan Adam, don haka Hauwa ta gama tashin kan Sarham gaba daya, tunda Madinah ta shata layi a tsakaninshi da ita tun zuwan Hauwa gidan, a cewarta ta barwa Hauwa, tana kyamar hada miji da mijin musaka.
Madinah kam sai dai ya gode mata da wannan filin da ta bashi yake wani irin amarci kamar bai taba samun lafiyayyar mace a hannunsa ba sai a kan Hauwa. Shi da kansa ya hana Sumayya dawowa gidan, ya gaya mata ba yanzu ba, sai sun gama honeymoon, kada tazo ta bata masa mata da kilbibi.
Ko daga nan Sumayya ta gane Hauwa komai zamzam, don ko waya bata samun amsawa yanzu, kullum likita na makale da ita, ta nan Sumayyah ta gane komai ya fara saisaita. Farin cikin Sumayyah ya kasa boyuwa. Ga Usman ya like yana bin Sarham da gaske yana so ya turo ayi tambayar aurensa da Sumayya. Sarham kuma yana basarwa yana cewa ya nemi amincewar Madinah.
Madinah wadda a lokacin fama take da kanta, cikinta ya fara girma da ga matsaloli irin na mace mai juna biyun da ya fara tasawa, ga rashin kwanciyar hankalin data sawa ranta na barranta kanta da rayuwa da mijinta, wanda ta debi shekara da shekaru cikin fafutukar samunsa. Wannan yasa ba tareda sanin ta ba, a tsaitsaye BP dinta ya hau, yau tana asibitinsu tana duba patient mai hakiyar ido, Hauwan Sarham ta fado mata a rai. Tsaki tayi kanta yayi mugun sarawa, kawai sai ta saki komai ta dafe kanta, ta sulale a kujerarta cikin wani hali na unconsciousness. With high blood pressure.
Nurse din da suke tare suna duba patient din ce ta ankara da gushewar hayyacin Dr. madinah, tayi maza ta yi kanta ta, kuma dinga danna ‘alarm’ na kiran likitoci da gaggawa.
A karshe gado aka baiwa Dr. Madinah a asibitinsu. Nan da nan aka shiga bata taimakon gaggawa don tana bleeding, kokarin su shine su tsayar da cikin jikin ta amma a karshe suka ga tsayar da shawarar gara su cire shi don ceton nata rayuwar.
Sarham na asibiti yana aiki Usman ya kira shi wai yazo yasa hannu zaa yiwa Madina tiyata a Dr. Siddiqah.
Tsananin kidima data same shi a lokacin manta hanyar asibitin nasu yayi sai Usman ne suka hadu a hanya yayi masa jagora.
Ya samu duk yan gidansu Madina sun riga shi hallara a asibitin shikadai ake jira amma kafin ya zo ma Daddy ya kulu ya saka hannu yace a shiga ayi mata, ciki kuma a cire shi in shi ke bata matsala. Babban Yayansu Madinah wato Abubakar Attahiru yace Daddy baka da wannan hurumin fa, ka bari mijinta ya karaso. Sai gashi ya shigo kamar an jefo shi shida Usman.
Daga kallon da Hajjah Ramlah take masa duk ya sha jinin jikinsa. Amma ya maida hankali ga yin needful, wato ya saka hannu aka shiga da Madina dakin tiyata.
Dukkansu jigum-jigum sukayi a reception shida iyayen Madina da yayyenta, Hajjah Ramlah ta kasa shiru tana tsane ido tace wallahi in Madinah ta rasa ranta saboda kai Sarhamu, bazan taba yafe maka ba, tun farko ai nace ta hakura da aurennan babu dole tunda har zaka iya rufe ido kayi mata kishiya da makauniya nace ta hakura, amma da yake kunnenta na kashi ne ta zauna a gidan kuna guma mata takaicin da yau yake neman ranta.
Alhaji Attahiru Habibu Sorondinki, ya kankance ido akan matarsa yana neman karin bayani yace me ke faruwa wai? Ki yi min bayani. Hajjah Ramlah na kuka ta zayyane masa komai cewa Sarham kara aure yayi da makauniya yar talakawa shine fa tun lokacin Madina take boye musu itama daliline yasa taji data yi tsami tsakanin ta da kanwar mijin nata.
Alhaji Attahiru jikinsa har tsuma yake ya nuna Sarham da dan alinsa yace wallahi in ya ta ta mutu sai nayi karar ka, azzalumi wanda bai san mutunci ba. ai shiyasa tun farko naki yarda ta aureka don yayan talakawannan ko a tandun mai aka saka ku sai kun fito kandas wajen nuna halinku na rashin halacci. Banda mutuwa mai tonon asiri ai Madinah matar manya ce ba irinka ba.
Kan Sarham a kasa yana jin cin mutuncin da Daddyn Madinah ke masa bai dago ba saida Daddyn yazo nan. Ya dago a hankali ya dubeshi idanunsa sun kada kamar gauta amma uffan ya kasa cewa. A lokacin aka fito da Madina daga dakin tiyata zuwa dakin jinya aka kuma hana su shiga sai bayan awa daya.
Saida Madinah ta dawo hayyacinta aka bar su suka shiga, family dinta suka rufu a kanta Waheedah na hannunHajjah Ramlah shi suka manta da shi a gefe. Abin yayi masa ciwo kwarai sai Usman ne ya zo ya kama hannunsa zuwa kan Madinah. Ta dube shi, ya dubeta suka kuma hada ido, ta lumshe idanunta bata kara budewa don bata son ma ganinsa a kanta.
Da aka bata sallama ma bayan kwana uku gidansa Daddy ya tafi da ita ba tareda nemsn iznin Sarham ba. ciki kuma an cireshi bayan ya fara girma.
Ko kusa Hauwa bata san me yake faruwa ba amma ta lura Sarhamya rage magana kuma baya cikin walwala kamar da. Shiyasa yau da Sumayyah ta nemi zuwa gidan don tayi weekend tare dasu bai hanata ba yace tana iya zuwa dakinta yana nan. Hauwa kuma yace su koma nasa dakin don nata yayi kusa dana Sumayyah, ta tambayeshi ko hakan bazai zama matsala ga Anti Madinah ba? sai yace bata nan tayi tafiya. Da haka sukayi parking dakinsa soyayya a tsakaninsu sai abinda ya karu.
Jumaah da yamma Sumayyah ta iso gidan daga makaranta.
Har ila yau, shi da team dinsa na Saudi-German suna ci gaba da shirye-shiryen aikin idon da za su yi wa Hauwa.
Tun ba a je ko ina ba Sarham ya gane shigar ciki a tare da Hauwa, tunda yanzu tare suke a daki guda duk wani motsinta ya sani. Wanda ita koda wasa bata san da cikin ba.
Kasa shiru ya yi don farin cikin da ya cika shi, wani na tafiya rariya wani na zuwa, har sai da yayi mata shagube cikin tsokana.
Ya daga PT strip din da ya auna fitsarin ta, yace wai yanzu Hauwa-Jiddah daga zuwa sai ciki? Bazaki barni ma in gama yada samartakata a jikin ki ba mu tsufa tare? Kamar wadda ta yi tuntube da shi a dokin kofa?
Hauwa saita saka kuka don tsakani da Allah ta tsorata da wannan maganar, ciki fa na haihuwa yake nufi? Ta yaya ta sameshi ma bata sani ba.
Yace Cry more Sweetheart, wani kukan ma sai an je labour room!.
Tana iya jin amon sautin muryarsa har zuwa lokacin cikin kwanyarta, a sanda yake cewa, ya janye kalamansa na baya.
Yau kam ta gasgata cewa Mama Uwa ce ta gari kuma mai sonta da alkhairin da kowacce mace ke samu a gidan aure, ta yarda Mama Uwar kowa ce ba ta Sarham kadai ba, domin yau ne ita ma ta san tana da wani boyayyen feeling mara fassaruwa a kan Sarham da ba ta san da shi ba sai yau. Kuma yau ne ta san mecece soyayyar kanta.
Da kyar ta roke shi kan yayi hakuri tana jin yunwa kuma bata yi sallah ba. Abincin da sai da ya sandare Sarham da Hauwa suka samu cin sa. Kasancewar dama a bowl na tangaran ya zuba musu baa warmers ba.
Da ya dawo sallah ya samu itama tana sallah, sai ya dauki abincin ya ajiye a kan ‘center-table’ ya jira har ta idar, shi ya zuba musu abincin suka ci a bowl guda.
Tun kafin ma ta gama cin abincin ya karkade gadon ya sake shimfida da sabon zanin gado hade da duvet dinsa, ya dauke wancan ya saka a kayan wanki, ya gyara dakin ya kimtsa komai da ta bata a dakin ya fesa room fresh, ya kuma hada mata ruwan wanka.
Hauwa na kammala cin abinci ta ji ta dauke a hannun Sarham. Bai direta ko a ina ba sai cikin ruwan wankan da ya hada ya saka ta da kayan jikinta da komai gaba daya, yace I wish you could see.. cewa yau tare Sarham da Hauwa zasuyi wanka abinsu. Gadaya ya sukurkuta Hauwa, ya kidimata da abinda yake fada. Daga bisani ta dauka marfi take yi saboda alamuran da yake gudanawar a gare ta masu ruda kwakwalwa ne da kidima masoyi, Hauwa-Kulu za ta iya cewa a cikin kwamin wankannan ta kara amsa sunan matar Sarham ba tare da ta ankara da yadda hakan ta faru ba. Amma hakika ta yi dauriyar da shikansa ya yaba mata. Don ba ta yi wani hobbasa don hana shi samun nutsuwar da ya nemi samu daga gare ta ba don ganin cewa a toilet ne, ta jure duk ta faranta masa rai a yadda ya bukata.
Shi ma kuma ya biyar da ita ne ta hanyar da ya kara mamaye zuciyarta da so da matsanancin so da kaunarsa.
Tun daga ranar Sarham da Hauwa suka dinke suka zama abu guda, musamman da Madinah ta ba su fili ta hanyar fita sabgar mijin kwatakwata, sai hakan ya bashi damar samun wani irin kusanci da Hauwa-Kulu, Madinah ta fara zuwa aikin dole datasa kanta, su kuma sun zama tantabaru don soyayya a gida. Wani lokacin yana office da ya samu sararin aiki kawai zai tuko motarshi ya dawo gida, ya kuma samu Hauwa matan da ake shuara bata nuna gazawa bata korafi akan dukkan bukatunsa, Hauwa sai yadda yake so ta ke yi, wato sai abin da ya koyar da ita.
Madinah na tunanin bar musu filin gidan da ta yi shi zai sa Sarham ya yi marmarinta, ya gane banbancinta da Hauwa, wato ya gane bambancin da ke tsakanin musaka da mai aji, bata san cewa a fannin matantaka duk mace sunanta mace ba, in dai tanada koshin lafiya kuma tana kula da jikinta, bata san hakan ya bai wa Sarham da Hauwa damar dinkewa ba suka manne wa juna suka like kamar tip da taya cikin morar niimar da Allah ya halatta a tsakaninsu, da wata irin soyayyar auratayya mai wuyar fassaruwa.
Kusan kullum ne Sarham sai ya sato jiki daga office ya dawo gida, don dai ya tabbatar da lafiyar Hauwa dama kuma Mama ta gama shirya yar ta tsaf, fiye da tsammanin dan Adam, don haka Hauwa ta gama tashin kan Sarham gaba daya, tunda Madinah ta shata layi a tsakaninshi da ita tun zuwan Hauwa gidan, a cewarta ta barwa Hauwa, tana kyamar hada miji da mijin musaka.
Madinah kam sai dai ya gode mata da wannan filin da ta bashi yake wani irin amarci kamar bai taba samun lafiyayyar mace a hannunsa ba sai a kan Hauwa. Shi da kansa ya hana Sumayya dawowa gidan, ya gaya mata ba yanzu ba, sai sun gama honeymoon, kada tazo ta bata masa mata da kilbibi.
Ko daga nan Sumayya ta gane Hauwa komai zamzam, don ko waya bata samun amsawa yanzu, kullum likita na makale da ita, ta nan Sumayyah ta gane komai ya fara saisaita. Farin cikin Sumayyah ya kasa boyuwa. Ga Usman ya like yana bin Sarham da gaske yana so ya turo ayi tambayar aurensa da Sumayya. Sarham kuma yana basarwa yana cewa ya nemi amincewar Madinah.
Madinah wadda a lokacin fama take da kanta, cikinta ya fara girma da ga matsaloli irin na mace mai juna biyun da ya fara tasawa, ga rashin kwanciyar hankalin data sawa ranta na barranta kanta da rayuwa da mijinta, wanda ta debi shekara da shekaru cikin fafutukar samunsa. Wannan yasa ba tareda sanin ta ba, a tsaitsaye BP dinta ya hau, yau tana asibitinsu tana duba patient mai hakiyar ido, Hauwan Sarham ta fado mata a rai. Tsaki tayi kanta yayi mugun sarawa, kawai sai ta saki komai ta dafe kanta, ta sulale a kujerarta cikin wani hali na unconsciousness. With high blood pressure.
Nurse din da suke tare suna duba patient din ce ta ankara da gushewar hayyacin Dr. madinah, tayi maza ta yi kanta ta, kuma dinga danna ‘alarm’ na kiran likitoci da gaggawa.
A karshe gado aka baiwa Dr. Madinah a asibitinsu. Nan da nan aka shiga bata taimakon gaggawa don tana bleeding, kokarin su shine su tsayar da cikin jikin ta amma a karshe suka ga tsayar da shawarar gara su cire shi don ceton nata rayuwar.
Sarham na asibiti yana aiki Usman ya kira shi wai yazo yasa hannu zaa yiwa Madina tiyata a Dr. Siddiqah.
Tsananin kidima data same shi a lokacin manta hanyar asibitin nasu yayi sai Usman ne suka hadu a hanya yayi masa jagora.
Ya samu duk yan gidansu Madina sun riga shi hallara a asibitin shikadai ake jira amma kafin ya zo ma Daddy ya kulu ya saka hannu yace a shiga ayi mata, ciki kuma a cire shi in shi ke bata matsala. Babban Yayansu Madinah wato Abubakar Attahiru yace Daddy baka da wannan hurumin fa, ka bari mijinta ya karaso. Sai gashi ya shigo kamar an jefo shi shida Usman.
Daga kallon da Hajjah Ramlah take masa duk ya sha jinin jikinsa. Amma ya maida hankali ga yin needful, wato ya saka hannu aka shiga da Madina dakin tiyata.
Dukkansu jigum-jigum sukayi a reception shida iyayen Madina da yayyenta, Hajjah Ramlah ta kasa shiru tana tsane ido tace wallahi in Madinah ta rasa ranta saboda kai Sarhamu, bazan taba yafe maka ba, tun farko ai nace ta hakura da aurennan babu dole tunda har zaka iya rufe ido kayi mata kishiya da makauniya nace ta hakura, amma da yake kunnenta na kashi ne ta zauna a gidan kuna guma mata takaicin da yau yake neman ranta.
Alhaji Attahiru Habibu Sorondinki, ya kankance ido akan matarsa yana neman karin bayani yace me ke faruwa wai? Ki yi min bayani. Hajjah Ramlah na kuka ta zayyane masa komai cewa Sarham kara aure yayi da makauniya yar talakawa shine fa tun lokacin Madina take boye musu itama daliline yasa taji data yi tsami tsakanin ta da kanwar mijin nata.
Alhaji Attahiru jikinsa har tsuma yake ya nuna Sarham da dan alinsa yace wallahi in ya ta ta mutu sai nayi karar ka, azzalumi wanda bai san mutunci ba. ai shiyasa tun farko naki yarda ta aureka don yayan talakawannan ko a tandun mai aka saka ku sai kun fito kandas wajen nuna halinku na rashin halacci. Banda mutuwa mai tonon asiri ai Madinah matar manya ce ba irinka ba.
Kan Sarham a kasa yana jin cin mutuncin da Daddyn Madinah ke masa bai dago ba saida Daddyn yazo nan. Ya dago a hankali ya dubeshi idanunsa sun kada kamar gauta amma uffan ya kasa cewa. A lokacin aka fito da Madina daga dakin tiyata zuwa dakin jinya aka kuma hana su shiga sai bayan awa daya.
Saida Madinah ta dawo hayyacinta aka bar su suka shiga, family dinta suka rufu a kanta Waheedah na hannunHajjah Ramlah shi suka manta da shi a gefe. Abin yayi masa ciwo kwarai sai Usman ne ya zo ya kama hannunsa zuwa kan Madinah. Ta dube shi, ya dubeta suka kuma hada ido, ta lumshe idanunta bata kara budewa don bata son ma ganinsa a kanta.
Da aka bata sallama ma bayan kwana uku gidansa Daddy ya tafi da ita ba tareda nemsn iznin Sarham ba. ciki kuma an cireshi bayan ya fara girma.
Ko kusa Hauwa bata san me yake faruwa ba amma ta lura Sarhamya rage magana kuma baya cikin walwala kamar da. Shiyasa yau da Sumayyah ta nemi zuwa gidan don tayi weekend tare dasu bai hanata ba yace tana iya zuwa dakinta yana nan. Hauwa kuma yace su koma nasa dakin don nata yayi kusa dana Sumayyah, ta tambayeshi ko hakan bazai zama matsala ga Anti Madinah ba? sai yace bata nan tayi tafiya. Da haka sukayi parking dakinsa soyayya a tsakaninsu sai abinda ya karu.
Jumaah da yamma Sumayyah ta iso gidan daga makaranta.
Har ila yau, shi da team dinsa na Saudi-German suna ci gaba da shirye-shiryen aikin idon da za su yi wa Hauwa.
Tun ba a je ko ina ba Sarham ya gane shigar ciki a tare da Hauwa, tunda yanzu tare suke a daki guda duk wani motsinta ya sani. Wanda ita koda wasa bata san da cikin ba.
Kasa shiru ya yi don farin cikin da ya cika shi, wani na tafiya rariya wani na zuwa, har sai da yayi mata shagube cikin tsokana.
Ya daga PT strip din da ya auna fitsarin ta, yace wai yanzu Hauwa-Jiddah daga zuwa sai ciki? Bazaki barni ma in gama yada samartakata a jikin ki ba mu tsufa tare? Kamar wadda ta yi tuntube da shi a dokin kofa?
Hauwa saita saka kuka don tsakani da Allah ta tsorata da wannan maganar, ciki fa na haihuwa yake nufi? Ta yaya ta sameshi ma bata sani ba.
Yace Cry more Sweetheart, wani kukan ma sai an je labour room!.