Sashe 9
Girma Ya Fadi Book 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Shi kansa Ya Faruk ya lura duk dokin zuwansa da nake, ya sagar min da gwiwa, don kuwa tunda na kwashi shirgina na haura kafa na yi dakinmu bai kara jin duriyata a gidan ba.
Da daddare ya saba ni nake kai mishi abinci har dakinsa, amma yau sai Zulkiflu ne ya kai masa, domin Inna Rakiyar da ta kwashe tuwon ta yi kiran duniyar nan na yi kamar ban ji ta ba.
Ganin Zulkiflu ya kawo mai abinci, ya tabbatar Abu dai fushi take yi. Ya yi cilli da jaridar da yake karantawa ya miqe ya shigo cikin gidan har dakin Innata.
A lokacin ina cin tuwo, sai kawai yasa hannu cikin tuwona yana ci, na lura cin nasa har da mugunta ne, domin kan na kai loma daya ya kai uku gunduma-gunduma, nan da nan ya cinye mun tuwon. Na tsame hannuna na koma gefe ina ta kumburi, sai ya fita ya dawo da roba da sabulu gami da ruwa a buta. Ya soma wanke min miyar kukar.
Inna ta ce, “Mulki sai mai shi”. Ya ce, “Kwarai, wannan Princess Diana ce”. Ban san sanda na yi murmushi ba. Ya ce, “To ko ke fa? Baki ga yadda kika yi kyau ba, da wannan murmushin naki mai narka zuciya, da wannan fararen idanun naki irin na Princess Diana, da wannan yalolon gashin naki irin nata. Na rantse da za ta ganki sai ta ce ke kanwarta ce. Duk namijin da Allah ya ba shi ke a matsayin mata, ya yi mai baiwa da rabin addininsa.
Ga dai kyau ga kyan hali, ga hankali da addini. Ga Alqur’ani a cikin kanki. Ga ki da daukar rayuwa da sauki ban san ki da zuciya ba. A kullum kina auna abubuwa a mizani na hankali, ki yi hukunci wanda ya dace, ban san yaushe kika koma bin son zuciya ba….”
Na toshe mishi baki cikin dabara ya cire hannun yace, “Is o.k, mun shirya ko Abuna? Taso maza muje ki gaya mun abubuwan da kika gabatar da bana nan, da kuma shirye-shiryen ki na tafiya babbar makaranta. Duk ‘ya’yan kirki suna makaranta sai ke ‘yar gatan Innarta da Ya Faruq”.
Ya juya ya fita, Inna na ta mamakin mu. Da gudu na juya na je na sako bantena, na dora doguwar riga a kai, na daura karamin hijabi, na bishi muka fita waje muka zauna a kan dakalin kofar gida.
Garin babu hasken lantarki sai na farin wata na daren goma sha hudu. Taurari birjik sun mamaye sararin samaniyar Subhana, sun kara haskakata. Da yake bayan isha ne duk almajiran Malam sun shiga gari bara, don ba duka Malam ke iya ciyar dasu ba saboda yawansu.
Na sanya hannu na lalubo ‘yar akwatuna daga cikin bantena, Ya Faruq na ba na ce, “Ga amana, ka ajiye min. Domin Baba Sa’idu ya ce kada in sake in bari Inna ta kyautar min da zobban nan, a nan gaba za suyi mun amfani”.
Cikin mamaki Ya Faruq ya soma kiciniyar bude akwatun, wani haske da ya fito ya dallare mana idanu ba shiri ya mayar ya rufe, daga inda nake ina iya juyo irin bugun da zuciyarshi ta shiga yi da sauri da sauri.
Ya sake budewa domin tabbatarwa ya fiddo daya yana juya shi a hannunsa, hasken wata da taurari na kara masa walkiya. Ya ce cikin shakakkiyar murya, “Shi…… Baba Sa’idun… ne ya baki wannan da kansa Abu?”
Na ce, “Allah shine, nima da fari na ji tsoro. Amma ya ce kar in sake in bawa Inna, to ni kuma na gaji da boyon su kullum tare dasu nake barci, har bandaki dasu nake shiga, shi yasa na matsu ka dawo”. Ya ce, “To ai nima wannan ya fi karfin in ajje shi wurina ‘sapphire’ ne (shudin yakutu) komai na iya faruwa. Shima Baban ban da abinsa bai dace da ya baki wannan ba yanzu, haba! Sai dai in kai banki”. Na ce, “Banki kuma Ya Faruq, ba kuxi ake ajiyewa a banki ba?” Ya ce, “Wannan ya fi karfin kudi, ya fi karfin zinari da diamond. Ana ajiye (valuable goods) wato kaya masu daraja a banki”.
Ya yi shiru cikin tunani mai zurfi, da alama kanshi ya yi zafi. Can ya ce,
“Gaya mun irin hirarrakin da kuke da Baba Sa’idu?”
Na gaya masa irin nasihohin da yake yi mun ne kadai a kan sallah, sai irin wulakancin da Inna na ke mishi. Na ce, “Abin yana damuna Ya Faruq, shin me yasa Inna ta tsani Baba Sa’idu ne? Me ya yi kullum yake cewa ta yafe mishi tana wulakanta shi?”
Akwai alamun rudewa sosai a tare da Ya Faruq, ya rasa amsar da zai bani, daga bisani ya daure ya ce,
“Ban san yaushe kika koyi sanya ido a kan abin da bai shafeki ba. Ba tare kika tashi kika gansu ba Abu? To ki bisu da yadda kika gansu, nima ban sani ba.
A yanzu haka Farfesa ya turo ni ne da wani al’amari mai girma wanda ban san yadda zan yi in shawo kan Innarki ba, don Malam ba matsala bane sai ita din mai tsatstsauran ra’ayi sa rashin kaunar duk wani al’amari daya shafi Baba Sa’idu. Ya turo ni ne da zungureriyar wasika zuwa ga Malam da ita Inna, kan su bada ke in tafi dake, an samar muku makaranta keda su Ifty.
Amma sanin kanki ne wannan ba karamin aiki bane ya hada ni dashi, tunda shima ya buga ya kasa balle ni? Sannan Inna Rabi na ganin mutunci na fiyeda kowa, ina tsoron abinda zai zubar da wannan mutuncin, ya rana na kaunata a zuciyarta. Saidai na gamsu da hujjojin da ya bayar.”
Daidai nan Malam ya karaso ya tadda mu, wani almajirin sa Matt ya rikon masa leda, da alama irin tsira da balanghiga gu da ya saba kawo mana ne duk dare, yana murmushi yace “yaya dai? Wa da ‘yar kanwar shi ana shawara ne?”
Muka yi murmushi dukkanmu tare da sunkuyar da kai kasa. Yace “ku tashi mu shiga gida, bana son zama cikin hasken farin watannan, yana gadar da ciwo”. Muka mike muka shiga gidan gabadaya, shi da Malam suka shige turakar Mallam din, nikuma nayi daki na kwanta.
Inna na bisa sallama tana ta sallah, wannan al’adarta ne na duk daren juma’ah kwana take sallah. Ta kan ce, “wanda ya bari du iya da Kyale-kyalenta ya rudest, ya manta da ambaton Allah da yawa ita tuba a gareshi, haqiqa yana cikin rafkanannu.
Don haka nima ta koya min, har yabi jinin jikina. Sau tari na kan bita muyi ta yi, har sai kafafuna sun sare, yawun bakina ya bushe.
A can dakin Malam me suka ce – me suka ce oho! Was he gari da asuba hi dai naga fuskar Malam babu annuri. Bayan yayi sallar asubah gari yayi Dan shaawa! Haka, misalin karfe shidda na safe ya shigo dakinmu. Inna na bisa sallaya tana lazumi har zuwa lokacin ba ta mike ba, ni kuma ina kwance bisa gado bayan da na ida sallah ban iya na koma ba.
Na dai rufe ido ne kawai cike da tunanin al’amuran rayuwa masu rudarwa, su sanya zuciyar mutum cikin wani hali na rashin sanin tabbas da rashin jin dadin rayuwar ko ta yaya. Ba a rasa ci ba, ba a rasa sha ba, ba a rasa suttura ba amma zukatan al’umma babu dadi. Wannan ita ce hakikanin rayuwar da ke faruwa a cikin gidanmu.
Da daddare ya saba ni nake kai mishi abinci har dakinsa, amma yau sai Zulkiflu ne ya kai masa, domin Inna Rakiyar da ta kwashe tuwon ta yi kiran duniyar nan na yi kamar ban ji ta ba.
Ganin Zulkiflu ya kawo mai abinci, ya tabbatar Abu dai fushi take yi. Ya yi cilli da jaridar da yake karantawa ya miqe ya shigo cikin gidan har dakin Innata.
A lokacin ina cin tuwo, sai kawai yasa hannu cikin tuwona yana ci, na lura cin nasa har da mugunta ne, domin kan na kai loma daya ya kai uku gunduma-gunduma, nan da nan ya cinye mun tuwon. Na tsame hannuna na koma gefe ina ta kumburi, sai ya fita ya dawo da roba da sabulu gami da ruwa a buta. Ya soma wanke min miyar kukar.
Inna ta ce, “Mulki sai mai shi”. Ya ce, “Kwarai, wannan Princess Diana ce”. Ban san sanda na yi murmushi ba. Ya ce, “To ko ke fa? Baki ga yadda kika yi kyau ba, da wannan murmushin naki mai narka zuciya, da wannan fararen idanun naki irin na Princess Diana, da wannan yalolon gashin naki irin nata. Na rantse da za ta ganki sai ta ce ke kanwarta ce. Duk namijin da Allah ya ba shi ke a matsayin mata, ya yi mai baiwa da rabin addininsa.
Ga dai kyau ga kyan hali, ga hankali da addini. Ga Alqur’ani a cikin kanki. Ga ki da daukar rayuwa da sauki ban san ki da zuciya ba. A kullum kina auna abubuwa a mizani na hankali, ki yi hukunci wanda ya dace, ban san yaushe kika koma bin son zuciya ba….”
Na toshe mishi baki cikin dabara ya cire hannun yace, “Is o.k, mun shirya ko Abuna? Taso maza muje ki gaya mun abubuwan da kika gabatar da bana nan, da kuma shirye-shiryen ki na tafiya babbar makaranta. Duk ‘ya’yan kirki suna makaranta sai ke ‘yar gatan Innarta da Ya Faruq”.
Ya juya ya fita, Inna na ta mamakin mu. Da gudu na juya na je na sako bantena, na dora doguwar riga a kai, na daura karamin hijabi, na bishi muka fita waje muka zauna a kan dakalin kofar gida.
Garin babu hasken lantarki sai na farin wata na daren goma sha hudu. Taurari birjik sun mamaye sararin samaniyar Subhana, sun kara haskakata. Da yake bayan isha ne duk almajiran Malam sun shiga gari bara, don ba duka Malam ke iya ciyar dasu ba saboda yawansu.
Na sanya hannu na lalubo ‘yar akwatuna daga cikin bantena, Ya Faruq na ba na ce, “Ga amana, ka ajiye min. Domin Baba Sa’idu ya ce kada in sake in bari Inna ta kyautar min da zobban nan, a nan gaba za suyi mun amfani”.
Cikin mamaki Ya Faruq ya soma kiciniyar bude akwatun, wani haske da ya fito ya dallare mana idanu ba shiri ya mayar ya rufe, daga inda nake ina iya juyo irin bugun da zuciyarshi ta shiga yi da sauri da sauri.
Ya sake budewa domin tabbatarwa ya fiddo daya yana juya shi a hannunsa, hasken wata da taurari na kara masa walkiya. Ya ce cikin shakakkiyar murya, “Shi…… Baba Sa’idun… ne ya baki wannan da kansa Abu?”
Na ce, “Allah shine, nima da fari na ji tsoro. Amma ya ce kar in sake in bawa Inna, to ni kuma na gaji da boyon su kullum tare dasu nake barci, har bandaki dasu nake shiga, shi yasa na matsu ka dawo”. Ya ce, “To ai nima wannan ya fi karfin in ajje shi wurina ‘sapphire’ ne (shudin yakutu) komai na iya faruwa. Shima Baban ban da abinsa bai dace da ya baki wannan ba yanzu, haba! Sai dai in kai banki”. Na ce, “Banki kuma Ya Faruq, ba kuxi ake ajiyewa a banki ba?” Ya ce, “Wannan ya fi karfin kudi, ya fi karfin zinari da diamond. Ana ajiye (valuable goods) wato kaya masu daraja a banki”.
Ya yi shiru cikin tunani mai zurfi, da alama kanshi ya yi zafi. Can ya ce,
“Gaya mun irin hirarrakin da kuke da Baba Sa’idu?”
Na gaya masa irin nasihohin da yake yi mun ne kadai a kan sallah, sai irin wulakancin da Inna na ke mishi. Na ce, “Abin yana damuna Ya Faruq, shin me yasa Inna ta tsani Baba Sa’idu ne? Me ya yi kullum yake cewa ta yafe mishi tana wulakanta shi?”
Akwai alamun rudewa sosai a tare da Ya Faruq, ya rasa amsar da zai bani, daga bisani ya daure ya ce,
“Ban san yaushe kika koyi sanya ido a kan abin da bai shafeki ba. Ba tare kika tashi kika gansu ba Abu? To ki bisu da yadda kika gansu, nima ban sani ba.
A yanzu haka Farfesa ya turo ni ne da wani al’amari mai girma wanda ban san yadda zan yi in shawo kan Innarki ba, don Malam ba matsala bane sai ita din mai tsatstsauran ra’ayi sa rashin kaunar duk wani al’amari daya shafi Baba Sa’idu. Ya turo ni ne da zungureriyar wasika zuwa ga Malam da ita Inna, kan su bada ke in tafi dake, an samar muku makaranta keda su Ifty.
Amma sanin kanki ne wannan ba karamin aiki bane ya hada ni dashi, tunda shima ya buga ya kasa balle ni? Sannan Inna Rabi na ganin mutunci na fiyeda kowa, ina tsoron abinda zai zubar da wannan mutuncin, ya rana na kaunata a zuciyarta. Saidai na gamsu da hujjojin da ya bayar.”
Daidai nan Malam ya karaso ya tadda mu, wani almajirin sa Matt ya rikon masa leda, da alama irin tsira da balanghiga gu da ya saba kawo mana ne duk dare, yana murmushi yace “yaya dai? Wa da ‘yar kanwar shi ana shawara ne?”
Muka yi murmushi dukkanmu tare da sunkuyar da kai kasa. Yace “ku tashi mu shiga gida, bana son zama cikin hasken farin watannan, yana gadar da ciwo”. Muka mike muka shiga gidan gabadaya, shi da Malam suka shige turakar Mallam din, nikuma nayi daki na kwanta.
Inna na bisa sallama tana ta sallah, wannan al’adarta ne na duk daren juma’ah kwana take sallah. Ta kan ce, “wanda ya bari du iya da Kyale-kyalenta ya rudest, ya manta da ambaton Allah da yawa ita tuba a gareshi, haqiqa yana cikin rafkanannu.
Don haka nima ta koya min, har yabi jinin jikina. Sau tari na kan bita muyi ta yi, har sai kafafuna sun sare, yawun bakina ya bushe.
A can dakin Malam me suka ce – me suka ce oho! Was he gari da asuba hi dai naga fuskar Malam babu annuri. Bayan yayi sallar asubah gari yayi Dan shaawa! Haka, misalin karfe shidda na safe ya shigo dakinmu. Inna na bisa sallaya tana lazumi har zuwa lokacin ba ta mike ba, ni kuma ina kwance bisa gado bayan da na ida sallah ban iya na koma ba.
Na dai rufe ido ne kawai cike da tunanin al’amuran rayuwa masu rudarwa, su sanya zuciyar mutum cikin wani hali na rashin sanin tabbas da rashin jin dadin rayuwar ko ta yaya. Ba a rasa ci ba, ba a rasa sha ba, ba a rasa suttura ba amma zukatan al’umma babu dadi. Wannan ita ce hakikanin rayuwar da ke faruwa a cikin gidanmu.