Sashe 2
Girma Ya Fadi Book 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read
A wadannan shekarun, bana damuwa da irin wadannan kalaman nata, kamar yadda bana fahimtar komai a cikinsu, domin hankalin bai isheni ba. Abinda na sani ko kuma na fahimta kawai shine, Inna Rabi rayuwarta daban ce da ta sauran matan Malam, komi baya faranta mata. Haka mafificiyar kaunar da Malam ke gwada mata, bata burgeta.
Tana da wani mummunan kullaci a kan mutane da al’amarinsu, haka gaba dayan rayuwarta cikin kunci take. Sau daya na taba ganin ta tayi dariya a tun tasowa ta, wato ranar da Faruk ya ce ba ta tausayin fatata. Kokarin Malam da Faruk a kullum shine farin cikin Rabi da farin cikina, amma hakan baya hanata zubar da hawaye a yawancin lokuta.
Duk wata kulawa ta uwa da uba kusan in ce na same ta ne daga Ya Faruk, yana sona, yana kulawa dani tamkar ‘yar da ya tsugunna ya haifa. Haka nan komi nawa mai muhimmanci ne a awurin Faruk, shirme ne ko akasi.
Ire-iren mutanen birni da ‘yan boko da kan zo wurin Malam, ba zan iya iyakance alhairan da nake samu daga garesu ba, kullum cikin sabbin kaya, kayan wasa, sabbin dinkuna, kayan zaki da kayan kwalam nake saboda farin jinin da Allah ya yi min. Wasu kuwa kan ce kyawuna ne yake sayo min farin jinin, kowa ya ganni sai ya tanka, ya kuma tambayi Malam game dani, don ko a farcen kafa bamu yi kama ba (komi nawa irin na mahaifiyata ne) tamkar ta yi kaki ta tofar. Amsar da Malam ke bayarwa a kullum shine, nayo Innata ne, wadda take Ba’abziniyar Niger.
Ni kaina na san ni da Inna ta daban ne a cikin gidan, haka muke wal! Sai ka ce tocilan don haske a cikin jama’ar gidan, ko kuma ka ce wata ne a cikin taurari.
Sai dai abin da yake matukar burge ni da rayuwar gidanmu shine, ba za ka taba ganin an nuna wariyar launin fata ba, da ni da su Indo da Hafsisi da su Dubu ke riko, duka su Inna Dubu sun dauke mu daya ne babu banbanci. Sai dai Malam da Ya Faruk a kullum, a komi kuma a ko’ina, su kan nuna nice ‘yar gaban goshinsu.
Halin Innata da irin rayuwar ta kam ya riga ya zame min jiki, har baya damuna, ba ni kadai ba haka duk kishiyoyin ta babu mai nuna damuwa da yanayin rayuwar ta, don in da sabo sun saba. Sai ta wuni ba ta yi magana ba sai bin kowa da ido, haka kullum daren Allah cikin yi min nasihohi da tsoratarwa a kan ZINA take.
Ni a lokacin ma ban san mene ne zinar ba, ban gama tantance ma’anar kalmar zinar ba. Abin da na fahimta kawai shine; zina wani abu ne da Innata ke matukar kyamata, kuma wani abu da Allah ya yi kakkausan hani da shi.
Na alkawarta ma raina zan guje shi, kamar yadda take gargadina a kullum, zan nisanceshi, kamar yadda Allah ya yi hani da shi. Akwai sanda ta ce min,
“Kyauta da ki yi zina, gara mun mutuwarki da rayuwarki”.
Tana da wani mummunan kullaci a kan mutane da al’amarinsu, haka gaba dayan rayuwarta cikin kunci take. Sau daya na taba ganin ta tayi dariya a tun tasowa ta, wato ranar da Faruk ya ce ba ta tausayin fatata. Kokarin Malam da Faruk a kullum shine farin cikin Rabi da farin cikina, amma hakan baya hanata zubar da hawaye a yawancin lokuta.
Duk wata kulawa ta uwa da uba kusan in ce na same ta ne daga Ya Faruk, yana sona, yana kulawa dani tamkar ‘yar da ya tsugunna ya haifa. Haka nan komi nawa mai muhimmanci ne a awurin Faruk, shirme ne ko akasi.
Ire-iren mutanen birni da ‘yan boko da kan zo wurin Malam, ba zan iya iyakance alhairan da nake samu daga garesu ba, kullum cikin sabbin kaya, kayan wasa, sabbin dinkuna, kayan zaki da kayan kwalam nake saboda farin jinin da Allah ya yi min. Wasu kuwa kan ce kyawuna ne yake sayo min farin jinin, kowa ya ganni sai ya tanka, ya kuma tambayi Malam game dani, don ko a farcen kafa bamu yi kama ba (komi nawa irin na mahaifiyata ne) tamkar ta yi kaki ta tofar. Amsar da Malam ke bayarwa a kullum shine, nayo Innata ne, wadda take Ba’abziniyar Niger.
Ni kaina na san ni da Inna ta daban ne a cikin gidan, haka muke wal! Sai ka ce tocilan don haske a cikin jama’ar gidan, ko kuma ka ce wata ne a cikin taurari.
Sai dai abin da yake matukar burge ni da rayuwar gidanmu shine, ba za ka taba ganin an nuna wariyar launin fata ba, da ni da su Indo da Hafsisi da su Dubu ke riko, duka su Inna Dubu sun dauke mu daya ne babu banbanci. Sai dai Malam da Ya Faruk a kullum, a komi kuma a ko’ina, su kan nuna nice ‘yar gaban goshinsu.
Halin Innata da irin rayuwar ta kam ya riga ya zame min jiki, har baya damuna, ba ni kadai ba haka duk kishiyoyin ta babu mai nuna damuwa da yanayin rayuwar ta, don in da sabo sun saba. Sai ta wuni ba ta yi magana ba sai bin kowa da ido, haka kullum daren Allah cikin yi min nasihohi da tsoratarwa a kan ZINA take.
Ni a lokacin ma ban san mene ne zinar ba, ban gama tantance ma’anar kalmar zinar ba. Abin da na fahimta kawai shine; zina wani abu ne da Innata ke matukar kyamata, kuma wani abu da Allah ya yi kakkausan hani da shi.
Na alkawarta ma raina zan guje shi, kamar yadda take gargadina a kullum, zan nisanceshi, kamar yadda Allah ya yi hani da shi. Akwai sanda ta ce min,
“Kyauta da ki yi zina, gara mun mutuwarki da rayuwarki”.