← Book details Babban Yaro Part 2 Complete Hausa Local reading mode
READING PART 34 OF 60

Sashe 34

Babban Yaro Part 2 Complete Hausa · about 8 min read

Sai wajan goma na safe suka tashi, Mimi ta tashi da wani irin zazzab'i mai zafin gaske, a daddafe yayi wanka ga wata irin yunwa yana ji, k'ananun kaya ya sanya a jikinshi, hade da feshe jikinsa da turaran shi na fama, zama yayi gefanta hade da rik'o hannunta a tausashe yace." Momyna pls ki daina kuka don Allah kinji ko." A hankali tace." Ka kira min Asma'u. " Jim yayi minti biyu yace." Wai me zata yi miki ne."? Domin baya kaunar ganin Asma'u a gidan shi, saboda halin da yake shiga a kanta, cikin kuka tace." Ina son in ganta ne." Tab'e baki yayi yace. " kiyi shiru OK yanzu zan sanya doh-doh ys dauko ta shikkenan ko."? Gyada kanta tayi kawai, mik'ewa yayi ya futa daga dakin yana jan tsaki, yunwa kawai yake ji. Futa yayi harabar gidan. Doh-doh Da Rambo na tsaye da sauri suka k'araso gurinsa Umarni ya bawa Doh yaje ya dauko Asma'u, suka tsaya da Rambo suna magana, shima minti biyar ya bar gurin, ya koma cikin gida.
A farlor ya zauna hade da dafe kansa, Rambo ya sanya yaje can sharararn gurin abincin nan na *Mai takobi* ya dauko masa kuku guda d'aya bazai iya jurarar yunwa zai iya biyan shi ko nawa ne, domin ya gaji da yin take away.

*****
Muna zaune a rumfa ni Umma aunt Hauwa ya Aminu Munnu domin itama bata tafi gida ba, karyawa muke yi, ina jinsu suna hira har da Ya Aminu ya sake sai dariya yake yi sosai, ni kuwa ni kadai nasan abunda yake damuna.

Sallama muka ji Ya Aminu ya mike da sauri ya futa minti uku sai gashi ya dawo yana kallona kana ya kalli Umma yace." Yaron Young millionaire ne yazo d'aukar Asma'u wai Mimi tace tazo."
Gabana ya wani irin fad'uwa wani kallo na watsawa Ya Aminu, Umma ta kalleni tare da fadin "Kinji ko sai ki tashi ki shirya watak'ila wani Abu zaki mata."
Haushi da takaici suka kamani nace"Umma kin San Ds yanda muka rabo da ita kuwa jiya."?
Tace"Eh dole ne amma yanzu ai tunda ta kwana zata saba.".
Aunt Hauwa tace"Ga Munnu nan kuje tare da ita, domin ni bazan je ba, kar rashin hankalin yayi yawa.
Gaddama na fara yi Umma ta b'ata fuskarta sosai tace"Yanzu kina son ganin b'acin raina ko."?
Mik'ewa nayi zuciyata babu dad'i na futa daga dakin.

Hijab na zura kan doguwar rigar shaddar dake jikina daga bakin kofa na tsaya tare da fadin"Munnu futo mu tafi. " Umma tace"kije kawai Yanzu aka kirata a waya tazo gida, futa nayi da sauri ba tare da nayi musu sallama ba, Motar na nufa doh ya bude min da sauri na shiga ko kallonshi Banyi ba, yaja motar da sauri muka bar gurin.

Mintuna ashirin ne suka kaimu unguwar ta Jambulo sosai na murtuke fuskata hade da futowa daga motar, Kai tsaye kofar parlor na nufa.
Rambo dake tsaye bakin kofar ya bude min ba tare da nace masa komai ba na shiga.

Yana zaune a farlor da cup din tae a hannunshi yana kurb'a kad'an-kad'an nayi sallama na shiga, kanshi ya d'aga yana kallonta har ta k'araso ciki sosai.

Babu yabo babu fallasa nace." Ina kwana." Shiru yayi yana binta da wani kallo shi ba na tsana ba shi ba na so ba, mugun haushi ya bani ana gaidashi shi kuma yans faman kallon mutane tsaki naja na nufi bedroom din Mimi, wani irin kallo ya bita dashi, wato shi take wa tsaki lallai ne. Cigaba yayi da kurbar tea d'insa hankalinsa kwance.

Halin da naga Mimi a ciki ya d'aga min hankali kuma ta bani tausayi mutuka hawaye na fara yi sosai ta rike hannuna tana kuka take fadin "Asma'u ciwo nake ji a gabana na kasa daga k'afafuna." Cike da takaici nace "Mimi kina nufin kice har ya kwanta dake ko d'aga k'afa babu ki gama warware gajiyar biki."
Rikeni tayi tana yunk'urin tashi zaune tace." Gashi kuwa kingani Asma'u sau hudu yayi min zafi wallahi."! Naji wani irin bakin ciki cikin zuciyata wai wannan guy wane irin Dan iska ne, budurwa ba bazawara ba, kayi sau hudu sai kace wani bunsuru.
Cike da takaici nace"Kinyi ruwan zafi ko."?
Gyada kanta tayi tare da fadin"Sau biyu ma nayi.
Nace"To yanzu kiran me kike min ne."?
"Kawai kizo in ganki." Tafad'a muryar ta na rawa."
Ajiyar zuciya na sauke nace." Tom gani shikkenan ko." Rike ni tayi ni kuma ina tunanin
taimakon Da zan yi mata

Shigowa dakin yayi cikin tafiyar shi ta jarumai ya k'araso kusa damu hannunshi rike da cup din tea dinshi, ya kalleni fuskarsa dauke da murmushi yace." Ina ganin ki had'a mata ruwan zafi ta gasa jikinta sosai tun jiya take kiran ki sunan ki, duk ts hanani sakewa da ita, a matsayin ki na makusanciyar ta, ki tamaka min ki gasa mata jikinta ba sai na dauko dector ba, idan kuma da matsala ta fada miki sai a dauko dector ya duba ta OK."

Ji nayi ina nema in kifa daga zaune zantukan shi suka dinga yi min yawo aka wai in hadawa Mimi ruwan zafi jiya tana kiran sunana me yake nufi guy nan ne." Tambayar kaina nake yi babu me bani amsa.
Zama tayi kusa da k'afafunta tare da janye bargon dake rufe a jikinta, da sauri na mike na bar gurin jin zuciyata tana wani irin bugawa toilet Din na nufa bana kallon gabana.

Tsayuwa nayi cikin toilet din narasa me ma zanyi shikkenan ta tabbata Mimi matar Amjadu tunda gashi har ya kwanta da ita ya raya sunna shikkenan ita dashi sun haramta da junnan su, wasu zafafan hawaye ne suka shiga zubowa daga idonna jingina nayi jiginayi jikin garo ina wani irin kuka me Sosa zuciya lokacin ji naka yi gwara in mutu in huta da wannan bakin cikin.
Motsin bude kofar toilet din naji firgit na dawo hayyacina ina goge fuskata ya shigo toilet din, sauri nayi na juya baya na soma had'a ruwan zafi da na sanyi jikina sai b'ari yake.

Bayanta ya k'ura ido da lumsassan idanun sa, kamar na mashaya sarai ya fahimci kuka take yi tunda ya gan hawayen a fuskar ta tana gogewa, murmushi yayi yana shafa siririn sajan shi, a hankali ya k'arasa har inda take, saura kad'an jikinsu ya had'u, gyaran murya yayi tare da fadin "Jimana."! Tun sanda ya iso kusa dani nake addu'ar Neman tsari dama nasan Neman fitina ne ya sanya aka dauko ni a daga gidanmu, fuskata a mugun hade da juyo k'irjina da nasa suka sad'u hakanan fuska ta da tashi ta had'u dogon hancin shi na tab'a goshina,
Zame wa nake kokarin yi ya babbake gurin, fuskar shi na kalla da tawa fuskar wacce take a mutukar daure!! Wannan d'an iskan murmushin nasa ya saki tare da tsare ni da fitinanun idanuwan sa, da babu d'igon kunya ko kad'an a cikinsu yace." Kukan me kike yi uhumm."? Wani irin masiffafan fleengs naji yana taso min a lokacin sai na fara addu ar neman tsari daga sharrin shi, cike da jarumta kamar ko da yaushe nace." Ina kuka ne kawai saboda rashin imanin da ka gwada akan Mimi Wallahi baka da Imani."!!
'Yar dariya yayi as'usuel ya shafa sumar shi hade da sajan shi, yace." Wane irin rashin Imani humm? Ko ke na samu haka zanwa tunda hakkina ne kuma sadaki na ne, mallakina ne, yanzu ma na kiraki ne kawai ki gasa min amarya ta, zuwa dare idan ta warware in lallab'ata in kwashi gara yanda ya kamata." Cike da iskanci yayi maganar.

Wani irin haushin sa da takaicin sa nake ji a lokacin sai na rasa me zance masa, kawai na buge k'irjinsa da mugun k'arfi na futa daga tsaka insa tare da fad'in"Dan iska kawai."
Mamakin ta yake yi wai d'an iska take kiran shi a kan hakkin shi, ya gano kishi tsagwaron sa a idanunta dama so yake ya tunzurata, babu wata damuwa a tare da shi yace." Ni kam babu mahalukin mutumin da zai kirani da wannan Kalmar a kan HAKKINA, kawai Dan nayi marking love da Matata sai a ce min d'an iska, kin ci albarka cin My Wife Mimi na da sai kin gane kuran ki."
Yana gama maganar shi ya futa daga toilet din ba tare da ya saurari abunda zata ce ba.

Zamewa nayi na zauna dab'as! Kan tayal din dake kasan toilet din na hada kaina da gwiwa ta wani irin kuka ya kufce min Wanda nayi ta kokarin danne shi, kuka nake sosai da sosai ina addu'ar Neman samun sauki daga Allah, wani irin sabon sonshi da kaunar shi naji yana taso min a zuciyata take jikina ya kama rawa duk narasa me zanyi inji dad'i a rayuwa ta.
Motsin bude kofar naji na mike zumbur domin na dauka shine ya dawo sai naga Mimi ta shigo tana bin bango, da sauri naje na kama ta, ita kuma ta dinga bin fuskata da kallo bakinta a bushe tace"Habibty kukan kike yi ko." Babu karya domin ga hawaye ne nan tana gani a kwarmin idona nace" Mimi kukan tausayin ki kawai kawai nake yi." Murmushi kawai tayi min tana fyada kanta, ruwan ha hada mata cike wani baho na zuba detol kad'an a hankali na zaunar da ita ciki. Kara ta k'walla ra tana rike hannuna nace" Mimi ki zauna ki Dade a ciki ZAKIJI dad'i jikin ki." Gyda min kai tayi tana rintse idonta, futa nayi daga toilet din na barta.

Babu kowa a dakin, na hau cire bedshirt din shina duk ga d'igon jini nan, gashi duk ya cukurkude raina babu dad'i ko na kwabo na cire shi hade da aje shi gefa guda, wani na ciro kai kyau na shimfid'a kan bed din, na Ciro mata kaya masu kyau na aje gefan gado, zama nayi ina jiran futowar ta,
Chapter 34 · 0% Book details