Sashe 23
Babban Yaro Part 2 Complete Hausa · about 8 min read
Kawu Yunusa yace." Muma maganar da take tafe damu kenan domin Asma'u taje har gida ta Sanar mana saboda haka tunda taga zata iya shikkenan dama kuma shi yaron Neman auran mutum biyu yazo ita da Mimi saboda haka kan Aminu baza mu bari a rusa wannan auran ba domin mu abun alfarin mu ne, hada jini da Amjadu saboda haka zamu tattashi Aminu."
Wannan shawarar ita ce matsaya Babansu Munnu na tsaye bai ce komai ba sai da suka gama magana yace."Idan babu damuwa Aminu yazo ga Munnubiya na bashi sai a d'aura auran rana daya.
Kawu Idiris yace." Mungode da wannan karamci zamu jira ya dawo hayyacinsa muji ta bakinsa.
4:35 Aminu ya farka masha Allah nuffashin sa ya dawo dai-dai budar bakinsa "Ina Mimi take kar kice min ta mutu Innalillahi wa'ina ilahi raji'un."
Ya fada yana yunk'urin tashi zaune
Dr Yayi saurin mai dashi ya kwantar yana rarrashin sa fafur Aminu yak'i zama dole sai an kaishi gurin Mimi, Dr da kansa ya Dora shi keke saboda jikinsa babu k'wari kai tsaye dakin da Mimi take ya nufa da shi.
Mimi na kwance sambal hancin ta sakale da oxygen idanunta a rufe Aminu ya tsura mata ido zuciyarsa nayi masa zafi wai yanzu shi Mimi take gudu tafi son bare dashi, hak'ika Allah ya jarrabe shi da kaunar ta tun tana 'yar jaririyar ta, Ashe zan Ga wannan ranar ta bakin ciki, wasu zafafan hawaye ya share cikin zuciyar sa yace ."Ya zama Dole in hak'ura dake Mimi domin ko ns aure ki zuciyar ki na can gurin wani bazan samu kulawar da nake so ba."
Wasa-wasa har k'arfe goma na dare Mimi bata farfado ba, likita ya duba ta sosai ya tabbatar tana Raye kawai tayi dogon suma ne, nan ya rarrashin Aminu da ya tada hankalinsa a kan hakan.
Da kyar Aminu ya futo daga d'akin sai yaji duk ya samu sauki ma domin halin da yaga Mimi a ciki ya tsora tashi babu shakka zai iya SADAUKAR da soyayyarsa a kanta domin ta rayu. Wannan shine sahihin so.da wannan tunanin ya futo.
Ya Tarar da tashin hankali a waje Inda Umma ta kasa nutsuwa ta tare wata narse tana share hawaye tana rokonta wai ta fada mata idan Mimi ta mutu shikkenan sai su hak'ura saboda d'azu da Dr ya futo Lokacin su Kawu Yunusa nan yake tambayar sa,lafiyar Aminu yace masa ya dawo dai-dai Ita Mimin ce bata dawo normal ba shine hankalin ta ya tashi .
Aminu yazo ya rike ta zuciyarsa nayi masa rad'ad'i da zugi ga wani irin jiri yana d'ibar muryarsa a shake yace." Kiyi hakuri Mimi lafiyar lau bata mutu ba, yanzu daga gurin ta nake." Umma ta rike hannunsa tana kallonsa cike da tausayi ta bude baki zata yi magana ya katse ta ta hanyar fadin "Umma na hak'ura da Mimi idan shine samun kwanciyar hankalinta na hak'ura ta auri Wanda take so. Umma ta rungume shi tana share hawayen ta tace." Aminu Allah yayi maka albarka Ubangiji Allah ya zab'a maka mafi alkairi a rayuwar ka, nagode da wannan karmanci da kayi min yarona ka fidda ni daga zargin mutane."
Rungume ta yayi tare da tausar zuciyar ta, Ni da aunt Hauwa muka kama ta muka zaunar da ita jikinta sai bari yake. A hankali Ya Aminu yace." Ni zan je gida in kwanta in huta jiri nake ji." Aunt Hauwa tace." Idan kana ganin babu matsala shikkenan. " gyada kansa yayi kawai ya bar gurin yanda yake tafiya zaka San ba shi da cikkakiyar Lafiya.
Tun lokacin da Ya Aminu ya fad'i cewar ya janye maganar auran sa da Mimi naji wani irin sanyi a zuciyata tayi wasai duk wani bacin rai da fargabar da nake ciki naji babu shi. Umma ma na lura ta sauya ta saki jikinta
Munanan zaune har sha biyu babu Wanda yake kokarin kwanciya ko gyangyadi muna sauraren futaw Dr wata narse ce ta futo daga d'akin da Mimi take Fuskata babu yabo babu fallasa tace." Wacece "Asma'u a cikin Ku."? Da sauri nace" Nice." Tace." Kizo maralafiyar nan da kuka kawo na Neman ki. Hamdala Umma tayi tare da fadin"Ta farfado kenan." ? Narse tace "Eh kusan awa biyu da farfadowar ta shine Yanzu tace." Wai a kira mata Asma'u." Umma tace." Maza jeki kiji kome ye ko kara kwantar mata da hankali." Da sauri na bi bayan nurse din.
Mimi na zaune ta jingina da jikin gado kanta a kasa tana wasa da hannunta kamar wata sokuwa ko kuma sabon shigar hauka duk ta sauya, cike da tausayin ta na zauna kusa da ita tare da fadin"Mimi gani menene."?
D'ago kanta tayi hawaye na bin kuncin ta, ta rike hannunwa tamau!! Bakinta na rawa tace." Habbity ya zanyi da rayuwa ta ne."!!!!? Ba kasaifai take kira na da wannan sunan ba, sai muna cikin damuwa da ni da ita.
Hannunta na rike sosai nace." Mimi ba dai *Amjadu* ba."? Shiru tayi min hawaye na zuba a idonta. Murmushi nayi me ciwo nace." Kamar kin aure shi kin gama an gama komai manya ma sun shiga maganar Ya Aminu kuma ya janye maganar auran ki, Yace ki auri Wanda kike so." Na k'arashe maganar fuskata dauke da murmushi na karfin hali.
Hannuna dake damk'e da nata ta matsaye sosai tana gyda kanta,bata CE min komai ba, minti biyu tsakani nace." Kuma d'azu yazo duba ki lokacin kina bacci ya dad'e ma tare da dr duk wasu hidima shine yayi, nima na amunce ya aure mu tare ki kwantar da hankalin ki."
Cikin nauyin baki tace"Nagode Habibty 'yar uwata ta kaina hak'ika kin cika 'yar halak Nagode Asma'u na rasa wata irin zuciya ce dani narasa wace iri ce ni, ki yafe min zuciya ta tafi karfina bazan iya sarrafa ta ba."
Murmushi nayi hade da rike hannunta nace "Ba laifin ki bane Mimi sharrin so ne kawai kowa ma haka tana iya faruwa dashi, kuma kinsan kowa da irin zuciyarsa wani yana da dauriya wani kuma bashi da ita, hakanan wani yana iya sarrafa zuciyar sa, wani kuma zuciyarsa tafi k'arfi sa, kamar ke kenan, hummm!! Yanzu dai magana ta wuce insha Allahu baki da miji sai Amjadu zakiyi rayuwa inuwa guda dashi."
Wata irin ajiyar zuciya ta sauke tare da sakin wani irin murmushi Wanda dashi gwara kuka tace." Asma'u na Dade da sanin cewar *Jad* baya sona nice nake haukana a kanshi, ke yake so inda ke kuma baya gaban ki!! Ki bani shawarar Ya za'ayi na jawo hankalin sa kaina. "
Murmushi nayi ina mamakin Mimi da so ya rufewa ido ashe har suna ta sanya masa wai *Jad* humm!! Sunan kuwa yayi min dad'i. Domin in kara kwantar mata da hankali nace" Mimi ke kike abunki kar ki damu ni nasan da an d'aura aure zai so ki kamar ya mutu zai so ki fiye da yanda Ya Aminu yake son ki, Mimi kina da kyau kina da kira mai d'aukar hankali gaki fara alkyabar mata, babu namjin da zai kauda kansa daga kanki ki kwantar da hankalin ke dai."
Murmushi tayi hade da sunkuyar da kanta har yanzu hannuna guda na rike da nata.nace "Kinga wayar ki ma a hannuna Bari in kira miki shi Ku gaisa ko."?
Bata ce min komai ba, na fara kiran numbar shi, bugu daya ya dauka muryar shi da alamun bacci yace."
*HUSNAH."!* Sai da naji wani irin yarrrr! A jikina jin yanda ya ambaci sunana da ba kowa ne yake kira na dashi ba, ga muryar tayi low sosai kamar me mura. Ajiyar zuciya na sauke babu yabo babu fallasa nace"Ga Mimi za kuyi magana. "
Shiru naji yayi nace ."Hello." Gyaran muryar shi na ji yace." Owk bata wayar." Mimi na mik'awa wayar da murmushi a fuskata, hannunta na rawa ta karb'i wayar tayi sallama da dusashashiyar muryar ta.
Ina jinsa yana amsa mata a sake, yace." Ya jikin naki Momyna."? Tace." Jiki da sauki." Yace." Alhmdullahi ki kwantar da hankalin ki kinji ko duk abunda kike tunanin bazai yi wu ba to zai yi yuwu da izinin Allah idan Allah ya kaddara ke din matata ce Sai ki ga munyi aure, ki daina tashin hankalin ki, Tare da yardar 'yar Uwar ki ni na amunce zan aure Ku a tare ina fatan alkairi a kan haka, daga k'arshe nake ce wa dake ki godewa 'yar Uwar ki, domin tabbas ta sadaukar da nata farin cikin a kanki da samun fi gaban ki hade da lafiyar ki. Momyna hak'ika kin sa'ar 'yar uwa me kyawun zuciya."
Ya karasa maganar tasa cikin nutsuwa.
Ba Mimi ba ni kaina kalaman sa sun yi min dadi kuma naji dadin yabon da yayi min abunda bai tab'a faruwa ba ni dashi, bai tab'a fad'ar alkairina ba sai yau.
Murmushi naga tana yi kunne na kasa sosai ko zan ji abunda yake fada mata Wanda yake sata sakin wannan kayataccan murmushi, babu abunda nake ji daga b'angaran sa saboda ya k'ara yin kasa da muryar sa sosai, ita kanta Mimi sai ta kasa kunne sosai sannan zata ji abunda yake fad'a.
Ji nayi zuciyata nayi min wani irin zafi nayi saurin kauda kaina tare da ambatar innalillahi cikin zuciyata domin ji nayi take wani kunci ya ziyarce ta, zuciyar tawa sai take raya min kamar da akwai wani munafurci a ciki don me yasa zai dinga magana a waya kamar munafuki wannan bayi bane ni a ganina. Maganar da Mimi tayi ce ta dawo dani hayyacina , wayar take mik'o min tare da fadin"Yace." A baki wayar ku yi sallama."
D'aga murya nayi domin yaji nace"Mimi kashe wayar nan don Allah bacci nake ji, tunda dai kun gaisa dashi shikkenan dama haka nake so in sanya zuciyar ki farin ciki, kashe wayar mu kwanta Wallahi nayi bala'in gajiya."
Wannan shawarar ita ce matsaya Babansu Munnu na tsaye bai ce komai ba sai da suka gama magana yace."Idan babu damuwa Aminu yazo ga Munnubiya na bashi sai a d'aura auran rana daya.
Kawu Idiris yace." Mungode da wannan karamci zamu jira ya dawo hayyacinsa muji ta bakinsa.
4:35 Aminu ya farka masha Allah nuffashin sa ya dawo dai-dai budar bakinsa "Ina Mimi take kar kice min ta mutu Innalillahi wa'ina ilahi raji'un."
Ya fada yana yunk'urin tashi zaune
Dr Yayi saurin mai dashi ya kwantar yana rarrashin sa fafur Aminu yak'i zama dole sai an kaishi gurin Mimi, Dr da kansa ya Dora shi keke saboda jikinsa babu k'wari kai tsaye dakin da Mimi take ya nufa da shi.
Mimi na kwance sambal hancin ta sakale da oxygen idanunta a rufe Aminu ya tsura mata ido zuciyarsa nayi masa zafi wai yanzu shi Mimi take gudu tafi son bare dashi, hak'ika Allah ya jarrabe shi da kaunar ta tun tana 'yar jaririyar ta, Ashe zan Ga wannan ranar ta bakin ciki, wasu zafafan hawaye ya share cikin zuciyar sa yace ."Ya zama Dole in hak'ura dake Mimi domin ko ns aure ki zuciyar ki na can gurin wani bazan samu kulawar da nake so ba."
Wasa-wasa har k'arfe goma na dare Mimi bata farfado ba, likita ya duba ta sosai ya tabbatar tana Raye kawai tayi dogon suma ne, nan ya rarrashin Aminu da ya tada hankalinsa a kan hakan.
Da kyar Aminu ya futo daga d'akin sai yaji duk ya samu sauki ma domin halin da yaga Mimi a ciki ya tsora tashi babu shakka zai iya SADAUKAR da soyayyarsa a kanta domin ta rayu. Wannan shine sahihin so.da wannan tunanin ya futo.
Ya Tarar da tashin hankali a waje Inda Umma ta kasa nutsuwa ta tare wata narse tana share hawaye tana rokonta wai ta fada mata idan Mimi ta mutu shikkenan sai su hak'ura saboda d'azu da Dr ya futo Lokacin su Kawu Yunusa nan yake tambayar sa,lafiyar Aminu yace masa ya dawo dai-dai Ita Mimin ce bata dawo normal ba shine hankalin ta ya tashi .
Aminu yazo ya rike ta zuciyarsa nayi masa rad'ad'i da zugi ga wani irin jiri yana d'ibar muryarsa a shake yace." Kiyi hakuri Mimi lafiyar lau bata mutu ba, yanzu daga gurin ta nake." Umma ta rike hannunsa tana kallonsa cike da tausayi ta bude baki zata yi magana ya katse ta ta hanyar fadin "Umma na hak'ura da Mimi idan shine samun kwanciyar hankalinta na hak'ura ta auri Wanda take so. Umma ta rungume shi tana share hawayen ta tace." Aminu Allah yayi maka albarka Ubangiji Allah ya zab'a maka mafi alkairi a rayuwar ka, nagode da wannan karmanci da kayi min yarona ka fidda ni daga zargin mutane."
Rungume ta yayi tare da tausar zuciyar ta, Ni da aunt Hauwa muka kama ta muka zaunar da ita jikinta sai bari yake. A hankali Ya Aminu yace." Ni zan je gida in kwanta in huta jiri nake ji." Aunt Hauwa tace." Idan kana ganin babu matsala shikkenan. " gyada kansa yayi kawai ya bar gurin yanda yake tafiya zaka San ba shi da cikkakiyar Lafiya.
Tun lokacin da Ya Aminu ya fad'i cewar ya janye maganar auran sa da Mimi naji wani irin sanyi a zuciyata tayi wasai duk wani bacin rai da fargabar da nake ciki naji babu shi. Umma ma na lura ta sauya ta saki jikinta
Munanan zaune har sha biyu babu Wanda yake kokarin kwanciya ko gyangyadi muna sauraren futaw Dr wata narse ce ta futo daga d'akin da Mimi take Fuskata babu yabo babu fallasa tace." Wacece "Asma'u a cikin Ku."? Da sauri nace" Nice." Tace." Kizo maralafiyar nan da kuka kawo na Neman ki. Hamdala Umma tayi tare da fadin"Ta farfado kenan." ? Narse tace "Eh kusan awa biyu da farfadowar ta shine Yanzu tace." Wai a kira mata Asma'u." Umma tace." Maza jeki kiji kome ye ko kara kwantar mata da hankali." Da sauri na bi bayan nurse din.
Mimi na zaune ta jingina da jikin gado kanta a kasa tana wasa da hannunta kamar wata sokuwa ko kuma sabon shigar hauka duk ta sauya, cike da tausayin ta na zauna kusa da ita tare da fadin"Mimi gani menene."?
D'ago kanta tayi hawaye na bin kuncin ta, ta rike hannunwa tamau!! Bakinta na rawa tace." Habbity ya zanyi da rayuwa ta ne."!!!!? Ba kasaifai take kira na da wannan sunan ba, sai muna cikin damuwa da ni da ita.
Hannunta na rike sosai nace." Mimi ba dai *Amjadu* ba."? Shiru tayi min hawaye na zuba a idonta. Murmushi nayi me ciwo nace." Kamar kin aure shi kin gama an gama komai manya ma sun shiga maganar Ya Aminu kuma ya janye maganar auran ki, Yace ki auri Wanda kike so." Na k'arashe maganar fuskata dauke da murmushi na karfin hali.
Hannuna dake damk'e da nata ta matsaye sosai tana gyda kanta,bata CE min komai ba, minti biyu tsakani nace." Kuma d'azu yazo duba ki lokacin kina bacci ya dad'e ma tare da dr duk wasu hidima shine yayi, nima na amunce ya aure mu tare ki kwantar da hankalin ki."
Cikin nauyin baki tace"Nagode Habibty 'yar uwata ta kaina hak'ika kin cika 'yar halak Nagode Asma'u na rasa wata irin zuciya ce dani narasa wace iri ce ni, ki yafe min zuciya ta tafi karfina bazan iya sarrafa ta ba."
Murmushi nayi hade da rike hannunta nace "Ba laifin ki bane Mimi sharrin so ne kawai kowa ma haka tana iya faruwa dashi, kuma kinsan kowa da irin zuciyarsa wani yana da dauriya wani kuma bashi da ita, hakanan wani yana iya sarrafa zuciyar sa, wani kuma zuciyarsa tafi k'arfi sa, kamar ke kenan, hummm!! Yanzu dai magana ta wuce insha Allahu baki da miji sai Amjadu zakiyi rayuwa inuwa guda dashi."
Wata irin ajiyar zuciya ta sauke tare da sakin wani irin murmushi Wanda dashi gwara kuka tace." Asma'u na Dade da sanin cewar *Jad* baya sona nice nake haukana a kanshi, ke yake so inda ke kuma baya gaban ki!! Ki bani shawarar Ya za'ayi na jawo hankalin sa kaina. "
Murmushi nayi ina mamakin Mimi da so ya rufewa ido ashe har suna ta sanya masa wai *Jad* humm!! Sunan kuwa yayi min dad'i. Domin in kara kwantar mata da hankali nace" Mimi ke kike abunki kar ki damu ni nasan da an d'aura aure zai so ki kamar ya mutu zai so ki fiye da yanda Ya Aminu yake son ki, Mimi kina da kyau kina da kira mai d'aukar hankali gaki fara alkyabar mata, babu namjin da zai kauda kansa daga kanki ki kwantar da hankalin ke dai."
Murmushi tayi hade da sunkuyar da kanta har yanzu hannuna guda na rike da nata.nace "Kinga wayar ki ma a hannuna Bari in kira miki shi Ku gaisa ko."?
Bata ce min komai ba, na fara kiran numbar shi, bugu daya ya dauka muryar shi da alamun bacci yace."
*HUSNAH."!* Sai da naji wani irin yarrrr! A jikina jin yanda ya ambaci sunana da ba kowa ne yake kira na dashi ba, ga muryar tayi low sosai kamar me mura. Ajiyar zuciya na sauke babu yabo babu fallasa nace"Ga Mimi za kuyi magana. "
Shiru naji yayi nace ."Hello." Gyaran muryar shi na ji yace." Owk bata wayar." Mimi na mik'awa wayar da murmushi a fuskata, hannunta na rawa ta karb'i wayar tayi sallama da dusashashiyar muryar ta.
Ina jinsa yana amsa mata a sake, yace." Ya jikin naki Momyna."? Tace." Jiki da sauki." Yace." Alhmdullahi ki kwantar da hankalin ki kinji ko duk abunda kike tunanin bazai yi wu ba to zai yi yuwu da izinin Allah idan Allah ya kaddara ke din matata ce Sai ki ga munyi aure, ki daina tashin hankalin ki, Tare da yardar 'yar Uwar ki ni na amunce zan aure Ku a tare ina fatan alkairi a kan haka, daga k'arshe nake ce wa dake ki godewa 'yar Uwar ki, domin tabbas ta sadaukar da nata farin cikin a kanki da samun fi gaban ki hade da lafiyar ki. Momyna hak'ika kin sa'ar 'yar uwa me kyawun zuciya."
Ya karasa maganar tasa cikin nutsuwa.
Ba Mimi ba ni kaina kalaman sa sun yi min dadi kuma naji dadin yabon da yayi min abunda bai tab'a faruwa ba ni dashi, bai tab'a fad'ar alkairina ba sai yau.
Murmushi naga tana yi kunne na kasa sosai ko zan ji abunda yake fada mata Wanda yake sata sakin wannan kayataccan murmushi, babu abunda nake ji daga b'angaran sa saboda ya k'ara yin kasa da muryar sa sosai, ita kanta Mimi sai ta kasa kunne sosai sannan zata ji abunda yake fad'a.
Ji nayi zuciyata nayi min wani irin zafi nayi saurin kauda kaina tare da ambatar innalillahi cikin zuciyata domin ji nayi take wani kunci ya ziyarce ta, zuciyar tawa sai take raya min kamar da akwai wani munafurci a ciki don me yasa zai dinga magana a waya kamar munafuki wannan bayi bane ni a ganina. Maganar da Mimi tayi ce ta dawo dani hayyacina , wayar take mik'o min tare da fadin"Yace." A baki wayar ku yi sallama."
D'aga murya nayi domin yaji nace"Mimi kashe wayar nan don Allah bacci nake ji, tunda dai kun gaisa dashi shikkenan dama haka nake so in sanya zuciyar ki farin ciki, kashe wayar mu kwanta Wallahi nayi bala'in gajiya."