Sashe 11
Babban Yaro Part 2 Complete Hausa · about 8 min read
Yace." Ya jin dadin ki Monyna hope komai lafiya Lou."
"Alhmdullahi wallahi."
Tafad'a fuskarta dauke da murmushi
"Ina *Asma'u?*
ya tambaye ta kai tsaye!!! Wata irin fad'uwar gaba taji jin ya baci sunan Asma'u.
Bakinta na rawa tace" Tana gida."
"Owk d'azu mun Dade da yayan Ku a waya ina fatan duk kunji sak'ona ni Amajadu zan aure ku dake da 'yar uwarki Asma'u."
Gyada kanta tayi tace"Ya fada ma Umma."
"Masha Allah." Ya fada da murmushi a fuskar sa, shiru na minti biyu sannan yayi gyaran murya tare da fadin" Shikkenan kije gida sai munyi waya, sai ki kira min *Asma'u* itama muyi zance kamar yanda mukayi dake."
Jiki babu k'wari Mimi ta bude mota ta futa, ya bita da kallo had'e da fadin "Kar ki manta fa ki kashe wayar ki, kafin in kwanta ina son jin muryar ki." Mimi taji wani sanyi ya tsirga mata a zuciyarta murmushi ta saki tare da fadin"Insha Allah."
Hannu ya d'aga mata ta tsallaka titi kana ta shiga layin su.
Umma na zaune a inda take tace"Har ya tafi."? Mimi tace"A'a Asma'u yace." A kira masa." Umma tayi shiru cike da mamaki tace." Asma'u Kuma. " daga Kai Mimi tayi.
Ina kwance a dakin ina jinsu sama-sama, domin bacci ya soma hawa kaina.
Ina jin sanda Umma take fadin "Sai kije ki kira ta tana daki."
Mimi ta shigo dakin hade da tsayawa a kaina tana kiran sunana.
Banza nayi mata.
Tace" nasan dai kina ji don yanzu ba lokacin baccin ki bane, kije Amjadu yana kiran ki."
Mik'ewa zaune nayi nace"Uwar me zanyi masa."
Tace"Idan kinje sai kiji."
Yanda ta fad'i maganar na gane taji zafin zagin da nayi.
Tsaki nayi na koma na kwanta.
Tace.don Allah ki tashi kije babu kyau wulakanci."
Ina daga kwance nace"Kin San Allah Mimi babu inda zanje domin ban ga tsiyar da zan masa ba.
Futa tayi daga dakin.
Can naji Umma na kwala min kira.
Mik'ewa nayi da sauri na futo tsakar gidan INA amsawa
Fuskarta a hade tace "kije kiran da ake miki ko ranki ya b'aci."
Shiru nayi raina a bace
Cikin tsawa tace." Ko bakya ji ne."
Nace" Tom Umma" dakin mu na koma na zurmo hijabina na sallah na futo silafas na zura a kafata na futa.
Tsayuwa nayi a waje ina tunanin ko in lab'e a wani gurin ne. ?
Wata zuciyar tace" kije ki kare masa rashin mutumci tunda yazo unguwar Ku.
Aikuwa tafiya nayi inda nasan zan ganshi
Can na hango motar shi kasancewar ya kunna futular motar.
Ina zuwa gurin na buga motar da k'arfi. Budewa yayi hade da haske fuskata da hasken wayar shi, kalon-kalon muka fara ni dashi. Gani nayi ya kauda kansa yana dariya
Haushi da takaici suka kama ni, sai kace mahaukaciya ya tasa ni a gaba yana dariya. Cike da takaici naja tsaki hade da juyawa da niyyar tafiya, ji nayi an fuzgo min hijabi da k'arfi na fada cikin motar.
Jikinshi ya kwanto kaina ya rufe motar hade da sanya mata security, kallonshi nake a tsorace! Naga fuskarsa a mutukar murtuke Yayi bala'in shan kunu irin Wanda bai tab'a yin irinsa ba,
Ya hasko fuskata sosai da wayar shi, Yana kallona tare da ya mutse fuskar sa.
Kauda kaina nake ganin yadda ya dallare min ido.
Hannunsa guda ya sanya ya shak'o wuyana dake cikin hijabi, Murya k'asa-k'asa yace." Maimata irin zagin da kikayi min a waya jiya." Kifkifta idona kawai nake, ya k'ara shak'e min wuyana hade da d'aga kaina sama sosai, yace"Ko bakya ji ne."?
Da kyar na samu na kakaro magana nace"Sakar mun wuya kar ka kashe ni."
Kin saki yayi sai ma kara damk'e wuyan yayi, hannuna guda na sa ina kokarin b'anb'are hannunsa daga jikin wuyana, ko motsi ya kiyi, wuyana yayi bala'in sagewa, nace"Ka Sakar min wuyan....... Ka tsani Yayi ta hanyar fad'in" Ki maimata irin zagin da kikayi min jiya Zan sake ki."
Babu wasa a cikin maganar sa.
Hawaye na ziraro min nace"Wane irin zagi nayi maka, duk abunda na fada maka gaskiya na fada ciki babu sharri ko kashe ni zakayi sai dai ka kashe ni."
"Very good."!! Ya fad'a yana k'ara bank'are min wuyana sama, cike da mugunta, yace." Na lura da abunda kike so in yi miki ni kuma bazan yi ba, na daina hora ki da abun domin na lura yana miki dad'i shiyasa kike bukatar haduwar mu, Yanzu zanyi miki horo ne irin na gidan prison. " Kasa magana nayi saboda yadda naji mak'o gwarona ya bushe,
Hannu ya sanya ya cire hijab din jikina, na rintse idona saboda nasan babu rigar arziki a jikina wata vest ce mai kama jiki sosai kuma iya kacin ta cibiya ta, domin nayi shirin bacci Mimi ta tashe ni shine kawai na zura hijab din a kai.
Miskilin murmushi ya saki tare da cije lips d'insa yace" Surprise!" Wato dama kin tawo da shirin ki kenan ko."? Shiru nayi masa wasu zafafan hawaye na zubo min a Kumatuna.
Murmushi yayi had'e da shafa sajan shi yace."Wannan karon baza ki samu abunda kike so ba, domin na fara nisanta kaina dake, sai kije gurin wannan saurayin naki mai kama da alade,sai Yayi miki wasa dasu."
Shashshekar kukana ce ta fara futowa fili ina mugun Jin ciwon rashin mutumcin da yake min.
Muryarsa a kaurare! Yace." Wancan karon kin min lafi nace ki bani hakuri kink'i OK wannan karon ki bani hakuri ko kuma in dauki mata ki nag gaba a kanki."
Cikin shashashekar kuka nace"Babu hakurin da zan baka tunda banga laifin da nayi maka, ba, kuma bak'i mai kama da alade da kake magana a kansa gwara min shi sau dubu a kanka, Allah ne ya hallice shi a haka. "
Gyada kansa yayi tare da fad'in"Wannan ke yake damu, kiyi abunda na umarce ki kafin in Riga goma." Cikin daga murya ya fad'i maganar.
Jin nayi shiru ne yasa ya damk'i gashin kaina hade da ja da mugun k'arfi !! Ihu! Na kurma ina fad'in"Zan y......Fuzgar gashin Yayi da k'arfi yace." Oya! Ce ne *Amjadu* kayi hakuri sau goma sha biyu nake so ki fada."
Rintse idona nayi ina cije bakina na fara fad'ar *Amjadu kayi hakuri bazan k'ara ba.!"* sai fa na fad'i haka sau goma sha biyu kamar yanda ya umarce ni.
Babu sauk'i a muryarsa yace." Duk naga shirme da kika rafka naga irin rashin mutumcin da kika tsula a gurin party ku , to ki sani ma Sam! Bakiyi wani kyau ba, kullum kina kiran kanki da Me aji mace mai daraja to duk baki amsa wannan sunan ba, *Momyna* ita za'a kira da wannan sunan."
Shiru yayi na minti biyu ya cigaba da cewa "Momyna ita yafi dacewar na aura a tsakanin Ku, to kuma sai d'azu wanki Aminu yake rokona kan in hada in aure Ku gaba d'aya, cewar kin tayar da hankalin ki, ke ni kadai kike so, hake ko ba haka bane."? Kallonsa nayi cike da mamaki anya Ya Aminu zai fada masa haka.? Wata zuciyar tace" Tsaf Ya Aminu zai iya fada masa haka saboda daman ba shiri kuke dashi ba."
A d'age na kalleshi ina ya mutse fuskata nace"Sai dai Mimi don da ita kuka fi dacewa amma ni ko maza sun k'are bana jin zan aure ka gwara in k'are rayuwata a haka."
Miskilin murmushi yayi bai ce komai ba ya sake ni, hijabina na dauka ina kokarin sanyawa naga ya tada motar nace"Ina zaka kaini."? Ko kallo ban ishe shi ba, ya figi motar da gudu.!
Da sauri na sanya hannu guda na rike sitiyarin motar murya ta na rawa nace"Ka mayar dani gida don girman Allah." Ko kallona bai yi ba, ya cigaba da fafura gudu, kuka sosai na sanya tsoro ya shige ni ganin fuskarsa murtuk!! Nace"Wai me nayi maka ne kake kokarin wulakantani ? Ita Mimi meya sa baka yi mata abunda kake min. " Shiru babu Amsa, yanzu tsoron gida nake da tsoron dukan da Yaya Aminu zai yi min.
Hannunsa na rike tamau! Ina rokanshi motar ta fara gargada! A fusace! Ya fuzge hannuna had'e da yarfa min mari." Cike da mamaki na dafe kuncina ina kallonsa... Da Jan ido ya kalle ni tare da fad'in"Ki shiga hankalin ki."
Shiru nayi tsoro yana shigata.
Gudu yake sosai kan kwalta, naga mun wuce Jambulo wajan gidan shi ya mik'e titin BUK bakina na rawa nace"Kayi hakuri." Hankalinsa na kan driving ki kallona bai yi ba.
Rimin Gata muka shiga sosai, yayi parking dai-dai wani k'aton gidan mai
Haske ko ina jama'a na ta shiga da motocin su Suna shan mai.
Da sauri naga wani mai aikacin ya nufo mu jikinsa sanye da Uniporm orange da tambarin sunan mai gidan mai yana k'araso wa na ga jikinsa rigarsa an sanya *A&A Amjadu Mai nasara feturolium* nace Ashe har gidan mai ne dashi, cikin turanci naji suna maganar Sam ban fuskanci komai ba na dai ga mutumin ya juya ya tafi da sauri!
Minti biyar sai ga mutumin shida wani, sai da suka k'araso sannan naso na gane wanene. Gaba na ne ya fad'i ganin Abokin Shamsu wato Abba gana, yayi tsuru-tsuru,
Bude kofar motar Yayi hade da umar tarsa ya shiga
Abba gana ya shiga motar ba tare da gaddama ba. Shi kuma ma'aikacin ya koma gurin akinshi
Juyo wa yayi yana kallonsa, muryarsa babu wasa yace." Malam meye sunan ka? Kuma meye ya kawo ka wannan jahar."?
Abba yace." Sunana Abba Gana ni mutumin mai duguri ne, yau sati na biyu a jahar kano, Nazo Neman kudi."
"Alhmdullahi wallahi."
Tafad'a fuskarta dauke da murmushi
"Ina *Asma'u?*
ya tambaye ta kai tsaye!!! Wata irin fad'uwar gaba taji jin ya baci sunan Asma'u.
Bakinta na rawa tace" Tana gida."
"Owk d'azu mun Dade da yayan Ku a waya ina fatan duk kunji sak'ona ni Amajadu zan aure ku dake da 'yar uwarki Asma'u."
Gyada kanta tayi tace"Ya fada ma Umma."
"Masha Allah." Ya fada da murmushi a fuskar sa, shiru na minti biyu sannan yayi gyaran murya tare da fadin" Shikkenan kije gida sai munyi waya, sai ki kira min *Asma'u* itama muyi zance kamar yanda mukayi dake."
Jiki babu k'wari Mimi ta bude mota ta futa, ya bita da kallo had'e da fadin "Kar ki manta fa ki kashe wayar ki, kafin in kwanta ina son jin muryar ki." Mimi taji wani sanyi ya tsirga mata a zuciyarta murmushi ta saki tare da fadin"Insha Allah."
Hannu ya d'aga mata ta tsallaka titi kana ta shiga layin su.
Umma na zaune a inda take tace"Har ya tafi."? Mimi tace"A'a Asma'u yace." A kira masa." Umma tayi shiru cike da mamaki tace." Asma'u Kuma. " daga Kai Mimi tayi.
Ina kwance a dakin ina jinsu sama-sama, domin bacci ya soma hawa kaina.
Ina jin sanda Umma take fadin "Sai kije ki kira ta tana daki."
Mimi ta shigo dakin hade da tsayawa a kaina tana kiran sunana.
Banza nayi mata.
Tace" nasan dai kina ji don yanzu ba lokacin baccin ki bane, kije Amjadu yana kiran ki."
Mik'ewa zaune nayi nace"Uwar me zanyi masa."
Tace"Idan kinje sai kiji."
Yanda ta fad'i maganar na gane taji zafin zagin da nayi.
Tsaki nayi na koma na kwanta.
Tace.don Allah ki tashi kije babu kyau wulakanci."
Ina daga kwance nace"Kin San Allah Mimi babu inda zanje domin ban ga tsiyar da zan masa ba.
Futa tayi daga dakin.
Can naji Umma na kwala min kira.
Mik'ewa nayi da sauri na futo tsakar gidan INA amsawa
Fuskarta a hade tace "kije kiran da ake miki ko ranki ya b'aci."
Shiru nayi raina a bace
Cikin tsawa tace." Ko bakya ji ne."
Nace" Tom Umma" dakin mu na koma na zurmo hijabina na sallah na futo silafas na zura a kafata na futa.
Tsayuwa nayi a waje ina tunanin ko in lab'e a wani gurin ne. ?
Wata zuciyar tace" kije ki kare masa rashin mutumci tunda yazo unguwar Ku.
Aikuwa tafiya nayi inda nasan zan ganshi
Can na hango motar shi kasancewar ya kunna futular motar.
Ina zuwa gurin na buga motar da k'arfi. Budewa yayi hade da haske fuskata da hasken wayar shi, kalon-kalon muka fara ni dashi. Gani nayi ya kauda kansa yana dariya
Haushi da takaici suka kama ni, sai kace mahaukaciya ya tasa ni a gaba yana dariya. Cike da takaici naja tsaki hade da juyawa da niyyar tafiya, ji nayi an fuzgo min hijabi da k'arfi na fada cikin motar.
Jikinshi ya kwanto kaina ya rufe motar hade da sanya mata security, kallonshi nake a tsorace! Naga fuskarsa a mutukar murtuke Yayi bala'in shan kunu irin Wanda bai tab'a yin irinsa ba,
Ya hasko fuskata sosai da wayar shi, Yana kallona tare da ya mutse fuskar sa.
Kauda kaina nake ganin yadda ya dallare min ido.
Hannunsa guda ya sanya ya shak'o wuyana dake cikin hijabi, Murya k'asa-k'asa yace." Maimata irin zagin da kikayi min a waya jiya." Kifkifta idona kawai nake, ya k'ara shak'e min wuyana hade da d'aga kaina sama sosai, yace"Ko bakya ji ne."?
Da kyar na samu na kakaro magana nace"Sakar mun wuya kar ka kashe ni."
Kin saki yayi sai ma kara damk'e wuyan yayi, hannuna guda na sa ina kokarin b'anb'are hannunsa daga jikin wuyana, ko motsi ya kiyi, wuyana yayi bala'in sagewa, nace"Ka Sakar min wuyan....... Ka tsani Yayi ta hanyar fad'in" Ki maimata irin zagin da kikayi min jiya Zan sake ki."
Babu wasa a cikin maganar sa.
Hawaye na ziraro min nace"Wane irin zagi nayi maka, duk abunda na fada maka gaskiya na fada ciki babu sharri ko kashe ni zakayi sai dai ka kashe ni."
"Very good."!! Ya fad'a yana k'ara bank'are min wuyana sama, cike da mugunta, yace." Na lura da abunda kike so in yi miki ni kuma bazan yi ba, na daina hora ki da abun domin na lura yana miki dad'i shiyasa kike bukatar haduwar mu, Yanzu zanyi miki horo ne irin na gidan prison. " Kasa magana nayi saboda yadda naji mak'o gwarona ya bushe,
Hannu ya sanya ya cire hijab din jikina, na rintse idona saboda nasan babu rigar arziki a jikina wata vest ce mai kama jiki sosai kuma iya kacin ta cibiya ta, domin nayi shirin bacci Mimi ta tashe ni shine kawai na zura hijab din a kai.
Miskilin murmushi ya saki tare da cije lips d'insa yace" Surprise!" Wato dama kin tawo da shirin ki kenan ko."? Shiru nayi masa wasu zafafan hawaye na zubo min a Kumatuna.
Murmushi yayi had'e da shafa sajan shi yace."Wannan karon baza ki samu abunda kike so ba, domin na fara nisanta kaina dake, sai kije gurin wannan saurayin naki mai kama da alade,sai Yayi miki wasa dasu."
Shashshekar kukana ce ta fara futowa fili ina mugun Jin ciwon rashin mutumcin da yake min.
Muryarsa a kaurare! Yace." Wancan karon kin min lafi nace ki bani hakuri kink'i OK wannan karon ki bani hakuri ko kuma in dauki mata ki nag gaba a kanki."
Cikin shashashekar kuka nace"Babu hakurin da zan baka tunda banga laifin da nayi maka, ba, kuma bak'i mai kama da alade da kake magana a kansa gwara min shi sau dubu a kanka, Allah ne ya hallice shi a haka. "
Gyada kansa yayi tare da fad'in"Wannan ke yake damu, kiyi abunda na umarce ki kafin in Riga goma." Cikin daga murya ya fad'i maganar.
Jin nayi shiru ne yasa ya damk'i gashin kaina hade da ja da mugun k'arfi !! Ihu! Na kurma ina fad'in"Zan y......Fuzgar gashin Yayi da k'arfi yace." Oya! Ce ne *Amjadu* kayi hakuri sau goma sha biyu nake so ki fada."
Rintse idona nayi ina cije bakina na fara fad'ar *Amjadu kayi hakuri bazan k'ara ba.!"* sai fa na fad'i haka sau goma sha biyu kamar yanda ya umarce ni.
Babu sauk'i a muryarsa yace." Duk naga shirme da kika rafka naga irin rashin mutumcin da kika tsula a gurin party ku , to ki sani ma Sam! Bakiyi wani kyau ba, kullum kina kiran kanki da Me aji mace mai daraja to duk baki amsa wannan sunan ba, *Momyna* ita za'a kira da wannan sunan."
Shiru yayi na minti biyu ya cigaba da cewa "Momyna ita yafi dacewar na aura a tsakanin Ku, to kuma sai d'azu wanki Aminu yake rokona kan in hada in aure Ku gaba d'aya, cewar kin tayar da hankalin ki, ke ni kadai kike so, hake ko ba haka bane."? Kallonsa nayi cike da mamaki anya Ya Aminu zai fada masa haka.? Wata zuciyar tace" Tsaf Ya Aminu zai iya fada masa haka saboda daman ba shiri kuke dashi ba."
A d'age na kalleshi ina ya mutse fuskata nace"Sai dai Mimi don da ita kuka fi dacewa amma ni ko maza sun k'are bana jin zan aure ka gwara in k'are rayuwata a haka."
Miskilin murmushi yayi bai ce komai ba ya sake ni, hijabina na dauka ina kokarin sanyawa naga ya tada motar nace"Ina zaka kaini."? Ko kallo ban ishe shi ba, ya figi motar da gudu.!
Da sauri na sanya hannu guda na rike sitiyarin motar murya ta na rawa nace"Ka mayar dani gida don girman Allah." Ko kallona bai yi ba, ya cigaba da fafura gudu, kuka sosai na sanya tsoro ya shige ni ganin fuskarsa murtuk!! Nace"Wai me nayi maka ne kake kokarin wulakantani ? Ita Mimi meya sa baka yi mata abunda kake min. " Shiru babu Amsa, yanzu tsoron gida nake da tsoron dukan da Yaya Aminu zai yi min.
Hannunsa na rike tamau! Ina rokanshi motar ta fara gargada! A fusace! Ya fuzge hannuna had'e da yarfa min mari." Cike da mamaki na dafe kuncina ina kallonsa... Da Jan ido ya kalle ni tare da fad'in"Ki shiga hankalin ki."
Shiru nayi tsoro yana shigata.
Gudu yake sosai kan kwalta, naga mun wuce Jambulo wajan gidan shi ya mik'e titin BUK bakina na rawa nace"Kayi hakuri." Hankalinsa na kan driving ki kallona bai yi ba.
Rimin Gata muka shiga sosai, yayi parking dai-dai wani k'aton gidan mai
Haske ko ina jama'a na ta shiga da motocin su Suna shan mai.
Da sauri naga wani mai aikacin ya nufo mu jikinsa sanye da Uniporm orange da tambarin sunan mai gidan mai yana k'araso wa na ga jikinsa rigarsa an sanya *A&A Amjadu Mai nasara feturolium* nace Ashe har gidan mai ne dashi, cikin turanci naji suna maganar Sam ban fuskanci komai ba na dai ga mutumin ya juya ya tafi da sauri!
Minti biyar sai ga mutumin shida wani, sai da suka k'araso sannan naso na gane wanene. Gaba na ne ya fad'i ganin Abokin Shamsu wato Abba gana, yayi tsuru-tsuru,
Bude kofar motar Yayi hade da umar tarsa ya shiga
Abba gana ya shiga motar ba tare da gaddama ba. Shi kuma ma'aikacin ya koma gurin akinshi
Juyo wa yayi yana kallonsa, muryarsa babu wasa yace." Malam meye sunan ka? Kuma meye ya kawo ka wannan jahar."?
Abba yace." Sunana Abba Gana ni mutumin mai duguri ne, yau sati na biyu a jahar kano, Nazo Neman kudi."