Sashe 6
Zarrah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mal Husaini ne ya shiga ciki ya sanar da matansa cewa zaa shigo ganin gda me tankade ta tashi me dakama ta miqe sukayi daki Inna ce dama tana daki a zaune tana lazumi shigowa sukayi suna duba gdan a zahirin gdan Babu uwar da Aseem zaiyi dashi Amma da suka gama dubawa sai ya dubi Zahran yace masa “ina ganin kamar gurin zaiyi ai ko?" Sarai Zahran yasan me yake nufi shikuma sai yace “dadai an nemi Wanda yafi wannan gsky shanun zasu takura" dafashi yayi yace “kada ka damu fashe dakunan zaayi daki biyun nan kawai zaa bari saboda me gadi da abincin dabbobi" da wannan suka juya zasu fita suna Shirin fita kyawawan yammatan na sawo Kai Dijangala ce a gaba sai Zabba'u ita kuwa gwanar ta cake a qofar gda Laila sarkin soyayya ita da Sadiqun ta suna bawa fure ruwa ai suna fitowa tana dago Kai suka hada ido ba itaba shima Saida yaji gabansa ya fadi ya kasa dauke ido daga kanta dake dariya takeyi yanzun sabanin duk haduwar da sukeyi dashi yau saiyaga tayi wani haske tayi kyau kyawawan haqoranta ya zubawa ido da akayi musu kwalliya da siririyar wushirya.
Ganin fitowarsu daga gdansu yasata saurin tsuke fuska kamar ba itace take dariya ba ta kawar dakai daga kallon da sukewa juna ita da Aseem din, sosai Sadiqu ya lura da sauyin nata don haka ya dubeta.
Yace “ya akayine jarumar Mata?" Ajiyar numfashi tayi tace “meye ya kawoshi gdanmu?" Da rashin fahimta yace “wafa?" Duban Aseem tayi da ya juya baya jikin motarsa yana waya tace “wancan Mara mutumcin Mana shine fah mutumin da nake baka lbrn na fashewa qafa ko qarata ya kawo gda gurin Mal tab aikuwa zan daku shikuma zai ragargazu Dan wlh hayar tantiran hayin qwari zanyi su rugurgujeshi.
Dariya Sadiqu yakeyi Mata domin ya lura gabadayanta a tsorace take tsinkayo muryar Mal tayi Yana qwala Mata Kira “Ma'ulele ke Ma'u bakijina ne bakiga mutane ba dan qaniyarki irin tarbiyyar da gyatumarki tayi Miki kenan?" Sumsum ta nufi gurinsu duk a razane take a rusuna tace “ina yininku" Zahran ne da Mal Bala suka amsa shikuwa gogan kallonta kawai yakeyi Mal Bala yace “Mal nayi nayi dakai ka bani daya cikin yammatannan naka kaqi da tuni baba nakece maka ga Ma'u ma ta girma abinta" tsuke fuska Mal Husaini yayi yace “yo Banda abinka yaro ai sai yaro kaga wancan kafirin yaron da qaton Kai shine ya zamemin alaqaqai nayi nayi na rabasu sunqi rabuwa harma na hqr basa zanyi suje su qarata"
Dagowa Aseem yayi yace “wai itama wannan din taka ce Baba?" Murmushi yayi yana sosa qeya yace “wlh kagansu Nan kamar yar maraqan shanu haka akayita jeramin su harsu uku gasunan kansu daya ita wannan itace qaramarsu shekararta sha shidda sabodasu nema zan sayar da gdannan" Jinjina Kai yayi cikin jin dadi yana hango nasara yace “a aikuwa ba ayi haka ba kasai da gda baba kaida kake da Yaya Mata kabar gdanka kawai" da sauri ya dubeshi yace “inbar gda fah kace Alh waye zaiyimin auren yayan?" Murmushi Aseem yayi ya bude motarsa ya bude dashboard ya dauka raffers ta dari biyar biyar guda biyu ya bashi yace “karka damu baba ka riqe wannan gobe insha Allahu zan dawo ai kamarka kanada wadannan kyawawan yammatan ba abarka ka tozarta ba" sake miqa Masa wata reffer yayi yace a rabawa matan gdan wannan anan suka qyale Mal Husaini sake da baki da kudi a hannunsa suka dauki Mal Bala suka tafi a mota Aseem ya dubi Mal Bala yace “yarinyar nan data gaishemu ta fanshi mahaifinta indai zai bani auranta na rantse zanyi Masa komai da yake buqata na hidimar aurensu tun daga satin farko har ranar da zaa gama biki ka sameshi ka fada Masa idan ya amince har gdanma zan gyara Masa"..........
[20/06 4:27 pm] Oum Hairan: *ZARRAH*
_Tare da Alƙalamin_
*_Oum Hairan_*
_Bismillahir Rahamanir Rahim_
_Free Page 11-12_
*_Wattpad realfauzahtasiu_*
Telegram
👇
https://t.me/joinchat/Gdtmu0TgTHu66CF7
______________________________
______________________________
Tunda suka tafi sukabar Asma'u da sakakken baki kallon da Aseem yakeyi Mata ita da Sadiqu shine yafi Bata mamaki da Kuma dalilin zuwansu gdansu ganin ya damqawa Mal Husaini kudine yasata sake maida hankalinsu garesu amma sai taga ya dubeta yayi murmushi yaja motarsa sunbar Mal da kallon kudi cikin mamaki.
Mal Husaini na dagowa suka hada ido da Asma'u yayi saurin sanya kudin cikin hularsa tare da watsa Mata daquwa tayi saurin kawar dakai sukaci gaba da tsinkar furensu ita da Sadiqun ta Saida aka Kira magariba sukayi sallama ya nufi masallaci ita Kuma ta shiga gda ta dauki buta ta shige bayi ta Kama ruwa ta fito ta daura alwala daidai lkcn da taji Mal Husaini na cewa “ni Babu ruwana da inda Zaki Amina gdane saidashi zanyi dole kowacce ta nemi inda zata zauna kafin ayi bikin yarannan ku koma qauye ba Saida nace kada ku kuskura ku haifi Mata ba ku masu kunne qashi kuka haifesu ai gashinan basu kawo kudi ba sun kwamushe muku naku" cafkar kunnen Asma'u yayi yace “ja'ira da kanta tunna zuwa duniya saura naji kince wani Abu baki kamar gdan tsutsa tana tafe kamar allura" itadai tana samu ya sakar Mata kunne sumsum ta shige daki ta tayar da sallah tare da jan bakinta ta tsuke Abu daya ta iya tambaya shine meye ya kawo baqin gdansu? Inna tace Mata. Masu siyan gdansu ne daga haka tayi shiru da bakinta saboda batason subutar baki tasa tayi wata magana don Bata kuskura ta fadawa Inna tsiyar da tayiwa Aseem Shaheed ba.
Kwana Asma tayi tana tunanin dalilin da yasa Aseem yakeson siyan gdansu, a daren taci alwashin indai Allah ya hadasu gobe a hanyar makaranta sai taci mutuncinsa yanda zaiji bama ya sha'awar siyan gdan nasu, aikuwa tun asuba ta shirya taja ta zauna tana jiran lkc bakwai daidai ta fice daga gdansu ta nufi gdansu Jiddah suka dunguma suka tafi tana bawa jiddah labarin abinda ya faru jiya na zuwan Aseem gdansu a matsayin Wanda zaisai gdan zaiyi kiwon shanu"
Dariya sosai Jiddah tayi tace “kin gamu da qarfen qafa me wuyar kwancewa wato gayen nan ya shiryawa wasan so yake ya qure malejinki ya wulaqantaki Kinga idan ya siye gdanku ko haya ya baku ai babanku ya koma qarqashinsa balle ma tashinku zaiyi a wulaqance ya zuba shanu a gdan Kinga ya nuna Miki rayuwar shanunsa tafi taku muhimmanci. Nifa dama bangano Miki nasara a buga wasa da wannan mutumin ba da ganinsa kinsan yaci yatada Kai zai iya ramawa wulaqancin da zakiyi Masa ta duk inda yaso gara dai yan gujaru gujarun da muke tsokana Basu da yanda zasuyi damu sai tsaki sai harara"
Har sukaje makarantar Allah be hadasu dashi ba haka ta rinqa Allah Allah a tashi nanma Basu gamu ba taji haushi sosai so batada yanda zatayi dole ta hqr tana zuwa suka nufi islamiyya sai yamma suka dawo liqis dake laraba ce sunyi hadda a dakin zaure suka tarar da Mal Husaini da Mal Bala suna tattaunawa Mal Husaini sai dariya yakesu suka durqushe suka gaishesu da fara'a Mal Bala ya amsa inda Mal Husaini yace “Ina Ma'ulelena zonan dan qaniyarki" gabanta ya fadi tunda dama a tsorace take tana jiran abinda zaije ya dawo.
Matsawa tayi a darare ta zauna tana barin jiki don tasan ba wuya bane Mal ya maketa ba gyaran murya yayi yace “Ina kike Asma'ul Husnah?" Ajiyar zuciya tayi tace “gani Mal" Jinjina Kai yayi yace “yawwa Masha Allah dama wani umarnin gaggawa zan baki Kinga dai a yanda kuka taso a wahale a talauce to ke ki godewa Allah yasoki da arziqi yayi miki ludufi da ludufin da yakewa duk Wanda yaso cikin bayinsa jiya anzo ganin gida Ashe rabon aganki ne dan farin yaron nan Alhajin Birni eh wlh tallahi shine dai bayan sunga gda kinje kin gaishesu yagani yakeso harma yayimin alqawarin idan na bashi aurenki zai barmin gdana Kuma zaiyimin komai na auren Dijangala da Zabba'u keko yace ki cokali bashi buqata, kinji fah inda arziqi yake"
Tunda ya fara mgnr ta kafesa da ido cikin mugun tsoro da kaduwa ta gane waye yake nufi domin Zahran ba fari bane Aseem ne fari Anna sai tace “wa...waikace Mal Sadiqun fah?" Wata uwar harara ya buga Mata yace “Sadiqun0 ubanki yo ko Laminu ne uban Sadiqu ya dawo duniya ai bazai hanani cin wannan arziqin ba ke nifa bama shawara nake daku ba dagake har uwarki dama na dauka ke dake kin shafi zamani zakiba da hadin Kai to kema naga qwalluwar yar baqin ciki ce saboda haka tashi ware kauce karna makeki sauna kawai wadda arziqi ke binta tsiya ke dawo da ita baya"
Yana fadin haka ya miqe abinda yasata miqewa itama da gudu tayi cikin gdan tana rushewa da kuka tana cewa “wlh baa isaba bazaa taba cutata a hadani da wannan shegen azzalumin mutumin ba ai bani kadai aka Haifa a gdanba abashi wata Mana saini saboda an rainamin hankali...." Jin takun sawayen Mal Husaini yasata shigewa qarqashin gadon qarfen Inna tana kuka ya shigo dakin yana huci Yana cewa “kajimin mutane yan baqin ciki arziqi yazomin har gda Allah ya amsa addu'a ta Nima nakusa hutawa shine zakuyimin baqin ciki tabdi ai wlh baku isaba wannan aure me hanashi saidai mutuwa idan ma mutuwa zakiyi saidai ki mutu ja'irar yarinya kina tafe kamar ki karye saboda rama yo kika sake kika auri Wannan Dan gadon talaucin da ubansa tunda nasanshi da tàgiya daya nasanshi basai kin qwammace wannan makauniyar uwar taki barinki tayi ba"
Harya gama sababinsa ya fita Inna batace komai ba sai bayan ya fitane Asma'u ta fito tanata shassheqar kuka Inna tace “wai waye wannan ne daga zuwa Mal ya aminta dashi Babu binkice Babu komi?" Nan Asma'u ta yiwa Inna bayani Inna ta saki salati da sallalami tare da yiwa Allah kirari tace “naga takaina ni aminatu dama akan wannan kwasasshen mutumin Mal yacimin mutunci har Yana cimin alwashin aure Babu fashi aikuwa da fashi don baza'ayi wannan son zuciyar dani ba yaro shekara da shekaru Yana wahala Rana tsaka saboda son abin duniya Mal ya rufe ido yana cima mutane mutumci ai bake kadai ya haifaba yabasa wata Amma bake ba"
Ganin fitowarsu daga gdansu yasata saurin tsuke fuska kamar ba itace take dariya ba ta kawar dakai daga kallon da sukewa juna ita da Aseem din, sosai Sadiqu ya lura da sauyin nata don haka ya dubeta.
Yace “ya akayine jarumar Mata?" Ajiyar numfashi tayi tace “meye ya kawoshi gdanmu?" Da rashin fahimta yace “wafa?" Duban Aseem tayi da ya juya baya jikin motarsa yana waya tace “wancan Mara mutumcin Mana shine fah mutumin da nake baka lbrn na fashewa qafa ko qarata ya kawo gda gurin Mal tab aikuwa zan daku shikuma zai ragargazu Dan wlh hayar tantiran hayin qwari zanyi su rugurgujeshi.
Dariya Sadiqu yakeyi Mata domin ya lura gabadayanta a tsorace take tsinkayo muryar Mal tayi Yana qwala Mata Kira “Ma'ulele ke Ma'u bakijina ne bakiga mutane ba dan qaniyarki irin tarbiyyar da gyatumarki tayi Miki kenan?" Sumsum ta nufi gurinsu duk a razane take a rusuna tace “ina yininku" Zahran ne da Mal Bala suka amsa shikuwa gogan kallonta kawai yakeyi Mal Bala yace “Mal nayi nayi dakai ka bani daya cikin yammatannan naka kaqi da tuni baba nakece maka ga Ma'u ma ta girma abinta" tsuke fuska Mal Husaini yayi yace “yo Banda abinka yaro ai sai yaro kaga wancan kafirin yaron da qaton Kai shine ya zamemin alaqaqai nayi nayi na rabasu sunqi rabuwa harma na hqr basa zanyi suje su qarata"
Dagowa Aseem yayi yace “wai itama wannan din taka ce Baba?" Murmushi yayi yana sosa qeya yace “wlh kagansu Nan kamar yar maraqan shanu haka akayita jeramin su harsu uku gasunan kansu daya ita wannan itace qaramarsu shekararta sha shidda sabodasu nema zan sayar da gdannan" Jinjina Kai yayi cikin jin dadi yana hango nasara yace “a aikuwa ba ayi haka ba kasai da gda baba kaida kake da Yaya Mata kabar gdanka kawai" da sauri ya dubeshi yace “inbar gda fah kace Alh waye zaiyimin auren yayan?" Murmushi Aseem yayi ya bude motarsa ya bude dashboard ya dauka raffers ta dari biyar biyar guda biyu ya bashi yace “karka damu baba ka riqe wannan gobe insha Allahu zan dawo ai kamarka kanada wadannan kyawawan yammatan ba abarka ka tozarta ba" sake miqa Masa wata reffer yayi yace a rabawa matan gdan wannan anan suka qyale Mal Husaini sake da baki da kudi a hannunsa suka dauki Mal Bala suka tafi a mota Aseem ya dubi Mal Bala yace “yarinyar nan data gaishemu ta fanshi mahaifinta indai zai bani auranta na rantse zanyi Masa komai da yake buqata na hidimar aurensu tun daga satin farko har ranar da zaa gama biki ka sameshi ka fada Masa idan ya amince har gdanma zan gyara Masa"..........
[20/06 4:27 pm] Oum Hairan: *ZARRAH*
_Tare da Alƙalamin_
*_Oum Hairan_*
_Bismillahir Rahamanir Rahim_
_Free Page 11-12_
*_Wattpad realfauzahtasiu_*
Telegram
👇
https://t.me/joinchat/Gdtmu0TgTHu66CF7
______________________________
______________________________
Tunda suka tafi sukabar Asma'u da sakakken baki kallon da Aseem yakeyi Mata ita da Sadiqu shine yafi Bata mamaki da Kuma dalilin zuwansu gdansu ganin ya damqawa Mal Husaini kudine yasata sake maida hankalinsu garesu amma sai taga ya dubeta yayi murmushi yaja motarsa sunbar Mal da kallon kudi cikin mamaki.
Mal Husaini na dagowa suka hada ido da Asma'u yayi saurin sanya kudin cikin hularsa tare da watsa Mata daquwa tayi saurin kawar dakai sukaci gaba da tsinkar furensu ita da Sadiqun ta Saida aka Kira magariba sukayi sallama ya nufi masallaci ita Kuma ta shiga gda ta dauki buta ta shige bayi ta Kama ruwa ta fito ta daura alwala daidai lkcn da taji Mal Husaini na cewa “ni Babu ruwana da inda Zaki Amina gdane saidashi zanyi dole kowacce ta nemi inda zata zauna kafin ayi bikin yarannan ku koma qauye ba Saida nace kada ku kuskura ku haifi Mata ba ku masu kunne qashi kuka haifesu ai gashinan basu kawo kudi ba sun kwamushe muku naku" cafkar kunnen Asma'u yayi yace “ja'ira da kanta tunna zuwa duniya saura naji kince wani Abu baki kamar gdan tsutsa tana tafe kamar allura" itadai tana samu ya sakar Mata kunne sumsum ta shige daki ta tayar da sallah tare da jan bakinta ta tsuke Abu daya ta iya tambaya shine meye ya kawo baqin gdansu? Inna tace Mata. Masu siyan gdansu ne daga haka tayi shiru da bakinta saboda batason subutar baki tasa tayi wata magana don Bata kuskura ta fadawa Inna tsiyar da tayiwa Aseem Shaheed ba.
Kwana Asma tayi tana tunanin dalilin da yasa Aseem yakeson siyan gdansu, a daren taci alwashin indai Allah ya hadasu gobe a hanyar makaranta sai taci mutuncinsa yanda zaiji bama ya sha'awar siyan gdan nasu, aikuwa tun asuba ta shirya taja ta zauna tana jiran lkc bakwai daidai ta fice daga gdansu ta nufi gdansu Jiddah suka dunguma suka tafi tana bawa jiddah labarin abinda ya faru jiya na zuwan Aseem gdansu a matsayin Wanda zaisai gdan zaiyi kiwon shanu"
Dariya sosai Jiddah tayi tace “kin gamu da qarfen qafa me wuyar kwancewa wato gayen nan ya shiryawa wasan so yake ya qure malejinki ya wulaqantaki Kinga idan ya siye gdanku ko haya ya baku ai babanku ya koma qarqashinsa balle ma tashinku zaiyi a wulaqance ya zuba shanu a gdan Kinga ya nuna Miki rayuwar shanunsa tafi taku muhimmanci. Nifa dama bangano Miki nasara a buga wasa da wannan mutumin ba da ganinsa kinsan yaci yatada Kai zai iya ramawa wulaqancin da zakiyi Masa ta duk inda yaso gara dai yan gujaru gujarun da muke tsokana Basu da yanda zasuyi damu sai tsaki sai harara"
Har sukaje makarantar Allah be hadasu dashi ba haka ta rinqa Allah Allah a tashi nanma Basu gamu ba taji haushi sosai so batada yanda zatayi dole ta hqr tana zuwa suka nufi islamiyya sai yamma suka dawo liqis dake laraba ce sunyi hadda a dakin zaure suka tarar da Mal Husaini da Mal Bala suna tattaunawa Mal Husaini sai dariya yakesu suka durqushe suka gaishesu da fara'a Mal Bala ya amsa inda Mal Husaini yace “Ina Ma'ulelena zonan dan qaniyarki" gabanta ya fadi tunda dama a tsorace take tana jiran abinda zaije ya dawo.
Matsawa tayi a darare ta zauna tana barin jiki don tasan ba wuya bane Mal ya maketa ba gyaran murya yayi yace “Ina kike Asma'ul Husnah?" Ajiyar zuciya tayi tace “gani Mal" Jinjina Kai yayi yace “yawwa Masha Allah dama wani umarnin gaggawa zan baki Kinga dai a yanda kuka taso a wahale a talauce to ke ki godewa Allah yasoki da arziqi yayi miki ludufi da ludufin da yakewa duk Wanda yaso cikin bayinsa jiya anzo ganin gida Ashe rabon aganki ne dan farin yaron nan Alhajin Birni eh wlh tallahi shine dai bayan sunga gda kinje kin gaishesu yagani yakeso harma yayimin alqawarin idan na bashi aurenki zai barmin gdana Kuma zaiyimin komai na auren Dijangala da Zabba'u keko yace ki cokali bashi buqata, kinji fah inda arziqi yake"
Tunda ya fara mgnr ta kafesa da ido cikin mugun tsoro da kaduwa ta gane waye yake nufi domin Zahran ba fari bane Aseem ne fari Anna sai tace “wa...waikace Mal Sadiqun fah?" Wata uwar harara ya buga Mata yace “Sadiqun0 ubanki yo ko Laminu ne uban Sadiqu ya dawo duniya ai bazai hanani cin wannan arziqin ba ke nifa bama shawara nake daku ba dagake har uwarki dama na dauka ke dake kin shafi zamani zakiba da hadin Kai to kema naga qwalluwar yar baqin ciki ce saboda haka tashi ware kauce karna makeki sauna kawai wadda arziqi ke binta tsiya ke dawo da ita baya"
Yana fadin haka ya miqe abinda yasata miqewa itama da gudu tayi cikin gdan tana rushewa da kuka tana cewa “wlh baa isaba bazaa taba cutata a hadani da wannan shegen azzalumin mutumin ba ai bani kadai aka Haifa a gdanba abashi wata Mana saini saboda an rainamin hankali...." Jin takun sawayen Mal Husaini yasata shigewa qarqashin gadon qarfen Inna tana kuka ya shigo dakin yana huci Yana cewa “kajimin mutane yan baqin ciki arziqi yazomin har gda Allah ya amsa addu'a ta Nima nakusa hutawa shine zakuyimin baqin ciki tabdi ai wlh baku isaba wannan aure me hanashi saidai mutuwa idan ma mutuwa zakiyi saidai ki mutu ja'irar yarinya kina tafe kamar ki karye saboda rama yo kika sake kika auri Wannan Dan gadon talaucin da ubansa tunda nasanshi da tàgiya daya nasanshi basai kin qwammace wannan makauniyar uwar taki barinki tayi ba"
Harya gama sababinsa ya fita Inna batace komai ba sai bayan ya fitane Asma'u ta fito tanata shassheqar kuka Inna tace “wai waye wannan ne daga zuwa Mal ya aminta dashi Babu binkice Babu komi?" Nan Asma'u ta yiwa Inna bayani Inna ta saki salati da sallalami tare da yiwa Allah kirari tace “naga takaina ni aminatu dama akan wannan kwasasshen mutumin Mal yacimin mutunci har Yana cimin alwashin aure Babu fashi aikuwa da fashi don baza'ayi wannan son zuciyar dani ba yaro shekara da shekaru Yana wahala Rana tsaka saboda son abin duniya Mal ya rufe ido yana cima mutane mutumci ai bake kadai ya haifaba yabasa wata Amma bake ba"