Sashe 5
Zarrah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yarinya ce me qwazo tun tana qarama hakan yasa uwarta taci burin sai tayi karatu me zurfi lkcn da aka makantar da Inna lkcn Asma'u ta gama primary daganan abubuwa sukayita lalacewa dan abinda ake fita a Nemo na rainawa babu halin fita a nemoshi Nan suka shiga Ni yasu abinda zasuci ma yakan gagaresu akwai wani yaro Sadiqu da tun tasowar Asma'u yakeyi Mata wahala shine rakata makaranta shine komanta saiya zamana idan yasai da rake ko ya dauki tallan yalon bello yaje ya siyar ne yake samu yabasu abinda zasuci.
Ana hakane wata Ladi almajira tayiwa Inna tayin fita bara tunda dai Allah yasani batada mataimaki da farko Inna taqi abin Amma lkcn da Asma'u ta farayi mata mitar duk qawayenta sun tafi makarantar secondary ita tana gda saita farabin Ladi bara suna samo na batarwa a hakadai har suka Tara kudin makarantar lkcn har anci zango daya suka kaita Prime school dake Inna tun dacan Bata yarda yaranta sunyi makarantar gwamnati ba tace Babu karatu ita Kuma so take yaranta suyi karatu, daga lkcn da Asma'u ta fara zama budurwa saiya kasance idan sunje neman taimako mutanenmu sai suka fara nuna maitarsu akan yarinyar itakuma uwar tana nuna Mata aibin hakan musamman dake Asma'u tana zuwa islamiyyar dare, matsalar Asma'u daya ita tun tana qarama batada hqr Kuma Bata yafiya indai kayi Mata saita rama so da mutane suka fara gwada rashin imaninsu akan mahaifiyarta sai ta dauki gabarar duk Wanda yayi Mata ko waye a duniya saitayi Masa kalmarta daya itace “ka jira ZARRAH ta ranar da zan zama babbar likita zanyi fada da uban kowa a duniya Kuma zan nuna maka kaiba komai bane" yanzu haka zancen da nakeyi maka burinta na gab da cika domin kuwa takusa kammala secondary Wanda Innarta tafi shekara biyar tana adashin gata domin Asma'u ta wucce makarantar da zatayi karatunta na likitanci"
Murmushi Dr Aseem yayi yace “aikinka yana kyau Kuma meye yanayin ubanta da kudi sannan a wacce unguwa suke zaune?" Jinjina Kai Zahran yayi yace “wanda yayimin bayanin tarihinsu yace kirarin mahaifinta Mal Husaini idon cin naira indai kanada kudi to kanada cikakken mutumci a gurinsa idan kuwa baka dashi to kashinsa yafika daraja anan Tukuntawa gdansu yake shikuma babanta a sabuwar gandu majalissarsu take gefen rumfar wani me nama suna zaune idan ansiya suyi sudi aikinsu kenan"
Jinjina Kai Aseem yayi yace “ka gama magana inason kwadayayyen mutum saboda buri yana saurin cika Asmah ki jirayi zuwana burinki bazai taba cikaba zan rusanki duk wata walwala da farin ciki zaki rayu da qunci zan massheki baiwa a gdana saikin lashe tafin qafata da harshenki...... Dafashi Zahran yayi yace “tabani haushi dazu Amma da naji tarihinta sai tabani tausayi please ka hqr da daukar fansar nan kabarta don Allah akwai quruciya yarinya ce qarama fah....." Hannu ya Dora Masa a baki yace “karka qara bani hqr wlh bantaba tausayin wani Abu kamar yanda na tausayawa yarinyar nan ba Amma hakan bazai hanani daukar mataki akanta ba saita Raina kanta Kuma sai tasan tasa Wasa da Aseem Shaheed"...........
Vote
Comments
Share
*_Oum Hairan_*
[20/06 4:27 pm] Oum Hairan: *ZARRAH*
_Tare da Alƙalamin_
*_Oum Hairan_*
_Bismillahir Rahamanir Rahim_
_Free Page 9-10_
*_Wattpad realfauzahtasiu_*
Telegram
👇
https://t.me/joinchat/Gdtmu0TgTHu66CF7
_____________________________
_____________________________
Tunda Asma'u ta koma gida take zumbure zumbure Matan gdan Babu Wanda ya kulata Inna kuwa ba ido ba balle tasan matsalar yartata haka tayi wanka tayi sallar azahar da La'asar ta zauna tsince wake bayan ta gama ta dora musu abinci tana girkin tana qunquni da haka ta gama ta zuba ta zauna tanaci bayan ta gama ta shirya ta tafi islamiyya sai shidda ta dawo lkcn uniform dinta ya jiqu ta wankeshi ta shanya sai lkcn ta jirge ta zauna tana bawa Inna lbrn abinda ya faru.
Sosai Inna ta nuna rashin jin dadinta da abinda yartata tayiwa Aseem tare da rufeta da fada daga baya ta dawo yimata nasiha to ta danji a lkcn ta miqe tayi sallah ta kwanta, washegari da wuri ta fice saboda so takeyi yau suje makarantar da wuri cikin saa ta tarar da Jidda ta shirya suka tafi suna tafe suna Hira Jidda tace.
“Nifa jiya kin kullemin Kai Asma'u waike bakida tsoro ne baki tsoron kada mutumin nan ya sanya yan sanda su kamaki?" Tsaki tayi tace “kuma saboda Ina tsoro saina bari yaci mutumcina na qyaleshi ko?"
Kada Kai Jiddah tayi tana Shirin yin magana wata mota tazo ta giftasu kawai sai sukaga taci burki a gabansu hankalin Asma baa kan motar yake ba har zasu gifta taji Jidda tace “mun shiga uku Asma'u mutumin jiya ne fah" da sauri ta kalli gurin suka hada ido ta galla masa harara ta qarawa tafiyarta sauri saboda Inna tace idan ta sake kulashi sai taci mutuncinta.
Murmushi yayi cike dajin tsanar yarinyar a qasan zuciyarsa yaja motarsa ya qara gaba ta gefenta ya wucce shuuu taja fasali tace “kaci arziqin Inna ta hanani kulaka wlh yauma dasai nayi maka rotse sakarai Wawa"
Duk da Aseem baiji abinda ta fada ba Amma ya fahimci dashi take murmushi yayi ya qara bawa motarsa wuta tabbas sai yayi maganin rashin kunyar yarinyar nan da take ganinta daidai dashi saiyabi ta kowacce hanya yaga ya koya Mata hankali saiya sanya Mata jin cewa Ashe ita ba kowa bace a rayuwarta tunaninsa yanzu ta inda zai fara gudanar da aikinsa kisan mummuqe yakeson yimata batare da wani ya gane qudurinsa ba yakeso ya baje tarihin rashin kunyar Asma'u,
Yana tuqi yana murmushi Yana maimata sunanta yanayin yanda ta harareshi dazun yana Masa gizo yanajin wani nishadi da Allah yasa yarinyar ta siyar Masa da qasar wasan dole akwai badaqala zai ganar da ita kurenta na shiga sharafin daba nataba. Koda yaje asibitin ya fara duba marasa lfyrsa bayan ya gama ya wucce nasa private hospital nanma yayi abinda zaiyi sannan ya shige office dinsa ya zauna yana juyi a kujerarsa cike da zumudin ganin yamma tayi Zahran ya gama aikinsa ya daukeshi suje su nemi mahaifin Asma'u kamar yanda ya tsara kafinnan Saida ya sake tura wani yaronsa yayi masa binciken tsaf inda anan ne yaron nasa Uzairu yake sanar dashi ai Mal Husaini yasa gdansa a kasuwa zaiyi auren yaransa uku sukuma iyayen zasu koma qauye da zama wacce bazataba Kuma tasan inda dare yayi mata.
Fiye da tunani Aseem yaji dadin wannan farin lbr aikuwa hudu da rabi suka fice daga asibitin suka nufi bakin kasuwar sabuwar gandu inda anan Mal Husaini yake zama Nan suka nemi a rakasu ofishin dillalan qasa akayi musu jagora sukaje suka gaisa Zahran yana nunawa Aseem Mal Husaini da yaketa maka hamma da hularsa ko Kari Babu bisa dukkan alamu yunwa yakeji.
Caraf kuwa Alh Bala dillali yace “Idon cin naira da alamun dai yau baa sammaka abin sawa a maqoshi ba ka fito" kamar me jiran kadan ya balle zance kamar Wanda ya qone a tsakiyar ka cewa yake “yo dama wadannan sakarkarun waye yanzu yake sammin abincin Lantana da Lamunde sunce sun daina cida qato Wai auren yayansu zasuyi Amina ce me tausayina take bane to itanma saidai idan wannan ja'irar yarinyar Ma'u batanan amma fir take hanawa tace ai ba Basu nakeyi ba kuma tana ganin lkcn da nake bawa Lamunde nikuma ganin suna fita bara nasan na annabi baya qarewa shiyasa bandamu da sammusu ba gashi anma kasa samun me siyan kangon can nawa bare na Dan murmure kafin bikin nan"
Jinjina Kai Aseem yayi Bala dillali ya dubesu yace “Alh Allah gida ko fili ko kango ko haya ake buqata?" Cire hularsa yayi ya maida hankalinsa ga Zahran Zahran ya gyara zama ya karkace yace “gda muke buqata ginin gargajiya anan Tukuntawa zamu zuba shanu da tumaki a ciki...." Yunqurowa Mal Husaini yayi Mal Bala ya dakatar dashi yace “toh ikon Allah kamar Kuma na nawa kuke buqata?" Kallon Aseem Zahran yayi Aseem da sai yanzu yaga samar mgn yace “ba qarami ba ba babba ba duk yanda kasuwa ta Kama munaso idan akwai a nuna Mana abune na urgent da muke buqatarsa tsakanin yau da sati biyu" duba Mal Bala yakai ga Mal Husaini da dama yake jiran abashi dama nan yayi kwance kwance yace “yo Alh Allah muje suga nawa Mana ko Allah zaisa a daidaita tunda qananun masu kudi sun kasa siye sunce zaici kudi wajen gyaransa
Tunda ya fara mgnr Aseem ya zuba Masa ido har ya gama murmushi Aseem yayi Wanda shikadai yasan dalilin murmushin nasa yace “ok muje mu gani idan yayi sai muyi ciniki Amma gsky muna buqatar gurin da wuri zamuyi aiki a ciki ne" Babu tunanin makomar iyalai Mal Husaini yace “Haba yaro abinda yake kasuwa ai ko yau kakeson abinka baka akayi indai ka biya nidai fatana Allah yasa gurin yayi maka fitinar zabba'u ta isheni yau ta debo wannan gobe ta kwaso wancan gara na auraddasu kawai na huta sauran kudin naci tsire dasu hhhh koba hakaba yaro..."
Sudai murmushi kawai sukayi suka nufi motar Mal Bala da Mal Husaini suka shiga baya Aseem da Zahran suna gaba a haka Mal Husaini yaketa basu kwatance suna amsawa har suka shiga unguwar tun daga farkonta suka fara Raina kansu asalin uguwar talakawa ce ko Ina kwatami ne yake gudu haka sukayita kutsawa lunguna har suka isa qofar wani tsohon gda ginin jar qasa dako arziqin yabe bai samu ba babu qofa a gidan sai labulan tampol da aka sanya domin sakaye gdan, tundaga qofar gdan Aseem ya qara Raina matsayin Asma'u tare da tsananin mamakin izzarta a matsayinta na wadda ta taso a wannan rubabbiyar unguwa a unguwar ma a gda mafi qasqanci domin shidai iyakar dubansa baiga gdan da yakai nasu Asma'u lalacewa ba a area.
Ana hakane wata Ladi almajira tayiwa Inna tayin fita bara tunda dai Allah yasani batada mataimaki da farko Inna taqi abin Amma lkcn da Asma'u ta farayi mata mitar duk qawayenta sun tafi makarantar secondary ita tana gda saita farabin Ladi bara suna samo na batarwa a hakadai har suka Tara kudin makarantar lkcn har anci zango daya suka kaita Prime school dake Inna tun dacan Bata yarda yaranta sunyi makarantar gwamnati ba tace Babu karatu ita Kuma so take yaranta suyi karatu, daga lkcn da Asma'u ta fara zama budurwa saiya kasance idan sunje neman taimako mutanenmu sai suka fara nuna maitarsu akan yarinyar itakuma uwar tana nuna Mata aibin hakan musamman dake Asma'u tana zuwa islamiyyar dare, matsalar Asma'u daya ita tun tana qarama batada hqr Kuma Bata yafiya indai kayi Mata saita rama so da mutane suka fara gwada rashin imaninsu akan mahaifiyarta sai ta dauki gabarar duk Wanda yayi Mata ko waye a duniya saitayi Masa kalmarta daya itace “ka jira ZARRAH ta ranar da zan zama babbar likita zanyi fada da uban kowa a duniya Kuma zan nuna maka kaiba komai bane" yanzu haka zancen da nakeyi maka burinta na gab da cika domin kuwa takusa kammala secondary Wanda Innarta tafi shekara biyar tana adashin gata domin Asma'u ta wucce makarantar da zatayi karatunta na likitanci"
Murmushi Dr Aseem yayi yace “aikinka yana kyau Kuma meye yanayin ubanta da kudi sannan a wacce unguwa suke zaune?" Jinjina Kai Zahran yayi yace “wanda yayimin bayanin tarihinsu yace kirarin mahaifinta Mal Husaini idon cin naira indai kanada kudi to kanada cikakken mutumci a gurinsa idan kuwa baka dashi to kashinsa yafika daraja anan Tukuntawa gdansu yake shikuma babanta a sabuwar gandu majalissarsu take gefen rumfar wani me nama suna zaune idan ansiya suyi sudi aikinsu kenan"
Jinjina Kai Aseem yayi yace “ka gama magana inason kwadayayyen mutum saboda buri yana saurin cika Asmah ki jirayi zuwana burinki bazai taba cikaba zan rusanki duk wata walwala da farin ciki zaki rayu da qunci zan massheki baiwa a gdana saikin lashe tafin qafata da harshenki...... Dafashi Zahran yayi yace “tabani haushi dazu Amma da naji tarihinta sai tabani tausayi please ka hqr da daukar fansar nan kabarta don Allah akwai quruciya yarinya ce qarama fah....." Hannu ya Dora Masa a baki yace “karka qara bani hqr wlh bantaba tausayin wani Abu kamar yanda na tausayawa yarinyar nan ba Amma hakan bazai hanani daukar mataki akanta ba saita Raina kanta Kuma sai tasan tasa Wasa da Aseem Shaheed"...........
Vote
Comments
Share
*_Oum Hairan_*
[20/06 4:27 pm] Oum Hairan: *ZARRAH*
_Tare da Alƙalamin_
*_Oum Hairan_*
_Bismillahir Rahamanir Rahim_
_Free Page 9-10_
*_Wattpad realfauzahtasiu_*
Telegram
👇
https://t.me/joinchat/Gdtmu0TgTHu66CF7
_____________________________
_____________________________
Tunda Asma'u ta koma gida take zumbure zumbure Matan gdan Babu Wanda ya kulata Inna kuwa ba ido ba balle tasan matsalar yartata haka tayi wanka tayi sallar azahar da La'asar ta zauna tsince wake bayan ta gama ta dora musu abinci tana girkin tana qunquni da haka ta gama ta zuba ta zauna tanaci bayan ta gama ta shirya ta tafi islamiyya sai shidda ta dawo lkcn uniform dinta ya jiqu ta wankeshi ta shanya sai lkcn ta jirge ta zauna tana bawa Inna lbrn abinda ya faru.
Sosai Inna ta nuna rashin jin dadinta da abinda yartata tayiwa Aseem tare da rufeta da fada daga baya ta dawo yimata nasiha to ta danji a lkcn ta miqe tayi sallah ta kwanta, washegari da wuri ta fice saboda so takeyi yau suje makarantar da wuri cikin saa ta tarar da Jidda ta shirya suka tafi suna tafe suna Hira Jidda tace.
“Nifa jiya kin kullemin Kai Asma'u waike bakida tsoro ne baki tsoron kada mutumin nan ya sanya yan sanda su kamaki?" Tsaki tayi tace “kuma saboda Ina tsoro saina bari yaci mutumcina na qyaleshi ko?"
Kada Kai Jiddah tayi tana Shirin yin magana wata mota tazo ta giftasu kawai sai sukaga taci burki a gabansu hankalin Asma baa kan motar yake ba har zasu gifta taji Jidda tace “mun shiga uku Asma'u mutumin jiya ne fah" da sauri ta kalli gurin suka hada ido ta galla masa harara ta qarawa tafiyarta sauri saboda Inna tace idan ta sake kulashi sai taci mutuncinta.
Murmushi yayi cike dajin tsanar yarinyar a qasan zuciyarsa yaja motarsa ya qara gaba ta gefenta ya wucce shuuu taja fasali tace “kaci arziqin Inna ta hanani kulaka wlh yauma dasai nayi maka rotse sakarai Wawa"
Duk da Aseem baiji abinda ta fada ba Amma ya fahimci dashi take murmushi yayi ya qara bawa motarsa wuta tabbas sai yayi maganin rashin kunyar yarinyar nan da take ganinta daidai dashi saiyabi ta kowacce hanya yaga ya koya Mata hankali saiya sanya Mata jin cewa Ashe ita ba kowa bace a rayuwarta tunaninsa yanzu ta inda zai fara gudanar da aikinsa kisan mummuqe yakeson yimata batare da wani ya gane qudurinsa ba yakeso ya baje tarihin rashin kunyar Asma'u,
Yana tuqi yana murmushi Yana maimata sunanta yanayin yanda ta harareshi dazun yana Masa gizo yanajin wani nishadi da Allah yasa yarinyar ta siyar Masa da qasar wasan dole akwai badaqala zai ganar da ita kurenta na shiga sharafin daba nataba. Koda yaje asibitin ya fara duba marasa lfyrsa bayan ya gama ya wucce nasa private hospital nanma yayi abinda zaiyi sannan ya shige office dinsa ya zauna yana juyi a kujerarsa cike da zumudin ganin yamma tayi Zahran ya gama aikinsa ya daukeshi suje su nemi mahaifin Asma'u kamar yanda ya tsara kafinnan Saida ya sake tura wani yaronsa yayi masa binciken tsaf inda anan ne yaron nasa Uzairu yake sanar dashi ai Mal Husaini yasa gdansa a kasuwa zaiyi auren yaransa uku sukuma iyayen zasu koma qauye da zama wacce bazataba Kuma tasan inda dare yayi mata.
Fiye da tunani Aseem yaji dadin wannan farin lbr aikuwa hudu da rabi suka fice daga asibitin suka nufi bakin kasuwar sabuwar gandu inda anan Mal Husaini yake zama Nan suka nemi a rakasu ofishin dillalan qasa akayi musu jagora sukaje suka gaisa Zahran yana nunawa Aseem Mal Husaini da yaketa maka hamma da hularsa ko Kari Babu bisa dukkan alamu yunwa yakeji.
Caraf kuwa Alh Bala dillali yace “Idon cin naira da alamun dai yau baa sammaka abin sawa a maqoshi ba ka fito" kamar me jiran kadan ya balle zance kamar Wanda ya qone a tsakiyar ka cewa yake “yo dama wadannan sakarkarun waye yanzu yake sammin abincin Lantana da Lamunde sunce sun daina cida qato Wai auren yayansu zasuyi Amina ce me tausayina take bane to itanma saidai idan wannan ja'irar yarinyar Ma'u batanan amma fir take hanawa tace ai ba Basu nakeyi ba kuma tana ganin lkcn da nake bawa Lamunde nikuma ganin suna fita bara nasan na annabi baya qarewa shiyasa bandamu da sammusu ba gashi anma kasa samun me siyan kangon can nawa bare na Dan murmure kafin bikin nan"
Jinjina Kai Aseem yayi Bala dillali ya dubesu yace “Alh Allah gida ko fili ko kango ko haya ake buqata?" Cire hularsa yayi ya maida hankalinsa ga Zahran Zahran ya gyara zama ya karkace yace “gda muke buqata ginin gargajiya anan Tukuntawa zamu zuba shanu da tumaki a ciki...." Yunqurowa Mal Husaini yayi Mal Bala ya dakatar dashi yace “toh ikon Allah kamar Kuma na nawa kuke buqata?" Kallon Aseem Zahran yayi Aseem da sai yanzu yaga samar mgn yace “ba qarami ba ba babba ba duk yanda kasuwa ta Kama munaso idan akwai a nuna Mana abune na urgent da muke buqatarsa tsakanin yau da sati biyu" duba Mal Bala yakai ga Mal Husaini da dama yake jiran abashi dama nan yayi kwance kwance yace “yo Alh Allah muje suga nawa Mana ko Allah zaisa a daidaita tunda qananun masu kudi sun kasa siye sunce zaici kudi wajen gyaransa
Tunda ya fara mgnr Aseem ya zuba Masa ido har ya gama murmushi Aseem yayi Wanda shikadai yasan dalilin murmushin nasa yace “ok muje mu gani idan yayi sai muyi ciniki Amma gsky muna buqatar gurin da wuri zamuyi aiki a ciki ne" Babu tunanin makomar iyalai Mal Husaini yace “Haba yaro abinda yake kasuwa ai ko yau kakeson abinka baka akayi indai ka biya nidai fatana Allah yasa gurin yayi maka fitinar zabba'u ta isheni yau ta debo wannan gobe ta kwaso wancan gara na auraddasu kawai na huta sauran kudin naci tsire dasu hhhh koba hakaba yaro..."
Sudai murmushi kawai sukayi suka nufi motar Mal Bala da Mal Husaini suka shiga baya Aseem da Zahran suna gaba a haka Mal Husaini yaketa basu kwatance suna amsawa har suka shiga unguwar tun daga farkonta suka fara Raina kansu asalin uguwar talakawa ce ko Ina kwatami ne yake gudu haka sukayita kutsawa lunguna har suka isa qofar wani tsohon gda ginin jar qasa dako arziqin yabe bai samu ba babu qofa a gidan sai labulan tampol da aka sanya domin sakaye gdan, tundaga qofar gdan Aseem ya qara Raina matsayin Asma'u tare da tsananin mamakin izzarta a matsayinta na wadda ta taso a wannan rubabbiyar unguwa a unguwar ma a gda mafi qasqanci domin shidai iyakar dubansa baiga gdan da yakai nasu Asma'u lalacewa ba a area.