Sashe 19
Zan Fasa Kwai Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bata fito fili ta fada mishi ba Amma ya lura da ita da take taken ta
Amma duk da haka yayi Mata hanzari don abinda ya nuna mishi kamar tagaji shine kullum cikin bacin Rai take abu kadan Kuma sai ya fusata ta Koda ko ita da yarane sai kaji tana ta antaka musu zagi abinda ta San bayaso bare duka sai ya zamo yanzu duk ta hada tanayiwa yaran sai dai ya kalla ya kauda kanshi
Idan Kuma ta hadosu shi da ita zata rufe idonta ta gurza Rashin mutunci son ranta Amma duk da hakan baya biyewa don ya San mafarin lamarin har dai wata Rana ya zaunar da ita Yana mata nasiha
"Kiyi hakuri lubabatu komai Kika gani aduniya Yana da farko da Kuma karshe. Kar wannan canjin yasa kiji aranki ko Rahamar ta Kare ko babu sauran wani Jin Dadi Nan gaba . A a yanzu ne ma lamarin zai Fara duk bawan da Kika ga an jarrabeshi matukar ya cinye jarrabawar shi to matakin nasara ne ya hau . Hska Kuma Babu Wanda zaiyi hakuri Bai cimma rabar hakurin shi ba don haka don Allah da manzon sa kiyi hakuri babun da muke ciki in Sha Allah zamu samu kanmu cikin wadata wata Rana matukar dai munyi hakuri domin Allah. Na sani ba kowane zai jurewa Rashi ba to Amma ai bawan da yayi imani yasan Dole ajarabeshi sai mu godewa Allah da ya bamu wannan jarabtar me sauki kiyi hakuri ki Kuma jure ki koma hango baya yadda kika samu Kai sai ki godewa Allah shi Kuma sai ya dubeki ke da lamarin ki.
Ta matse hawaye ba tare da tankawa nasihar sa ba inda yaji tausayin ta ya Kara kamashi
Da hakan dai ake ta gurgurawa da Dadi ba Dadi kamar dai ta dauka ko ta hakura inda ake cikin Rufin Asirin Allah wani abun mamaki Kuma ba a Kara kiranshi Kan abinda ya shafi harkar kwangila ba shima kuma Bai nemi cusa kanshi ba ya tsaya matsayin shi Yana ta laluben hanyar da Asiri zai rufu inda Allah cikin ikon shi masu zanen taswirar gidaje Kan bashi aikin zanen kasancewar shi eng Wanda ya hada har da sanin makamar zanen inda Kuma kudi ke Dan shigowa Amma ba kamar yadda aka sababa
Inda agefe Daya Kuma Kabir yayi wata irin shahara da tunbatsa akan harkar gwangila saboda ayanzu shine ke Kan kadamin shi aiki Kuma Babu nagarta haka za ayi shi agama kafin lokaci kadan ya lalace saboda an saka manuba da ha inci
Malam Ali yayi ta Kiran wayar shi Amma kememe yaki dagawa saboda ya San maganar dungo za ayi mishi inda a yau malam Ali ya bugo hanya ya iso garin Abuja duk da Bai San gidan Kabir din ba Amma akace matambayi baya Bata kasancewar shi shahararre Bai Sha wuya wurin gano gidan ba inda ya tsaya Yana karewa gidan kallo Wai gidan dan dungo ne wannan Amma ta Rayu a wani gida da bashi da maraba da kufai saboda ruwan damuna da ya kayar dashi Anna Bata samu arzikin tadawa ba Amma dubi gidan da yazo garin Abuja ya Gina tamkar yayi wurin Zama aduniya
Bama wannan ne abin ji ba irin yadda aka kirashi yazo ya samu mahaifiyar shi cikin halin ciwo da neman agaji Amma bawan Allah Nan tunda ya ufa ya tafi Bai Kara waiwayo ta ba bare yayi tunanin duba yadda ta karaji da jiki bare ya kawo Mata dauki ko agaji
Yau tsayin watanni shida Babu dungo Babu labarin ta Amma ko dai dai da Rana guda Daya Tak Bai tunawa da uwar shi na cikin neman taimako da agaji bare Kuma ya ruko wani Abu irin na jinkai da ya'yan kwarai masu neman albarka kewa tsaffin su Kai wannan wace irin SHIGA UKU da asara ce? Ubangiji ka shiryi bayinka masu Bata kasa yaran musulmi su zamowa iyayen su sanyi idaniya irin su kabiru Kam da haihuwar su wallahi gara barin su don haihuwar su batayiwa Wanda yayita Rana ba
Malam Ali ya share hawayen tausayin dungo yayiwa me gadin magana akan asanar da me gidan yayi bako
Aiko sai gashi ya fito cikin shiga ta Wanda ya samu wurin Zama a duniya Kaya masu tsada Wanda kallo daya zakayi mishi ka bashi matsayin minister ko Dan majalissa
Ganin malam Ali yasa ya ji wani Abu marar Dadi ya sauki she da ruwa da lemu inda yake tambayar shi
"Kabiru baka tambayi me jiki ba bare ka Kira kaji ya ta Kare ji?
"To ai lafiya ita ke fakuwa na San dai taji sauki..............
"Amma ko taji sauki ai tana bukatar kulawa mussamman Kai da kake dolen ta
"Kabir kayi sannu da kidan da duniya ke maka kana taka rawa Wallahi Babu komai acikin wannan Rayuwar sai rudani
Duk nasarar mutum a Rayuwa ya samota ne daga addu ar iyaye don su ke da mabudin kowace irin nasara...
"Bama abinda ya kawo Ni wurinka kenan ba don kowa ya gyara ya sani banzo don nayi maka wa azi ba sakone dungo taba Ni ta Kuma ce in isar gareka gashi Kuma Allah ya Taya min na kawo maka sai dai abin tashin hankali da saka zuciya rawa shine mun nemi dungo sama ko kasa mun rasa.....................
[5/24, 7:50 PM] Aunty Fauzah Yar Amanah: *ZAN FASA KWAI*
*NA*
*HADIZA BARA'U GIDAN IKO*
_Hakkin Mallakar na gidan iko ne_
*Page 37*
*_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
...........Arude yake kallon malam Ali Jin yace Wai Babar tashi ta bace an nemeta sama da kasa Babu ita Babu labarin ta.............
"Malam Ali ba asan inda take ba kenan?
"Abinda yake daurewa mutane Kai kenan don faruwar lamarin tamkar kiftawar ido Wai an nemi dungo Babu ita Babu dalilin ta
"Shin wani ne ya sace ta Koko guduwa tayi???..........
"Allah shine mafi sani abinda kawai na kawowa Raina shine dungo tana ganin Bata da kowa sai kanta idan ta faku idanun Al umma batayi laifi ba shiyasa don nafi zargin guduwa tayi don bakin ciki Babu abinda baya sawa...........
"Bakin cikin me malam Ali?........
"Bakin cikin ka kabiru me yuwa dungo tana kallon kanta a wadda batayi SA AR haihuwa ba don ban taba ganin Dan halak yayi irin abinda kayiwa mahaifiyar ka ba Kabir
Abu Daya Zan fada maka shine ka saurari zuwan musiba don kuwa kajawo Allah fada....
Arikice kabiru ya Mike Yana duban malam Ali da ya fada mishi gaskiya Amma ya kasa abinda zaiyi don ya yarda ya amince lallai ya jawo Allah fada
Malam Ali ya Mike Yana fadin
"Ni na koma sai Allah ya kaddaro saduwar mu idan kazo inda nake ma gaisa idan kuwa ta Kama mun hadu shima ma gaisa don ba Zan yaudari kaina cewa zaka zo gidana sada zumunci ba Toni a wa?
Da haka malam Ali ya fice ya bar Kabir da hada hudu da ukun da zasu bashi takwas
Izzatu da taji batun itama taji Babu Dadi Amma sai tace addua kawai zasuyi itace mafita
Yayinda humaira fulani taji ya kakar tata ta Bata kuka take tamkar dai izzatu ce ta Bata abinda ya Bata ran izzatu ta shiga zazzaga Mata masifa
Kwana biyu Kabir ya watsar da batun dungo inda yace duk ma inda ta SHIGA zata fito idan Kuma tayi haka ne don ta tada mishi hankali to ta tada mishi
Bai samu zarafin duba kunshin da takardar ba ya kwashe su ya watsa ciki kabit din ajiyar takardun shi
Kwana biyu ummita na zuwa kuki cafee kasa saboda Babu kudin da zatayi transport din zuwa gashi saura wata biyu ta Ida ta karbi sakamakon
Tana tafe anatse inda kamar daga sama Wilson ya hangota zata ketare titin da zai sadata da kuki cafee inda ya zuba Mata ido a yau ji yake tamkar idan baiyi Mata magana ba zaiyi Rashi na zuciyar shi sai dai kafin ya faka motar ya fito har ta shige
Ya kasa tsaye da zaune zuciyar shi na kawo mishi shawarwari akan kawai ya jira ta fito in yaso ko mayar da its gidane sai yayi Aiko ya dasa zaman jira har uku na maraice ta fito ta soma tafiya inda ya kula tamkar Bata da lafiya
Ta gota shi kadan ya ga ta dafe bishiya ta rike kanta Wanda alamu suka nuna ciwo yake Mata inda dabara ta fado mishi ya tashi motar ya karaso gareta Yana fitowa
Ya tunkaro ta ta zuba mishi ido kallo daya ta Gane shine Wanda ya tsura Mata idon Nan a country mall
Yayi Mata sallama cikin hausar shi da Bata fita Bata amsa ba ta dai dubeshi
"Sannu fa Naga kamar kina neman taimako na?......
Tayi saurin Kada mishi kanta
"No nagode zaka iya tafiya.
"Kiyi hakuri nasan inda zakije akwai nisa kizo na kaiki Naga kamar kina headache ne ......
"Nagode sosai Zan iya komawa ba damuwa...........
"Kiyi min alfarma ko ta kaiki gida ne tunda har Baki da lafiya..........
"Idan aka ganni a motarka nace me? "Ka ganka kuwa ? "Taimako wani abune da addinin mu ya koyar damu ga mabiyan sa shin kana daga mabiyan ne da zaka taimakeni?
"To duhu da haske basa tarayya a wuri Daya Dole daya ke bawa Daya wuri idan haske ya bayyana to duhu yayewa yake don haka na gode da taimakon ka gareni
"Na sani amma haka Nan naji Ina son taimakon ki tunda muma namu addinin ya koyar damu taimakon Kuma Bai saka kiyayya ga sauran addinan ba indai ba naku adfinin ya saka muku kiyayyar sauran addinan ba. Kiyi hakuri ki shigo na saukeki nayi Miki alkawarin Babu cuta tsakanin mu haka kawai nake son taimakon ki
Azahiri ita kanta tana bukatar taimakon don Jin kanta take tamkar zai tarwatse Dole ma ta nemi abinda zai kaita gida don Bata sababa ga kuma yunwa da takeji wadda idan akasa tace zata tafi to ko shakka Babu sai dai akwashe ta amika gidan don haka ta sallama ta shiga motar yaja suka iso gida ya sauketa ya Miko Mata fakitin maganin ciwon Kai me tsadar gaske ta karba tana godiya
Amma duk da haka yayi Mata hanzari don abinda ya nuna mishi kamar tagaji shine kullum cikin bacin Rai take abu kadan Kuma sai ya fusata ta Koda ko ita da yarane sai kaji tana ta antaka musu zagi abinda ta San bayaso bare duka sai ya zamo yanzu duk ta hada tanayiwa yaran sai dai ya kalla ya kauda kanshi
Idan Kuma ta hadosu shi da ita zata rufe idonta ta gurza Rashin mutunci son ranta Amma duk da hakan baya biyewa don ya San mafarin lamarin har dai wata Rana ya zaunar da ita Yana mata nasiha
"Kiyi hakuri lubabatu komai Kika gani aduniya Yana da farko da Kuma karshe. Kar wannan canjin yasa kiji aranki ko Rahamar ta Kare ko babu sauran wani Jin Dadi Nan gaba . A a yanzu ne ma lamarin zai Fara duk bawan da Kika ga an jarrabeshi matukar ya cinye jarrabawar shi to matakin nasara ne ya hau . Hska Kuma Babu Wanda zaiyi hakuri Bai cimma rabar hakurin shi ba don haka don Allah da manzon sa kiyi hakuri babun da muke ciki in Sha Allah zamu samu kanmu cikin wadata wata Rana matukar dai munyi hakuri domin Allah. Na sani ba kowane zai jurewa Rashi ba to Amma ai bawan da yayi imani yasan Dole ajarabeshi sai mu godewa Allah da ya bamu wannan jarabtar me sauki kiyi hakuri ki Kuma jure ki koma hango baya yadda kika samu Kai sai ki godewa Allah shi Kuma sai ya dubeki ke da lamarin ki.
Ta matse hawaye ba tare da tankawa nasihar sa ba inda yaji tausayin ta ya Kara kamashi
Da hakan dai ake ta gurgurawa da Dadi ba Dadi kamar dai ta dauka ko ta hakura inda ake cikin Rufin Asirin Allah wani abun mamaki Kuma ba a Kara kiranshi Kan abinda ya shafi harkar kwangila ba shima kuma Bai nemi cusa kanshi ba ya tsaya matsayin shi Yana ta laluben hanyar da Asiri zai rufu inda Allah cikin ikon shi masu zanen taswirar gidaje Kan bashi aikin zanen kasancewar shi eng Wanda ya hada har da sanin makamar zanen inda Kuma kudi ke Dan shigowa Amma ba kamar yadda aka sababa
Inda agefe Daya Kuma Kabir yayi wata irin shahara da tunbatsa akan harkar gwangila saboda ayanzu shine ke Kan kadamin shi aiki Kuma Babu nagarta haka za ayi shi agama kafin lokaci kadan ya lalace saboda an saka manuba da ha inci
Malam Ali yayi ta Kiran wayar shi Amma kememe yaki dagawa saboda ya San maganar dungo za ayi mishi inda a yau malam Ali ya bugo hanya ya iso garin Abuja duk da Bai San gidan Kabir din ba Amma akace matambayi baya Bata kasancewar shi shahararre Bai Sha wuya wurin gano gidan ba inda ya tsaya Yana karewa gidan kallo Wai gidan dan dungo ne wannan Amma ta Rayu a wani gida da bashi da maraba da kufai saboda ruwan damuna da ya kayar dashi Anna Bata samu arzikin tadawa ba Amma dubi gidan da yazo garin Abuja ya Gina tamkar yayi wurin Zama aduniya
Bama wannan ne abin ji ba irin yadda aka kirashi yazo ya samu mahaifiyar shi cikin halin ciwo da neman agaji Amma bawan Allah Nan tunda ya ufa ya tafi Bai Kara waiwayo ta ba bare yayi tunanin duba yadda ta karaji da jiki bare ya kawo Mata dauki ko agaji
Yau tsayin watanni shida Babu dungo Babu labarin ta Amma ko dai dai da Rana guda Daya Tak Bai tunawa da uwar shi na cikin neman taimako da agaji bare Kuma ya ruko wani Abu irin na jinkai da ya'yan kwarai masu neman albarka kewa tsaffin su Kai wannan wace irin SHIGA UKU da asara ce? Ubangiji ka shiryi bayinka masu Bata kasa yaran musulmi su zamowa iyayen su sanyi idaniya irin su kabiru Kam da haihuwar su wallahi gara barin su don haihuwar su batayiwa Wanda yayita Rana ba
Malam Ali ya share hawayen tausayin dungo yayiwa me gadin magana akan asanar da me gidan yayi bako
Aiko sai gashi ya fito cikin shiga ta Wanda ya samu wurin Zama a duniya Kaya masu tsada Wanda kallo daya zakayi mishi ka bashi matsayin minister ko Dan majalissa
Ganin malam Ali yasa ya ji wani Abu marar Dadi ya sauki she da ruwa da lemu inda yake tambayar shi
"Kabiru baka tambayi me jiki ba bare ka Kira kaji ya ta Kare ji?
"To ai lafiya ita ke fakuwa na San dai taji sauki..............
"Amma ko taji sauki ai tana bukatar kulawa mussamman Kai da kake dolen ta
"Kabir kayi sannu da kidan da duniya ke maka kana taka rawa Wallahi Babu komai acikin wannan Rayuwar sai rudani
Duk nasarar mutum a Rayuwa ya samota ne daga addu ar iyaye don su ke da mabudin kowace irin nasara...
"Bama abinda ya kawo Ni wurinka kenan ba don kowa ya gyara ya sani banzo don nayi maka wa azi ba sakone dungo taba Ni ta Kuma ce in isar gareka gashi Kuma Allah ya Taya min na kawo maka sai dai abin tashin hankali da saka zuciya rawa shine mun nemi dungo sama ko kasa mun rasa.....................
[5/24, 7:50 PM] Aunty Fauzah Yar Amanah: *ZAN FASA KWAI*
*NA*
*HADIZA BARA'U GIDAN IKO*
_Hakkin Mallakar na gidan iko ne_
*Page 37*
*_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
...........Arude yake kallon malam Ali Jin yace Wai Babar tashi ta bace an nemeta sama da kasa Babu ita Babu labarin ta.............
"Malam Ali ba asan inda take ba kenan?
"Abinda yake daurewa mutane Kai kenan don faruwar lamarin tamkar kiftawar ido Wai an nemi dungo Babu ita Babu dalilin ta
"Shin wani ne ya sace ta Koko guduwa tayi???..........
"Allah shine mafi sani abinda kawai na kawowa Raina shine dungo tana ganin Bata da kowa sai kanta idan ta faku idanun Al umma batayi laifi ba shiyasa don nafi zargin guduwa tayi don bakin ciki Babu abinda baya sawa...........
"Bakin cikin me malam Ali?........
"Bakin cikin ka kabiru me yuwa dungo tana kallon kanta a wadda batayi SA AR haihuwa ba don ban taba ganin Dan halak yayi irin abinda kayiwa mahaifiyar ka ba Kabir
Abu Daya Zan fada maka shine ka saurari zuwan musiba don kuwa kajawo Allah fada....
Arikice kabiru ya Mike Yana duban malam Ali da ya fada mishi gaskiya Amma ya kasa abinda zaiyi don ya yarda ya amince lallai ya jawo Allah fada
Malam Ali ya Mike Yana fadin
"Ni na koma sai Allah ya kaddaro saduwar mu idan kazo inda nake ma gaisa idan kuwa ta Kama mun hadu shima ma gaisa don ba Zan yaudari kaina cewa zaka zo gidana sada zumunci ba Toni a wa?
Da haka malam Ali ya fice ya bar Kabir da hada hudu da ukun da zasu bashi takwas
Izzatu da taji batun itama taji Babu Dadi Amma sai tace addua kawai zasuyi itace mafita
Yayinda humaira fulani taji ya kakar tata ta Bata kuka take tamkar dai izzatu ce ta Bata abinda ya Bata ran izzatu ta shiga zazzaga Mata masifa
Kwana biyu Kabir ya watsar da batun dungo inda yace duk ma inda ta SHIGA zata fito idan Kuma tayi haka ne don ta tada mishi hankali to ta tada mishi
Bai samu zarafin duba kunshin da takardar ba ya kwashe su ya watsa ciki kabit din ajiyar takardun shi
Kwana biyu ummita na zuwa kuki cafee kasa saboda Babu kudin da zatayi transport din zuwa gashi saura wata biyu ta Ida ta karbi sakamakon
Tana tafe anatse inda kamar daga sama Wilson ya hangota zata ketare titin da zai sadata da kuki cafee inda ya zuba Mata ido a yau ji yake tamkar idan baiyi Mata magana ba zaiyi Rashi na zuciyar shi sai dai kafin ya faka motar ya fito har ta shige
Ya kasa tsaye da zaune zuciyar shi na kawo mishi shawarwari akan kawai ya jira ta fito in yaso ko mayar da its gidane sai yayi Aiko ya dasa zaman jira har uku na maraice ta fito ta soma tafiya inda ya kula tamkar Bata da lafiya
Ta gota shi kadan ya ga ta dafe bishiya ta rike kanta Wanda alamu suka nuna ciwo yake Mata inda dabara ta fado mishi ya tashi motar ya karaso gareta Yana fitowa
Ya tunkaro ta ta zuba mishi ido kallo daya ta Gane shine Wanda ya tsura Mata idon Nan a country mall
Yayi Mata sallama cikin hausar shi da Bata fita Bata amsa ba ta dai dubeshi
"Sannu fa Naga kamar kina neman taimako na?......
Tayi saurin Kada mishi kanta
"No nagode zaka iya tafiya.
"Kiyi hakuri nasan inda zakije akwai nisa kizo na kaiki Naga kamar kina headache ne ......
"Nagode sosai Zan iya komawa ba damuwa...........
"Kiyi min alfarma ko ta kaiki gida ne tunda har Baki da lafiya..........
"Idan aka ganni a motarka nace me? "Ka ganka kuwa ? "Taimako wani abune da addinin mu ya koyar damu ga mabiyan sa shin kana daga mabiyan ne da zaka taimakeni?
"To duhu da haske basa tarayya a wuri Daya Dole daya ke bawa Daya wuri idan haske ya bayyana to duhu yayewa yake don haka na gode da taimakon ka gareni
"Na sani amma haka Nan naji Ina son taimakon ki tunda muma namu addinin ya koyar damu taimakon Kuma Bai saka kiyayya ga sauran addinan ba indai ba naku adfinin ya saka muku kiyayyar sauran addinan ba. Kiyi hakuri ki shigo na saukeki nayi Miki alkawarin Babu cuta tsakanin mu haka kawai nake son taimakon ki
Azahiri ita kanta tana bukatar taimakon don Jin kanta take tamkar zai tarwatse Dole ma ta nemi abinda zai kaita gida don Bata sababa ga kuma yunwa da takeji wadda idan akasa tace zata tafi to ko shakka Babu sai dai akwashe ta amika gidan don haka ta sallama ta shiga motar yaja suka iso gida ya sauketa ya Miko Mata fakitin maganin ciwon Kai me tsadar gaske ta karba tana godiya