← Book details Uwar Gidana Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 19

Sashe 11

Uwar Gidana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Khadija kuwa fuuu tayi d'akinta don haushin Bada i'ta da yayi a gaban matarshi" Humaira tashi tati ta tafi d'akinta Ta zauna abakin gado kenan sai taji sallama tana lek'awa ta Window ta hango su "Aunty Maryam da " Aunty Murja sai Hamida. Murna ce tacikata ta tashi da saurinta tafito tayi musu sannu da zuwa.A lokacin ba kowa aparlon sai k'arar Tv a kunne,Suma sunji dad'in ganin k'anwar tasu saidai a lokaci d`aya suka had'a baki suna cewa"Humaira ciwo kikayine Kinga yadda kika koma kuwa,Suka zauna Suna k'ara tambayarta tace lah wallahi zazzab'ne kedamuna kwana biyu"Aunty Maryam tace Ke Humaira Kuma bakije asibiti ba sai kika zauna agida ciwonma zurfin ciki a keyimaine tace A"ah nasha panadol ne shiyyasa yanzu da sauk'i A'i.

"Hamida kuwa tace wallahi Humaira zurfin ciki babu inda zai kaiki,na amshi Juniour A hannunta shine tayi min takwara Maher Sunanshi sai Akecemai Juniour bayan tayaye twinsne ta haifeshi yaro maikyau dashi.Inata yimai wasa Nanfa muka shiga hira"Muna cikin hirarne " Aunty Maryam ta ke cewa ni kuwa Ina "Khadija naga shiru bata fitoba " Aunty Murja tace toh mu zamu shiga mugaidata kenan Tasha zamanta A'i naga"Humaira tana jin tahowarmu ta taso tazo muka gaisa KO i'tace shaha Rarrariya.

"Aunty Maryam tace A'ah A'i ba'ah haka Murja kidaina haka A'i k'anwarmuce A'i sai tadaina ganin girmanmu.duk wannan hirar da sukeyi "Hamida ba tace k'alaba saboda tana tayani kishi tasawa kanta KO zuwa gidan tayi i'dan batayi Mata magana ba to i'ta bazata yi mataba.

" Tunda sukazo"Khadija KO lek'ensuma batayi ba har kusan k'arfe 2:0 harnayi girkin Rana Ashe Yaya Maher bayan muntashi daga parlon shiryawa yayi yatafi Aiki saboda haushi ga "Huamirarsa tak'i bashi had'inkai.

" Aunty Maryam tacewa "Aunty Murja nikuwa" Khadija lafiya take kuwa,kafin su rufe bakinsu Sukajiyo sallamar"Baby da Aunty Hamida sunshigo Suna zuwa suka gaisa sai wani yamutsa fuska sukeyi,

"Khadija ce tafito tararsu " Aunty Hamida Tasha kwalliyarta cikin wani leshi'Humaira nakan hanya wacce i'tama tasheka kwalliyarta cikin Riga da siket na atamfa Holland tayi kyau sosai Hips d'inta yafito sosai gwanin ban sha'awa don tayi ramane,Khadija kuwa ganin Humaira na kan hanya ta bangajeta tayi baya"Aunty Murja tace ke baki da mutunci KO kinbige mutun Amman kamar kinbuge banza,ature ta kinfanmu munxo Amman Dan kin i'ya rainin wayo saida kikaga Hamshak'ai sunzo Sannan kika fito,Khadija tace sorry Aunty murja bansan kunzo bane Kinga su Sun sanar dani zasu zo shiyyasa.

*Ummu Maher ce*✍️

*Vote*

*Share*
and

*Comment*🗳️📧📨💌
[11/10 16:19] 💖Rabee'atu Ummu Maher💖: 💖💖💖💖💖💖
*UWAR'GIDANA*
💖💖💖💖💖💖

*By*.

*_Rabee'atu . B . Abdullahi_*
( _Ummu_ _Maher_ )

Whattpad Rabi'atu222s

*Page*45&46*

"Aunty Murja tak'ara kallon 'Khadija ta ce i'nagaya miki kibi duniya a sannu duniya cike ta ke da abubuwa Kala Kala Kuma duniya Wanda baizo bama jiranshi ta keyi.Aunty Murja ta ce Kinga Maryam, Hamida,Ku ta ho mutafi ta farayin gaba suka bi bayanta,Nima na bisu don in rakasu.

" I'na dawowa naji Aunty Masha'hudaa tana cewa hmm munafurci dodo maishi baza yaci ribaba"Baby tace A toh gaya Mata sai"Khadija tayi karaf tace ni wallahi"Aunty Murja ce ma naga tana wani bin bayanta i'nbanda munafurci ni da Yaya ta uwa d'aya uba d'aya sai anemi ayimaka munafurci'ita Maryam d'in da tazama dolenta basai taje wajenta ba.i'ta Kuma wancen shashar Hamida wai i'ta tana jin dad'i Ana wulakanta kishiyar "Ramlat shine ta kejin dad'i to A'i idan wani yayi Rawa an wasa kud'i to Kai KO kayi saidai kasha d'anbanzan duka.
Kawai gyad'a kaina nayi na wuce Ina mamakin hali irin nasu,Ina shiga daki nad'auko wayata naga kiran " Innarmu har sau biyu,Nayi saurin bin kiran Nata,tana d'agawa naji tace "Haba Mamana Ina kika ajje wayar Nace lah'Innarmu su Aunty Murja na raka kafin indawo sainaga kiran,tace toh daman i'nason yin magana dake 'Nace toh Inna inajinki,tace daman akan maganar y'ar uwarki" Khadija ne Dan Allah kuringa hak'uri da junanku kinji kici gaba da hak'uri kinji nace toh "Innah nagode sosai,tace to Mamana kigaida Maher din kinji Nace toh " Innarmu agaida "Babana tace toh zaiji" Mamana mukayi sallama na ajje wayar.

"Rayuwa na cigaba da tafiya kullum cikin bakin ciki nake gashi rash in lafiya ta ta dawomin namafarkin Ana saduwa dani.
Yauma Ina kitchen Ina girki Yaya Maher ya dawo na ajje girkin nayimai sannu da dawowa,Na'ajjemai abincinshi dayake Ni'ce da girki muna cikin cin abincin muna hirarmu don mundade rabonmu da wannan hirar,tun zuwan " Khadija saboda Narasa kan Yaya Sam.

Tana fitowa takaraso cikin wani yauki da yanga,tasaka wani less pinch colour,Ni Kuma Ina sanye da Arabian gown mai Dan karan kyau da sheki,da yane kaina da mayafinta,nayi kyau nayi shar Dani kamar ba"Humaira ba,Kallona takeyi tana wani hararata ta zauna da k'yar "Yaya kuwa baice Mata komai ba munata hira don KO kallonta ma baiyiba,A'i kuwa haushi yak'ara turnik'ke " Khadija tace mai sannu da zuwa ya juya yana mai cigaba da hira Dani yace Mata yauwa,munfara cin abinci kenan i'tama tafara cin abincin kawai sai ta tashi da gudu tana yunk'urin yin amai,Cikin tashi hankali na kalli Yaya nace mishi "Khadija daman bata da lafiyane yace oho'Nace kaje kagani mana'Yace toh Yatashi yabita lokacin da yashiga tayi amai sosai kamar zata amayar da kayan cikin ta ya taima kamata ta gyara jikinta.

" Bayan sunfito ne yake tambayarta daman bata da lafiyane'Tace A'ah yaune kawai ta kwanta yace zai Kira Mata likita"Bayan yafito ne Nake tambayarshi yajikin Nata yace dasauk'i Nace kakira Mata likita mana yace toh.

"Bayan gwaje gwaje da likita yayi Mata yagano tanada ciki na wata biyu'A'i Yaya Maher ya damki likitan cikin wasa yace da gaske kake Zan samu" Baby'Likita yace I'am show da gaske nake nanfa yaringa murna.saidai shidai yasan tun ranar da yaga tazamarmai "Humaira yayi mu'amala da'ita bai sake yi da'ita wannan shine ikon Allah.

"Humaira tana kitchen Yaya ya shigo cikin murnarshi yake fadamun " Cewar Khadija tanada ciki na wata biyu,duk da naji babu dad'i Amman saina tayashi murna sosai Ranar har dare Ina zaune sukuku ga ciwo ya isheni,har narasa yadda zanyi Kai duniya kenan ni Humaira Tunda nayi Aure ban ji dad'i ba har yau na rike kaina da yakeyimun ciwo,Amman nasan wataran sai labari.

*Kuyi hak'uri banida lafiyane shiyyasa nayi tyiping kad'an Sannan Dan Allah kuyi hak'uri kwana biyu bazan hau online ba*🙏🏻

*Ummu Maher ce*✍️

*Vote*
*Share*
And
*Comment*
[11/10 16:20] 💖Rabee'atu Ummu Maher💖: 💖💖💖💖💖💖
*UWAR'GIDANA*
💖💖💖💖💖💖

*_By_*

*_Rabee'atu_ . _B_ . _Abdullahi_*( _Ummu_ _Maher_ )

*My _Whattpad_ _Rabi'atu222s_*

*Page🔹47&48*

"Labarin Khadija Nada ciki ya cika dangi y'an uwa da abokan arzik'i" Momin Maher kuwa ranar kusan yini tayi agidan Ina d'akina ban fitoba Don ina tsoron masifar Momi'.
Yaya Maher yadawo har lokacin bata tafiba'don haka nayi sauri na fito don nasan zata i'ya cewa mai ban fito na gaisheta ba,don haka nasakawa kaina kome zatace saidai tace Amman zanje i'ngaidata ko don gudun surutun Momi,Ina fitowa Nasameta aparlon "Khadija tana ta zuba Mata shagwab'a wai i'ta mai ciki,Nagaidata na K'ara bata d'ago ta kalleniba balle insaka ran zata amsamin,koda na K'ara gaisheta Tunkafin in rufe bakina tayi wuf tacemun 'Toh'jikar nayu dolene saina amsa A'i kinsan nazo kikayi zamanki ad'aki wai ke munafuka KO ta Bari kiji bandamu da zuwanki KO rashinki ba banza juya wadda bata i'ya komai ba saidai taci tayi kashi'toh Allah yaso bake kad'ai ce Mace ba ga " Khadija nan ta nuna ta Sannan ta D'ora da cewa gatanan watan ta biyu agidannan gatanan da cikin ta Kinga nanda wata bakwai zamuyi d'a agidanan don haka da kizo da kar kixo duk Uwar Ubansu d'aya tashi kibani waje na daina ganin wannan fuskar taki irin ta mayu..

A guje na tashi na tafi d'akina Ina faman rusa kuka mai k'una A'yanzu gidan Yaya ya Fara fita araina saboda Mahaifiyarshi,ta tsaneni tsana mai yawa,Adaidai lokacinne Yaya Maher ya shigo gidan don dama ya tsaya yin Waya da abokinshi "Doctor Bashir,Akan wani aiki da zasujeyi k'asar 'India' shiyyasa ya Dad'e bai shigoba Yana shigowa ya ga motar " Momi saida gabanshi ya fad'i don yasan halin Momin nashi yanzu zata hargitsamai gida.don haryanzu baiyarda a wulak'anta "Humairanshi ba saboda i'ta ta musammance acikin rayuwarshi.Yana shiga alokacin Momi ta fito zata tafi" Khadija ta rako Momi,Sukayi kicib'is akan hanya Yaya "yace A'ah Momi badai tafiya zakiyi ba tace eh tafiya zanyi daman nazo duba jikin " Khadija ne da Kuma abun Alkhairi da naji,to Allah yasauketa lafiya ya kad'e i'don mahassada don y'an bak'in ciki su ne sukafi yawa,koda Maher yaji ta dauko zance maiyawa Saiyayi saurin cewa"Momi ya Dady kwana biyu haryanzu baidawo bane tace A'i Dadynku sai next Month wannan Karen ya Dad'e yace oky Sukayi sallama ta tafi gida.

*** *** ***
Haka rayuwa taci gaba da tafiya yau fari▫️gobe bak'i▪️,Yanzu cikin "Khadija yanada wata Biyar Amman yanda kasan maiciki wata Tara bawai don girmanshiba A'ah sai don Iyaye da Son jikinta don yanzu babu abinda ta keyi sai Bacci,Yaya Maher ya sameni ad'aki Ina linke kayana yazauna yace A'ah My UWAR'GIDANA,Linki akeyine Nace " eh'batare da na kalleshiba don yanzu haushi yake bani Akwai ranarda bazan manta da i'taba ranar i'na period marata nayimun ciwo Ranar ba nice da girkiba "Khadija ce da girki don ta Dad'e daman bata girki saidai agirka taci wai i'ta maiciki,Sannan Kuma ahaka miji ya kwana adak'inta Amman saita k'iyin girki saidai inyi,idan nayima saikaji tace i'ta Dan malele, fate,take so tsirfadai Kala Kala,Yaya kuwa yayi biye Mata koda b'ata raina nayi saiyacemun Ina bak'inciki da " Khadijane,to wannan kenan toh ranarma Ina period ne marata keyimun azababben ciwonda kuka ne kawai banyiba Amman nakadai nasan abunda yake damuna,Yashigo yasemeni yace lafiya kuwa,Humaira kunsan ni dai da zurfin ciki kawai sai nace masa bakomai'Yashafa k'eyarshi yace daman"Khadija ce ta keson D'an wake shine nace Bari nagaya miki kidafa mata'dakyar na d'ago kaina Nace mai'Yaya bazan iyaba cikina ciwo yakeyi saikawai naga yacemun Amman"Humaira yaushe kika Fara min karyane ehe yanzu i'ntambayeki kice lafiyarki lau Amman yanzu kihau murkususu haba "Humaira kiyi koda donni mana bakya gananin tana dauke da cikina haba " Humaira...Tunkafin yakarasa maganar nayi wuf da sauri sauri na shige band'a ki narufe.
Chapter 11 · 0% Book details