← Book details Uwar Gidana Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 19

Sashe 1

Uwar Gidana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

[*UWAR'GIDANA
💖💖💖💖💖

*STORY &WRITTING*
(By Ummu Maher)

*🖊️⚔️Alkalami Yafi Takobi Writter's Association*⚔️🖊️
*(A.Y.T.W.A)*
*Bismillahir_Rahmanir_Rahim*

"Inamika gaisuwa ta ga Yar uwa *(Nabeeha Aminu)* Da Yar'uwa *(Nabeela Dikko)* da Yar Mutan Dikkawa.Da yan uwa da abokan arziki.wannan littafin gaskene ma,ana true life story.

🅿️0️⃣1️⃣

******************** "Sauri Nake yi sosai kamar zan Fadi,Hamida Nagani Narankayo baki har kunne nace wai Innar mu tahaihu tace mun ta haihu "Yamace kuna kama da,ita wlh nayi dariya harsaida dunpull dina yalotsa.Nashiga daki dagudu nahaye KAN CINYAR Innar mu,"Tace ketashi karki karyani,Natsirawa jaririya ido ina kallo gidan mu yacika dayan uwa ana taya Innar mu murna,Saboda shekarar Inna takwas rabonta da haihuwa.Ammi tashigo rikeda kunun kanwa daya sha kayan kamshi sosai,gatuwon alkama damiyar ugun. tasha nama da manshanu,gakunun aya maidadi,babu Wanda ba,ah bani nashaba."To ranar suna Yarinya taci aminatu sunan ammi."Wacece ammi makota muke dasu wacce tazama aminiyar "Innar mu,wacce mijinta yake aminin "Babanmu tun yarinta.sun shaku sosai Wanda tunda muka taso basu taba koda cacar bakiba,mu biyarne wajen Wanda Ayanzu Muka zama shidda "Innar mu akwai babban mu shine Yaya Mustapha,Aunty Maryam,Aunty Sha,awa,Yaya Nura,Saini mai bakin baya Aishatu Humaira mai babban suna sai Amina Mai sunan Ammi.
"Ammi Nada Yaya takwas babbansu,Yaya Mukhtar,Yaya Ana's,Aunty Murja, aunty Bilkisu,aunty Aisha,Aunty hapsat,sai khadija,sai Bashir shine Auta."Wanda tare suke haihuwa da ammi amma daga kaina sai Haihuwar ta tsaya mata.Andauka tadaina haihuwa saikuma gashi Allah yayi tahaifi 'Autarmu aminatu.Amma aunty maryam tayi aure aka hadasu su hudu akayi musu aure Aunty maryam aunty,sha,awa,aunty murja,aunty bilkisu,sai Yaya mukhatar Yakai kudin aure.aunty Hafsat shekara daya tabani dawa tanni,Wanda nikuma nabawa khadija shekara Biyu.saidai aduk yayan babu wacce akeso sama dani "Humaira,

"Dani da khadija sai muka zama kanmu daya ita tanada tsayi Nikuma matsa kai ciya ce. "Khadija Fara ce tas,Nikuma wankan tarwada,"Saidai duk Wanda yagan ni saiya kara kallona,Inada hancina siriri dabikina dankarami ga idanu ga dun full, Gni yar duma duma domin INA da wani hips mai firgitarwa domin hips dina Yanada fasali sosai,Tayadda inata fiya mazaunai na aikinsu. ayanzu INA da shekara goma amma inada cikar halitta sosai komai cas ,Saidai banida gashi Wanda yan gidan mu suke cemun kwakwi doce ,Yayyina sunfini gashi sosai,"Yayan ammi ma sunada gashi,saidai khadija tana matukar kishi dani sosai Wanda iyayenmu sungane hakan tunda muka taso bamu taba shiri da khadijaba nikuwa ko ajikina."Inasauri zanshiga gun ammi khadijace tataho tasiyo wa ammi kankara lokacin azumini tana gani na tazubamin kankarar akaina Nasaki kara, "Daidainan Abba yafito " Koda Yaga Abinda yafaru Yayi Kan Khadija.
'Aiwani mari yayi mata harsau uku sannan yafara dukanta,Ammi dake kitchen tafito asukwa ne "Nikuwa inda nafadi Ashe suma nayi sabida Sanyin kankara,"Ammi tayo kaina tadau keni takaini daki tadebu ruwa maidan dumi tawatsamin nayi Fir gigit "Natashi khadija kuwa guduwa tayi gidan Momi. Abba yace narasa wacce irin Yarinyace yanzu tana inane tace nasan tagudu gidan momi,
"Momi kanwar ammi CE Wanda take aure (G.R.A)Mijinta mai kudin gaskene tana da Yaya hudu Nafarko Shine Yaya "Maher ,sai Aunty Masha huda sai,Hassana da Hussaina sune sa,anninmu."Wanda kwata kwata batasan alakar Ammi da Innarmu sam."Ammi tace wlh saina kusa targada yar,iskar yarnan Nikuwa nayi lamo jikin Ammi ni ba mutun ce mai Fadaba Sam.Sam banida Fada saidai inada tsokana"Saida akasha ruwa Ammi tarikoni tadawodani saidai ba"Tafadi abinda yahadamuba.
Kubiyoni don jinkarashen.
❤️🧡💛💚💙💜🖤ummu maher🤍
✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻
[11/10 16:13] 💖Rabee'atu Ummu Maher💖: 💖💖💖💖💖💖
*UWAR'GIDANA*
💖💖💖💖💖💖
*STORY & WRITING*
( By Ummu maher)

*🖊️⚔️ Yafi Takobi Writter's Association⚔️🖊️*
*(A.Y.T.W.A)*

*Bismillahir Rahmanir Rahim*

🅿️2️⃣3️⃣4️⃣5️⃣

***************
"Saidanayi kwana biyar ina zazzabi aranar na shida nafito mukayi karo da mutum Naji tsoro harnayi hanyar gida da gudu aka janyoni zansa kara akarufemun baki na yahaskoni da touch light nace LA, "Yaya Maher yace na,am 'uwar gidana,Nasa ka Dariya,
yace Ashe bakijin dadiko "Na ce eh 'Yace sannu Uwar gidana,muna tafe muna hira koda muka je store din kayaYatilo dayawa kuma bai amshi kudina muka taho dai layinmu nagaHamida aminiyata 'Tace ah kaida uwar Gidane rangida Yace wlh aminiyarmu 'Bayanma UWAR'GIDANA najin kunyata 'Komai Sai Arufe fuska muna magana saiga khadija Tazo wucewa, Aituni nayi hanyar gida inajin tsoronta kamar mala'ika Hamida Ta janyoni kedai ko sokuwa wlh daga ganin kanwarki saigudu 'Yaya Maher yace saboda me?Hamida 'Tace Yaya kaga khadija Tsironta Humaira takeji kwanaki da aka Aikemu shago baka dukan Datayimata ba 'Yamatso kusa da inda Khadija take Saida ya Mareta Dagudu tayi hanyar gida, dominshi bai iya dukan mace ba wannan ma don' akan UWAR'GIDANA ne shiyyasa.Da yatsa yace ke yar'iskace yayarki kike duka muna fuka kullum saina Ganta a gidan Momi tana zuwa gulma.Tobari kiji ko kallon banza tayi miki aminiyarmu kifadamun,Aituni tayi hanyar gidan momin Maher donkai kara. "Momi tace Maher Babban soko ne ace mutum bai kaunar yar,uwarsa sunshanyesa da anyi magana shi Mara kunya yace UWAR'GIDANA banza shanyayye itama adda amina damijinta sunshanyesu mst taja tsaki,Banza yaga diri kamar anhura balo yamanne dondai ita bafarace kamar kuba da daga India za,ace tafito sabida kyau.shegiya yarmayu,momi nata sababi "Tace tashi sai Allah yakaimu bayan sallah kyakoma don Naga su iyayennaki sunfi sonta yar mayu.

***************
"Yaya Maher yana matukar sona sosai tareda kyaunata'Nima INA kaunarshi sosai idan banganshiba banjin dadi,Iyayenmu sunyi murna sosai suna da burin su Aurardani dawuri sabida inada halitta tabanmamaki ko hips dina kadai abin kallane samari kuwa kota ina suna zuwa amma 'Nace sai Yaya maher .akwai Dan Yayan Inna Ammar sunanshi "Dan Babban yayantane Namiji akabiya musu karatu Kasar "Germany yatafi to tafiyar dayayi ne nasamu sauki Donda kullum saiyazo gidanmu Waiyazo Hira Wajen 'Inna Babu Damar Nafito saiyayi Tabina Da kallo Kamar wani Maye
"To Yaya Maher yayi tafiya zuwa kasar Rasha Donyin Wani wani course dominshi Likitane Yaro matashi kenan.Likitan Zuciya Don Babu Wanda Baison shiba Fannin Likitan Xuciya Kwararrene Awannan Fannin.

**************
"Muna fira da Hamida tace kin son Wani Abu 'Nace A'Ah Saikin Fada? "Yayan kifa yanaso Nace wanne tace Yaya mustaphaMana "Nace ke yakai kudifa tace oho yadai cemun yanaso nima kuma haka to yanzu yazaiyi dasu Baba da abba.tace toh "Ke damanfa Nane mai tayi Taga Dan saurayi Mai Kyau kuma Wallahi Ba sonta Yakeyiba "Asirine kawai sukayi"Yayarsu ke fadawa Hajiyarmu kinsan su biyune Matan Gidan "To babbar yar Uwargidan itace tafada mana "Nace kai tomeye na asiri akan Namiji .Haka Dau mukata hirarmu saiga "Yaya Mustafa yayi kyau cikin "Suit baki da fari gashi farine tas kamar zaki taba jini yafito Yana aikin bankine baida Da farawaba "Wanda yayan Innarmu yasa Momai ayanzu shine dan majalissa. Kallon kallo suka shigayi da "Hamida yaKallo Inda Nake "Yace mun ke fita Natashu Nafito tsakar gida ya "Kalleta yace babyna kwana Biyu "Ko Hajiyarmu Taboyekine tayi dariya Tanasonshi sosai "Tayi saurin cewa Yaya wai mubiyu zaka aura "Yace a,ah kece UWAR'GIDANA "Ashe Yaya Mystafa Harya fadawa su baba baya Sonta sukace su ba iyayen banza bane. saidai "yace tunda sun dage shikkenan ammafa zai auri wacce yakeso sukace sunji,Suna ta firarsu tamasoya,Nima natuno da masoyina abin alfaharina gashi ba a yarda inrike wayaba.
"Yaya mukhtar yayan khadija shikuma Yayar Hamida yakeso yakai kudi.

***********
"Yau Yaya Maher zai dawo inata faman shirina ammi tace "Khadija shiga kitaya Humaira aiki Nantace toh, Kamar abin Arziki, "Tunda Na ganta naji kamar inzura dagudu amma babu damar haka,Nafito daga Kitchen din don inbata Waje "Khadja tazubamin tsu TSA Datake Sunad bishiyar Umbrella Takanyi Tsutsa Harsu Fado. "Nikuma Bansaniba bayan fried rice din tayi Tace inbada flask azuba, Tayi Na dau ko Mata Nabata Jikina Yana Rawa. Sannan Nayi Su Lemoka Kala Kala.Kalu Balenku Mata Kunga Sai Gashi Yanmata Ma Sunayiwa Saurayinsu Abinci Mai Kyau Musamman Na Insunsan Sunyi Tafiya.Saikiga Wacce "Macen Kullum sai miji Harya dawo Baki Kammala Mai Abincin Tarbar shiba.To Gwara ni gyara Don Idan Baki gyraba Wataran Wata Tagyaramai.

"Lemuka masu tsada nasiyo cake Babbba Maikyau Maidauke da Sunana Danashi,Nayi kyau cikin Riga da siket "Wow naji anfadi koda najuya sainaga aunty Sha,awa Ce Nakan Kameta INA murna gata da Yaronta Yayi Wayo Sosai Wanda Muke Cemai Abil Khairi,Wato Baban Alkhairi. Gata kuma da Tsohon ciki "Duk yayyina ina Sonta Sosai Domin ita Ma Tanasona. Tace kai gaskiya azubomun abincinnan nace aunty na "Yaya Maher ne fa tace sai Anzubo mun Wallahi "Natashi nadauko flask nabude nazuba mata tace 'ah ah kasan yafi kayan hadi nazubamata tadauki spoon saime sai ga tsutsa Dsame Irinta Bishiyar Gidansu "Khadijace tajefar dafarantin tace mezangani,tace wlh Aunty bansaniba, "Tace meye haka kedawa kukayi girkin, 'Nace Khadija Tace toh koda naji ita Khadija Wacce yar,isakace sai Mutun Zaiyi Magana "Inna tahana 'Ni nagaji wlh,Tace Kinga Tashi Babu Komai Kanta Tayiwa.Babu Komai kinji kanwata yihakuri Babu komai nashare hawayena takara "Fesamun turare amma had lokacin INA kuka Yaya Maher Yashigo Suna gaisawa Da Inna,Tace Suna Daki Itada Sha,awanatu "Yashigo da sallama turus yayi ganina AHaka Kuma Haryanzu Bandaina Kukaba Nayi Saurin daukar mayafina zansa yace UWAR'GIDANA lpy Kuwa? Aunty Sha,awa "Tace Babu komai "Yace Haba Aunty lpy Kufadamun....
💚💛💜🖤🤍💗By Ummu maher
🧡💙💜🤎❤️

✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻
[11/10 16:13] 💖Rabee'atu Ummu Maher💖: 💖💖💖💖💖💖
*UWAR'GIDANA*
💖💖💖💖💖💖
*STORY& WRITING*
(By Ummu Maher)

*🖊️⚔️ Alkalami Yafi Takobi writter's Association⚔️🖊️*

*(A.Y.T.W.A.)*

*Bismillahir -Rahmanir- Rahim*

🅿️ 6

***************
"Aunty tafada mishi Abinda Yafaru "Nan dai yaringa bani hakuri,Na ajje mai kayan ciye ,ciye muna hirarmu,Innarmu Fita Gaisuwa Nan Mako tanmu tadawo suka Kara gaisawa. Narakashi hanya yatafi gida INA mai byebye.
"Ankawo kudin Aurena "Nida Hafsat Aranar yakirawoni mukasha fira,Muna waya Innarmu "Tace tashi Humaira in aikeki Gidan kaka"Nace to Nakashe Kiran na Tafi. Inazuwa ammar yana fitowa nagaishe shi ya amsa dakyar INA ganinshi har nashiga yana kallona,Inazuwa nayi matashi da cinyar kaka"Tace keni tashi karki karyani namika mata sakon tace kai Gorone Da Sweet Alawa. Tace Kai Aikwa Naji dadi wlh Allah yasa ayi damu Amin. Naga Auren Mai sunana Narufe Fuskata Don Kunya. "Kaka itace mahafiyar Innarmu tana sona sosai,Ita Yaran Su Shine shuwa Arab CE Baban Inna Kuwa Shikuma Bahaushe ne,Nan na zauna sai dayamma Natafi Gida.
Chapter 1 · 0% Book details