Sashe 2
Shin So Daya Ne Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta feffesheni da turare,aka fito dani xuwa bangaren Abba inda anan ne za'a mana fada da nasiha.Gida ya rud'e da rangad'e rangad'en guda.Koda na shiga falon na tarar har Suhaima ta rigani isa,zaune take akasa kusa da kafafuwan Umma,ta kifa kai asaman cinyar Ummar tana rera kuka ahankali ayayin da Umma ke dan bubbuga bayanta alamun rarrashi.Can gefensu Abba ne zaune sae karkada kafafuwa yake yana meh fesar da iskan bakinsa.
Ganin shigowar Fadima da Kuma kukan da itama take rerawa ya saka Umma saurin mik'ewa don bazata juri tsayawa yin bankwana da 'ya'yan nata ba.
Hanyar fita ta nufa alokacin da taga Fadimar ta sami gu ta zauna akasa akusa da Abba.
"Haba! Kareemah dawo ki sallami 'ya'yanki mana,ki dawo kiyi musu fatar alheri acikin sabuwar rayuwar da zasu shiga..... "
Sabon kuka dukanmu muka rushe dashi har Umman,dakyar ta dawo ta nemi gu ta zauna.Abba ya shiga lallashinmu da Kuma ban baki,dakyar muka haqura mukayi shiru don sauraren nasiharsa agaremu.
Abba yayi gyaran murya sannan ya soma jawabinsa"Alhamdulillah! Alhamdulillah! godiya ta tabbata ga mahallicin sammai da kassai,mahaliccin dabbobi,aljan,mutum da duka komai meh rai ko mara rai.Na godewa Allah da ayau ya bani damar sauke nauyin daya rataya bisa wuyana amatsayina na mahaifinku na ganin na aurar daku ga nagartattun mazaje na gari,Fadima hakika nasan ko kadan ban kyauta miki ba dana hana miki auren zab'inki,amma ina son ki san cewar ko kadan banyi kuskure ba,don idan baki manta ba,ah addinance wajibi ne iyaye su zabarwa 'ya'yayensu abokanan rayuwa na gari,don haka karki ka laifina don na aurar dake ga wanda ba zabinki ba,Wallahi Fadima ina meh tabbatar miki da cewar watarana keda kanki zaki zo kice Abba nagode da zab'inka,ashe zab'inka alheri ne agareni.........."
Haka de Abba yayi ta mana fada da nasiha kan mu riki aurenmu da kyau Kuma mu baiwa auren muhimmanci sosae,mu bi mazajenmu sau da kafa sannan kuma mu k'yautatawa danginsa.Haka mah Umma itama tayi mana fad'a sosae.Ashe wai wasu acikin danginmu wayenda suka sanni tare da Leedar sunyi ta mamakin yadda akai ya koma mijin Suhaima,Abba de ce musu yayi haka Allah ya tsara tun fil'azal cewar Suhaimar itace matarsa amma ko kadan be labarta masu komai na game da shashancinmu ba.
Su goggonnina,mamannina da wasu kawunnina duk se da suka shigo suka mana fada da nasiha meh ratsa xuciya.Ni da Suhaima babu abinda muke illa kuka.Daga k'arshe akayi waje damu don har 'yan daukar amarya hadda na Suhaima sun iso.Sae da akayi da gaske kafin arabamu da su Abba da kannena.
Abba yace baya son tarkacen mutane da nufin kai amarya,sam an bar yayin nan.Mama Jamila,Anty Hajaar,Mama Sadiya cousin dinsu babanmu,sae kuma kawayena biyu,Ash da zuwairah kadai akace zasu bini.
Ita kuwa Suhaima mutane har Kusan goma ne wai zasu bita tunda nan cikin Zariar za'a kaita kuma ayau din zasu komo,kuma duka kawayenta suma zasu bita.Nayi kuka sosae,sae nake ganin kamar an nuna min rashin gata ne.
Ni da Kawayena muka shiga mota daya,ayayin da dayar motar kuma su mamanni ne aciki. Sae gud'a ake tayi har motocinmu suka bar kofar gidan.....
A/N
Hey Fadima sa'ad Mainasara welcome to Nakowa's family!!!
Ina kuke tunanin za'a kai Fadima? Family house ko kuwa gidan Baba Mu'azzam za'a sauketa? Ku biyo.
Sorry guys! chapters na kashi biyu zasu dunga zuwar muku a little bit scanty don novel din ya Kusan zuwa karshe & I want the chapters too be a little bit much..... Yeeeepeeee shout out to Hafnan! Her first novel is about rounding up!!! 💗💗
©QUEEN CE©
*💘SHIN SO DAYA NE? 💝*
*MALLAKAR:HAFSAT AL-MUSTAPHA*
*WATPADD:HAFNANCY💞*
*KASHI NA BIYU:RIKICIN KARSHE*
🌼BABI NA BIYU🌼
*💧💧💧KAI AMARE💧💧💧*
💧💧 💧💧
💧 💧
*page 3-6*
Har muka isa kanon ban mah san mun iso ba sabida tun shigata motar,cigaba nayi da sana'ar kukana,Ash kuwa sae aikin rarrashina take don ni da ita kawai muke xaune agidan baya,ita kuwa Zuwairah gidan gaba ta xauna wacce jefi-jefi suke d'an taba hira da meh tuki wanda na lura kamar yana cikin abokan ango.Shi din mah yayi rarrashin duniyar nan amma naki nayi shiru,can yace arabu dani kila so nake shi angon nawa yazo ya rarrashi abarsa da kansa,abin ya baiwa su Ash dariya,ni kuwa haushi maganar tasa taban kamar na tashi na kifa masa lafiyayyun mari.
Mubarak ne ya fad'o min arai,yanzu shikenan mun rabu kenan? Yanzu baza'a taba k'irana da matar mubeen ba kamar yadda nake ta burin hakan sae matar Mahmood Nakowa?abin mamaki mah wai dangin mijin nawa ah kanon suke,kada watarana fa mu had'e dashi.... Wani b'angaren xuciyata kuma yace"xancen banza keda mah ah Zaria zaki zauna? Sannan meye naki na wani damuwa akan mutumin da baya qaunarki,mutumin da kuma sam be damu da rayuwarki ba?
"Toh! amaryar Nakowa mun iso,sae ki had'iye kukan naki ya isa hakanan kinga gidan surukai xamu shiga kada suga kina koke-koke su aza ko surukar tasu ba jaruma bace...... "
Ash ce ta katse min gajeriyar tunanina alokacin data bud'e min kofa da k'yau wai na fito,sae asannan na ankara da cewar har mun iso ban sani ba.
Sannu ahankali na sako kafafuwana waje tare da dire su akasa,wani daddad'ar ni'imtaccen iskar yammacin nan ne ya soma min barka da xuwa.fitowar tawa tayi daidai da wayar da wannan meh tukin keyi wanda ayanzu nasan sunansa don naji Zuwairah ta ambaci sunan wai *'KHALEED'*.
Cewa yayi"Kai dan iskan ango kana ina? gashi fah mun iso amma anki bamu amaryar..... "
Saurarawa naji yayi,can yace"Na taba maka irin wannan wasar ne? Ka yadda dani anki bamu ita wai sae kaje da kanka.... "
Ya sake saurarawa,can ya d'an d'ara yace"Kai wasa nake maka mallam karka min hauka,ga amaryarka nan mun kawo maka ita,tasha kuka kuma har yanxu tana kan yi ne sae kazo ka lallashi abarka........ "
"Ayyyirihiiiiiiii,lale marhaba da zuwan amarya.... " rangad'e rangad'en gudar dangin mijina ne ya hana min jin k'arshen maganar Khaleed da mijina.Ni kuwa jin sun nufoni ya saka na k'ara jan mayafina gaba don kada suga fuskata.
Wata 'yar matashiyar budurwace naga ta rungumeni tana fadin"Oyoyo!amaryarmu sannu da xuwa...... "
Mama Jamila ce ta rad'a min magana akunne,cewa tayi"Ki shiga da kafar damarki tare da bismillah,haka kuma xakiyi idan aka maidaki can gidanki.... "
Daga mata kai nayi alamar naji jawabin nata,daga haka naji wasu mata su wurin uku suma sun rungumeni kamar zasu kada ni akasa suna min sannu da xuwa har muka shige gidan.
Wani daki aka saukemu aciki wanda muka ji wani daddad'ar kamshin turaren wuta ya mana maraba da xuwa,gaskia ba laifi suma kanawa akwai son kamshi.Maganar gaskia ba k'aramin karramamu akai ba,nima sae naji na d'an saki jikina amma har xuwa wannan lokacin ban yaye mayafin kaina ba,ina nan lullub'e aciki kamar wata munafuka,lokaci xuwa lokaci nake dago kai na d'an saci kallon mutane.
Cikin k'ank'anin lokaci muka ga an cika mana gaba da kayan ciye-ciye da shaye-shaye.Mama Sadiya ne suka dan taba amma babu yadda basuyi dani ba amma naki ci.Ce musu nayi ak'oshe nake.Ak'arshe dai ruwa kawai na d'an sha.
Mama Jamila ce tace"Yarinya idan zaki mah saki jiki toh tun wuri ki saki don anan zamu barki,gobe idan Allah ya kaimu komawa gida abinmu xamuyi..."
Juyawa tayi ga Mama Sadiya tace"Sadiya hanzarta ki gama cin abincin ki min rakiya xuwa gidan wata k'awata dake nan jambulo,bazamu jima ba..... "
"Toh Addah... "acewar Mama Sadiya don Mama Jamila na gaba da ita.
Ni kuwa wani sabbin hawaye naji sun ziraro min saman k'unci,tayaya xan soma rayuwa agidan wasu bayan na sab'a da namu?taya mah xan soma had'a shimfid'a daya da wani k'aton gardi amatsayin mijina?
Yaye min mayafi naji anyi ana fad'in"Ai kya bari muga fuskartaki muga ko kin fini kyau koh? "
Ji nayi an fashe da dariya,ni kuwa gabana ne naji ya yanke ya fad'i,dakyar na iya d'ago kai ina duban wacce ta yaye min mayafina,ido hudu nayi da wata tsohuwa wacce kana ganinta kasan ta dad'e ana cin sallar idi da ita.Sae dai ba'a wani gane tsufanta don jikinta meh k'yau ne.
Tace"Masha Allah!.. Ashe dai megidan nawa balarabiya ya zab'o mana shiyasa yake ta rawar kafa da dokin auranta..... "
Aka sake fashewa da dariya akaro na biyu,ni kuwa d'an murmushin leb'en baki ne kawai ya sub'uce min,atake anan na gane cewar wannan tsohuwar kakarsu ce.
Tace"Amarya share hawayenki,don ni dake xamuyi zaman lafiya idan da hakan kika zo,idan kuwa da akasinta kika zo,toh nima nan uwargida ashirye nake...... "
wasu 'yan mata ne naji sunce"sae kakus! Kakaaa rigima.... " aka fashe da dariya.
Haka dai tayi ta mana barkwanci da wasannin wanda atake anan naji kawai tsohuwar ta shiga raina.Su Mama Jamila kuwa suna gama ciye-ciyensu suka sa kai suka fice xuwa unguwar da suka ce xasu,muka rage daga ni,Ash,Zuwairah sae kuma Anty Hajaar wacce ga dukkan alamu jininta ya hadu dana Kaka rigima,don sae hira suke ta xubawa.
Ba'a wani jima ba muka ji an soma k'iraye-kirayen sallar magrib,daya bayan daya muke shiga bandaki muna dauro alwala.
***
Itama Suhaima anata b'angaren an musu tarban mutunci,sosae aka karramasu.Reedah itace wacce ta soma rungumota,ta rad'a mata magana akunne"Oyoyo sahibata,barka da xuwa,yau Allah ya cika muku burinku ta mallakar junanku,Suhaima dear welcome home as matar yayanah...... "
Ita kuwa Suhaimar murmushi kawai tayi abinta tana meh jin wani irin farin ciki mara misaltuwa na ratsa xuciyarta.
Leedar da Engr. bazan iya kamanta muku irin tsananin farin cikin da suka tsinci kansu aciki ba na ganin ayau sun mallaki 'the women of their dreams'.Bama kamar Mahmood wanda jinsa yake kamar Zaynab d'insa ce ta dawo.
***
"Anty Fadima inji Yaya Mahmood wai na kawo miki wa'ennan kayan ki saka wai xuwa qarfe takwas za'a taho ah daukeku xuwa reception...... "
Hafeezah 'yar baba Mu'azzam ne ke yiwa Fadima wannan maganar wacce take kusan sa'ar su Suhaima.
Kokarin magana nake sae naji Ash ta rigani,cewa tayi"K'anwata zubasu saman gado yanzu xata shirya kinji? "
"Toh.. " kawai tace sannan ta zubasu saman gadon dakin ta fice.
Ina gama ganin ficewarta na dubi inda Ash ke xaune nace"Sannu sarkin felek'e da iyayi,ina fatar da kika amshi wannan kayan ke zaki sakasu kuma ki bisu donni yadda kika ganni nan babu inda zani.... "
Zuwairah ce tayi saurin taran numfashina"Haba babe ya kike neman kwafsa mana ne?"
Ganin shigowar Fadima da Kuma kukan da itama take rerawa ya saka Umma saurin mik'ewa don bazata juri tsayawa yin bankwana da 'ya'yan nata ba.
Hanyar fita ta nufa alokacin da taga Fadimar ta sami gu ta zauna akasa akusa da Abba.
"Haba! Kareemah dawo ki sallami 'ya'yanki mana,ki dawo kiyi musu fatar alheri acikin sabuwar rayuwar da zasu shiga..... "
Sabon kuka dukanmu muka rushe dashi har Umman,dakyar ta dawo ta nemi gu ta zauna.Abba ya shiga lallashinmu da Kuma ban baki,dakyar muka haqura mukayi shiru don sauraren nasiharsa agaremu.
Abba yayi gyaran murya sannan ya soma jawabinsa"Alhamdulillah! Alhamdulillah! godiya ta tabbata ga mahallicin sammai da kassai,mahaliccin dabbobi,aljan,mutum da duka komai meh rai ko mara rai.Na godewa Allah da ayau ya bani damar sauke nauyin daya rataya bisa wuyana amatsayina na mahaifinku na ganin na aurar daku ga nagartattun mazaje na gari,Fadima hakika nasan ko kadan ban kyauta miki ba dana hana miki auren zab'inki,amma ina son ki san cewar ko kadan banyi kuskure ba,don idan baki manta ba,ah addinance wajibi ne iyaye su zabarwa 'ya'yayensu abokanan rayuwa na gari,don haka karki ka laifina don na aurar dake ga wanda ba zabinki ba,Wallahi Fadima ina meh tabbatar miki da cewar watarana keda kanki zaki zo kice Abba nagode da zab'inka,ashe zab'inka alheri ne agareni.........."
Haka de Abba yayi ta mana fada da nasiha kan mu riki aurenmu da kyau Kuma mu baiwa auren muhimmanci sosae,mu bi mazajenmu sau da kafa sannan kuma mu k'yautatawa danginsa.Haka mah Umma itama tayi mana fad'a sosae.Ashe wai wasu acikin danginmu wayenda suka sanni tare da Leedar sunyi ta mamakin yadda akai ya koma mijin Suhaima,Abba de ce musu yayi haka Allah ya tsara tun fil'azal cewar Suhaimar itace matarsa amma ko kadan be labarta masu komai na game da shashancinmu ba.
Su goggonnina,mamannina da wasu kawunnina duk se da suka shigo suka mana fada da nasiha meh ratsa xuciya.Ni da Suhaima babu abinda muke illa kuka.Daga k'arshe akayi waje damu don har 'yan daukar amarya hadda na Suhaima sun iso.Sae da akayi da gaske kafin arabamu da su Abba da kannena.
Abba yace baya son tarkacen mutane da nufin kai amarya,sam an bar yayin nan.Mama Jamila,Anty Hajaar,Mama Sadiya cousin dinsu babanmu,sae kuma kawayena biyu,Ash da zuwairah kadai akace zasu bini.
Ita kuwa Suhaima mutane har Kusan goma ne wai zasu bita tunda nan cikin Zariar za'a kaita kuma ayau din zasu komo,kuma duka kawayenta suma zasu bita.Nayi kuka sosae,sae nake ganin kamar an nuna min rashin gata ne.
Ni da Kawayena muka shiga mota daya,ayayin da dayar motar kuma su mamanni ne aciki. Sae gud'a ake tayi har motocinmu suka bar kofar gidan.....
A/N
Hey Fadima sa'ad Mainasara welcome to Nakowa's family!!!
Ina kuke tunanin za'a kai Fadima? Family house ko kuwa gidan Baba Mu'azzam za'a sauketa? Ku biyo.
Sorry guys! chapters na kashi biyu zasu dunga zuwar muku a little bit scanty don novel din ya Kusan zuwa karshe & I want the chapters too be a little bit much..... Yeeeepeeee shout out to Hafnan! Her first novel is about rounding up!!! 💗💗
©QUEEN CE©
*💘SHIN SO DAYA NE? 💝*
*MALLAKAR:HAFSAT AL-MUSTAPHA*
*WATPADD:HAFNANCY💞*
*KASHI NA BIYU:RIKICIN KARSHE*
🌼BABI NA BIYU🌼
*💧💧💧KAI AMARE💧💧💧*
💧💧 💧💧
💧 💧
*page 3-6*
Har muka isa kanon ban mah san mun iso ba sabida tun shigata motar,cigaba nayi da sana'ar kukana,Ash kuwa sae aikin rarrashina take don ni da ita kawai muke xaune agidan baya,ita kuwa Zuwairah gidan gaba ta xauna wacce jefi-jefi suke d'an taba hira da meh tuki wanda na lura kamar yana cikin abokan ango.Shi din mah yayi rarrashin duniyar nan amma naki nayi shiru,can yace arabu dani kila so nake shi angon nawa yazo ya rarrashi abarsa da kansa,abin ya baiwa su Ash dariya,ni kuwa haushi maganar tasa taban kamar na tashi na kifa masa lafiyayyun mari.
Mubarak ne ya fad'o min arai,yanzu shikenan mun rabu kenan? Yanzu baza'a taba k'irana da matar mubeen ba kamar yadda nake ta burin hakan sae matar Mahmood Nakowa?abin mamaki mah wai dangin mijin nawa ah kanon suke,kada watarana fa mu had'e dashi.... Wani b'angaren xuciyata kuma yace"xancen banza keda mah ah Zaria zaki zauna? Sannan meye naki na wani damuwa akan mutumin da baya qaunarki,mutumin da kuma sam be damu da rayuwarki ba?
"Toh! amaryar Nakowa mun iso,sae ki had'iye kukan naki ya isa hakanan kinga gidan surukai xamu shiga kada suga kina koke-koke su aza ko surukar tasu ba jaruma bace...... "
Ash ce ta katse min gajeriyar tunanina alokacin data bud'e min kofa da k'yau wai na fito,sae asannan na ankara da cewar har mun iso ban sani ba.
Sannu ahankali na sako kafafuwana waje tare da dire su akasa,wani daddad'ar ni'imtaccen iskar yammacin nan ne ya soma min barka da xuwa.fitowar tawa tayi daidai da wayar da wannan meh tukin keyi wanda ayanzu nasan sunansa don naji Zuwairah ta ambaci sunan wai *'KHALEED'*.
Cewa yayi"Kai dan iskan ango kana ina? gashi fah mun iso amma anki bamu amaryar..... "
Saurarawa naji yayi,can yace"Na taba maka irin wannan wasar ne? Ka yadda dani anki bamu ita wai sae kaje da kanka.... "
Ya sake saurarawa,can ya d'an d'ara yace"Kai wasa nake maka mallam karka min hauka,ga amaryarka nan mun kawo maka ita,tasha kuka kuma har yanxu tana kan yi ne sae kazo ka lallashi abarka........ "
"Ayyyirihiiiiiiii,lale marhaba da zuwan amarya.... " rangad'e rangad'en gudar dangin mijina ne ya hana min jin k'arshen maganar Khaleed da mijina.Ni kuwa jin sun nufoni ya saka na k'ara jan mayafina gaba don kada suga fuskata.
Wata 'yar matashiyar budurwace naga ta rungumeni tana fadin"Oyoyo!amaryarmu sannu da xuwa...... "
Mama Jamila ce ta rad'a min magana akunne,cewa tayi"Ki shiga da kafar damarki tare da bismillah,haka kuma xakiyi idan aka maidaki can gidanki.... "
Daga mata kai nayi alamar naji jawabin nata,daga haka naji wasu mata su wurin uku suma sun rungumeni kamar zasu kada ni akasa suna min sannu da xuwa har muka shige gidan.
Wani daki aka saukemu aciki wanda muka ji wani daddad'ar kamshin turaren wuta ya mana maraba da xuwa,gaskia ba laifi suma kanawa akwai son kamshi.Maganar gaskia ba k'aramin karramamu akai ba,nima sae naji na d'an saki jikina amma har xuwa wannan lokacin ban yaye mayafin kaina ba,ina nan lullub'e aciki kamar wata munafuka,lokaci xuwa lokaci nake dago kai na d'an saci kallon mutane.
Cikin k'ank'anin lokaci muka ga an cika mana gaba da kayan ciye-ciye da shaye-shaye.Mama Sadiya ne suka dan taba amma babu yadda basuyi dani ba amma naki ci.Ce musu nayi ak'oshe nake.Ak'arshe dai ruwa kawai na d'an sha.
Mama Jamila ce tace"Yarinya idan zaki mah saki jiki toh tun wuri ki saki don anan zamu barki,gobe idan Allah ya kaimu komawa gida abinmu xamuyi..."
Juyawa tayi ga Mama Sadiya tace"Sadiya hanzarta ki gama cin abincin ki min rakiya xuwa gidan wata k'awata dake nan jambulo,bazamu jima ba..... "
"Toh Addah... "acewar Mama Sadiya don Mama Jamila na gaba da ita.
Ni kuwa wani sabbin hawaye naji sun ziraro min saman k'unci,tayaya xan soma rayuwa agidan wasu bayan na sab'a da namu?taya mah xan soma had'a shimfid'a daya da wani k'aton gardi amatsayin mijina?
Yaye min mayafi naji anyi ana fad'in"Ai kya bari muga fuskartaki muga ko kin fini kyau koh? "
Ji nayi an fashe da dariya,ni kuwa gabana ne naji ya yanke ya fad'i,dakyar na iya d'ago kai ina duban wacce ta yaye min mayafina,ido hudu nayi da wata tsohuwa wacce kana ganinta kasan ta dad'e ana cin sallar idi da ita.Sae dai ba'a wani gane tsufanta don jikinta meh k'yau ne.
Tace"Masha Allah!.. Ashe dai megidan nawa balarabiya ya zab'o mana shiyasa yake ta rawar kafa da dokin auranta..... "
Aka sake fashewa da dariya akaro na biyu,ni kuwa d'an murmushin leb'en baki ne kawai ya sub'uce min,atake anan na gane cewar wannan tsohuwar kakarsu ce.
Tace"Amarya share hawayenki,don ni dake xamuyi zaman lafiya idan da hakan kika zo,idan kuwa da akasinta kika zo,toh nima nan uwargida ashirye nake...... "
wasu 'yan mata ne naji sunce"sae kakus! Kakaaa rigima.... " aka fashe da dariya.
Haka dai tayi ta mana barkwanci da wasannin wanda atake anan naji kawai tsohuwar ta shiga raina.Su Mama Jamila kuwa suna gama ciye-ciyensu suka sa kai suka fice xuwa unguwar da suka ce xasu,muka rage daga ni,Ash,Zuwairah sae kuma Anty Hajaar wacce ga dukkan alamu jininta ya hadu dana Kaka rigima,don sae hira suke ta xubawa.
Ba'a wani jima ba muka ji an soma k'iraye-kirayen sallar magrib,daya bayan daya muke shiga bandaki muna dauro alwala.
***
Itama Suhaima anata b'angaren an musu tarban mutunci,sosae aka karramasu.Reedah itace wacce ta soma rungumota,ta rad'a mata magana akunne"Oyoyo sahibata,barka da xuwa,yau Allah ya cika muku burinku ta mallakar junanku,Suhaima dear welcome home as matar yayanah...... "
Ita kuwa Suhaimar murmushi kawai tayi abinta tana meh jin wani irin farin ciki mara misaltuwa na ratsa xuciyarta.
Leedar da Engr. bazan iya kamanta muku irin tsananin farin cikin da suka tsinci kansu aciki ba na ganin ayau sun mallaki 'the women of their dreams'.Bama kamar Mahmood wanda jinsa yake kamar Zaynab d'insa ce ta dawo.
***
"Anty Fadima inji Yaya Mahmood wai na kawo miki wa'ennan kayan ki saka wai xuwa qarfe takwas za'a taho ah daukeku xuwa reception...... "
Hafeezah 'yar baba Mu'azzam ne ke yiwa Fadima wannan maganar wacce take kusan sa'ar su Suhaima.
Kokarin magana nake sae naji Ash ta rigani,cewa tayi"K'anwata zubasu saman gado yanzu xata shirya kinji? "
"Toh.. " kawai tace sannan ta zubasu saman gadon dakin ta fice.
Ina gama ganin ficewarta na dubi inda Ash ke xaune nace"Sannu sarkin felek'e da iyayi,ina fatar da kika amshi wannan kayan ke zaki sakasu kuma ki bisu donni yadda kika ganni nan babu inda zani.... "
Zuwairah ce tayi saurin taran numfashina"Haba babe ya kike neman kwafsa mana ne?"