← Book details Ni Da Aminiyata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 36

Sashe 34

Ni Da Aminiyata Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Yaukam tunda safe Gurum tai d'iba, shabiyu a Gurum tayi musu, su gwaggo sunyi farin cikin ganinsu, anmusu tarba mai k'yau, abinci har sopy ta rasa wanda zata ci.
Aysha ta gyara musu b'an garensu.
Da yamma baba yadawo daga gona shima yayi matuk'ar farin cikin ganinsu, yay musu godiyar hidimar dasuka sha da su Libabatu, yasa musu albarka sosai, itadai sopy saijin kunya takeyi.
To haka rayuwa tacigaba da tafiya mai tarin farinciki, dan Gurum tayi musu dad'i, gashi kullum sai aysha ta raka sopy gidajen 'yan uwa da abokan arzik'i, tun uncle G! yana nuna baya so har ya hak'ura.
Yau kwanansu hud'u da zuwa, sopy ta yashi da matsanancin zazzab'i, tun dare take zuba amai, har zuwa safiya, duk jikinta yasaki, saida safe uncle G! ya sanar da su gwaggo.
Cikin hanzari gwaggo tazo b'an garensu, ta iske sopy tanata shek'a amai, ta kalli uncle G! ta ce, "yusufa yakamata kakira mas'ud abokinka yazo ya dubata ko?.
Uncle G! ya ce, "to gwaggo, bari naje naga idan yana nan, gwaggo ta ce, "to ALLAH yasa adace.
Ya fice yana fad'in amin, babu dad'ewa suka dawo tareda mas'ud shima d'an Gurum ne, tare sukai piramary da secondary, ya duba sopy sosai, saiya saka mata k'arin ruwa yatafi dan ya bincika abinda ke damunta.
Karin ruwan da aka saka mata yasatayi barci, gwaggo da uncle G! zaune sun saka sopy Gaba sun zabga tagumi, baba kuma yana daga k'ofar d'aki zaune akan dankari, shimadai yayi shirun, aysha kuwa ta garzaya domin sanar da su aunty hafsat halin da'ake ciki.
Sai wajen karfe d'aya mas'ud yadawo, sannan su gwaggo sun fito, ya mik'ama uncle G! hannu yana murmushi.
Jiki a sanyaye uncle G! yabashi sukayi musabaha, mas'ud ya ce, "my Brother congratulation on your success!".
Cikin rashin fahimta uncle G! yake kallonsa, ya daure ya ce, "d'an uwa ni wane arzik'i nasamu da har zaka tayani murna.
Mas'ud yay murmushi ya ce, "kasamu babban arzik'i wanda wasu da yawa suke nema, harma dani aciki,kasamu k'yauta wadda ALLAH kad'aine yake badawa,kasamu arzik'i mai tarin ni'ima, na samun d'a daga matarka Safiyya!.
Cikin matuk'ar farin ciki ya rungume mas'ud, yana fad'in "Alhmdllhi ALA kulli halin", lallai nayi maraba da samun wannan d'ingimemiyar k'yauta, ina kuma godiya ga sarkin sarakuna, mai so dak'aunar bayinsa.
Uncle G! Yadawo da kallonsa ga sopy yana murmushi, lallai ALLAH yasoshi daba'a zubarmasa da d'a ba wajen dambe.
Sun dad'e suna murna kafin gwaggo ta shigo, itama mas'ud ya fad'a mata, dan uncle G! yakasa saboda kunya.
Dan danan gida ya kaure da murna, harsu aunty hafsat ma sunzo tun d'azu, kowa farin ciki yake zasuga d'an uncle G! Aduniya, gwaggo da baba jisuke kamar yau suka fara samun jika, bare kuma uban ginsami uncle G!, aii jiyake yafi kowa sa'a a wannan rana.
""wannan na sopy ne da uncle G!!!!👍🏻😘😘👌🏻"".......................✍🏻

💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 26~November~2016

🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷

NA BILKISA IBRAHIM💞

🔶🔸5⃣6⃣🔸🔶

.............Sopy bata farkaba sai la'asar bayan ruwan da'aka saka mata ya k'are, uncle G! ya taimaka mata tayi wanka dan taji k'arfin jikinta.
Su aunty hafsat suka shigo suna mata sannu, gwaggo takawo mata Abinci da Awara da fura wadda tasha nono mai k"yau.
Aunty hafsat ta ce, "k'anwata azuba miki abincin ko? kici.
Sopy tad'an yatsine fuska ta ce, "aunty nak'oshi, uncle G! ya harareta ya ce, "mikike nufi da kin k'oshi, haka kikeso ki zauna da yunwa?, tun jiyafa rabonki da cin abinci.
Gwaggo ta ce, "A'a yusufa abita ahankali, gwaggo ta matso kusada ita, ta ce, "d'iyata daure kici koda awararce, ko fura, fad'a min wanne kikeso, inkuma bak'ya sonsu a sake miki wasu.
Sopy ta ce, A'a Gwaggo zanci awarar, to shikenan gwaggo ta fad'a, Libabatu ta zuba mata awarar ta mik'a ma uncle G! dake kusada ita.
Ya d'auka yakai bakin sopy, sopy tayi k'asa da kai dan kunya, ahankali ta furta uncle kabarsa zan iya ci dakaina.
Ya ce, "karb'a kici kinga hannunki akwai datti gashi kuma jikinki babu k'arfi.
Gwaggo dake jinsu ta ce, "in bata son naka, bari ni nabata, da sauri sopy ta bud'e baki uncke G! ya saka mata awarar.
Abun yabasu dariya, dan haka suka tuntsure da dariya suduka d'akin, aunty hafsat ta ce, "k'anwata kunyarki tayi yawa.
Gwaggo ta ce, "aii haka akeson mace takasance mai kunya, Dan kunya adon mace .
Sopy tad'anci Awarar, dan tayi mata dad'i sosai, bayan tagama ta k'ara kwanciya, uncke G! ya ce, "tashi kid'an zauna ki huta, kar kwanciyar tayi yawa.
Gwaggo ta ce, "A'a kabarta ta kwanta, k'ila tafi jin dad'in kwan ciyar.
Ya ce, "to.

Sai dare su aunty hafsat suka tafi.
Baba ya sissiyoma sopy abubuwan kwad'ayi ya ce, "abata taci, bayan yai mata sannu suka tafi b'an garensu.
Uncle G! ya kalleta yana murmushi, ya ce, "lallai ke 'yar gata ce, kowa jiyake dake, tayi murmushi tana fad'in kokana kishine?.
Ya murmusa tareda d'ora hannunsa akan cikinta, ya ce, "bawani kishi, kema aii gamasu kwace miki fada nan sun kusa zuwa.
Cikin rashin fahimta sopy ta ke kallonsa, ta daure ta ce, "ban gane abinda kake nufiba??, ya kanne mata ido d'aya ya ce, "zaki gane, alokacin da yarona ko yarinya suka fara aikin 'yan kwallo acikinki.
Sopy ta zaro idanu waje ta ce, "kamar ya ya?, ya kwanto da kanta bisa cinyarsa, yad'ora hannunsa saman cikinta, d'ayan hannunsa yana shafa gashin kanta, ya ce, "Inada babbar ajiya awannan cikin, ma'ana saka makon ciyonki na bayyanar yarona ne.
Sopy tasaka hannu ta rufe fuska dan tagane miyake nufi, yay 'yar dariya, lallai yarinya kardai kice yarona d'an farin k'auye za'a maidashi?, to wlhy ban yardaba, garama tun yanzu na fad'a miki, dan banyarda a b'oyema yarinyata ko yarona suna ba, banyarda atureshi saboda yazo a matsayin d'an fariba, yasa hannu ya cire hannunta data rufe fuska dashi.
Saita rintse idanuwa, yakai bakinsa kan nata, yafara al'amura.
Na ce, "hummmm shidai uncle G! baya gajiya dayin kiss, bare kwana biyu ba'a had'uba.

Haka al'amura suka cigaba da tafiya a gurum, sopy tana shan tarairaya, duk abinda ta ce, "tana so sai an nemamata, koda awajen gurum yake kuwa, gwaggo ta hanata aikin komai, d'akinsuma Aysha ce take gyarawa kullum, a b'an garen uncle G! kuwa abin ba'a magana, suma su lubabatu suna bada gudummawa, dahaka sati biyun dasuka d'ebo tacika.
Amma baba da gwaggo sun hana tafiya, sunce tunda ba'a koma makarantar ba to bazasu tafiba sai sopy ta k'ara samun sauk'i, badan uncle G! yasoba dole ya hak'ura.
Shikam yana so su tafine dan yana cikin takura, gashi kuma wata sa'inma sopy a d'akin gwaggo take kwana idan jikin yay tsanani, itama kanta sopyn ya lura yanzu gudunshi takeyi.
Itako sopy bataso uncle G! yazo mata da buk'ata ne, shiyyasa take baya2 dashi, dan bata so yacika takura mata.
Kunsan wani cikin yana faruwa haka.

In tak'aice mu dai saida sukayi wata d'aya dawasu kwanaki, dan saida aka sanar an koma yajin aiki sannan baba yabarsu suka dawo kano.
Sun dawo cike da kewar muta nen gurum, yayinda suma suka barosu da kewarsu.
Tsaf suka tarar da gidansu an gyara, wananan duk aikin aunty Asiyane, sunji dad'i sosai, suna zuwa sai wanka da cin abincin da aunty asiyar ta aiko musu.
Bayan sun gana suka kwanta dan su huta.

A b'an garen fareeda kuwa al'amira sai ahan kali, dan ba komai take nema ta samuba, sauk'in tama tana agidan su sopyne, amma tayi bak'i ta rame kamar ba'itaba, kullum sai inna ta ce, "taje ta gaidasu mama.
Badan tasoba take zuwa, dan idan taje gidan sai mama ta had'e mata rai, daga ita har baba basa sakar mata fuska, lamuran suna damunta, amma tasan laifintane.
Yau ma tana zaune ad'akin sopy nada, ta had'a kai da guywa, hawaye suna kwaranya a idanunta, tana tuna rayuwa irin ta gidan sopy, duk da uncle G! bamai kud'i bane, amma yana k'ok'ari akan iyalinsa, yana wadatasu da cima mai dad'i, amma nan daga tuwo sai shinkafa, tarik'e kai tana hawaye.
Araina ne ce, "su fareeda anji jiki, an shiryu badan ALLAH ba😜.....................✍🏻

💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 27~November~2016

🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷

NA BILKISA IBRAHIM💞

🔶🔸5⃣7⃣🔸🔶

BAYAN WATA TAKWAS
...........Rayuwa mai gudu da sauri, daga safiya tayi sai gari ya waye, fareeda dai an shiryu da gsk, dan takoma makarantar islamiyya, gashi takoma wata shiru2, batada burin daya yuce tasamu miji tayi aure itama ta zauna agidanta, kullum kuma tana cikin yin istigifari, takan shiga gidansu ta taya mama aiki, dukda har yanzu mama bata sakar mata fuska, haka aikin inna duk ita takeyi, damuwar ta d'aya sopy, dan har yanzu sopy bata yafe mataba, ko gidan tazo bata kulata, gaisuwama sama2 sukeyi, kullum burinta ALLAH yakawo randa sopy zata yafe mata sukoma yanda suke da.
Inna tana k'ok'ari wajen yiwa sopy nasiha akan tayafema fareeda tunda ta shiyu, duk sanda tazo gidan saita yimata irin wannan nasihar.
To itama sopyn tayarda fareeda ta canja, amma tanaso tak'ara shiryuwane kafin ta ce, " ta yafe mata, dan tuni ta yafema fareedar batadai furta bane kawai.
Chapter 34 · 0% Book details