Sashe 9
Nahuce Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Yau gidan Ambasada Shehu Bichi komawa ya yi kamar gidan mutuwa don koke-koke, sakamakon cewa gobe ne Raheenah za ta bi Uncle din ta zuwa gida Nigeria. Wanda ya kara zuwa Jamus a karo na biyu don tafiya da ita. Ahlan kuka har da majina, Yafendo kuwa habar zani ta sa tana ta fyace hanci kamar an aiko musu da manzon mutuwa, Nene ce kadai mai lallashin kowa tana tuna musu suma kwanan nan za su koma Nigeria, sabida tenure din Ambasada Shehu ta kusan karewa.
Rabuwar Raheenah Omar da iyalin Ambasada wata irin rabuwa ce veryemotional. Wadda mai raguwar zuciya ba zai iya tsayawa a wajen ba. Abu daya ya kwantar musu da hankali, shi ne, su ma ahalin gidan na gab da dawowa Abuja bakidaya.
Suna sauka a Kaduna, Alhaji Usman ya sa direban sa ya wuce da ita Girei, kafin ta huta ta zo ta wuce NYSC, lokacin har an fara daukan batch A, don haka Uncle (yadda ta ke kiran sa) ya shigar da sunan Raheenah cikin masu tafiya hidimar kasa na wannan shekarar.
Ba ta fi sati biyu da dawowa Kaduna ba ta wuce NYSC a Ibadan inda suka yi posting dinta zuwa asibitin koyarwa na Ibadan.
Duk inda Raheenah ta shiga farin jinin ta da kyawun ta ke sayo mata soyayyar jama'a. Ga ta nan kamar ka taba jini ya yi tsartuwa (jazir sumul da ita) bafullatanar usli, wadda ta samu gogewa cikin zuzzurfan ilmin zamani. Ta wanke ta yi sumul ba za ka taba tunanin bafulatana ba ce, ta fi kama da larabawan Oman, Qatar haka, ko kuwa na Maghrib.
A Ibadan Teaching Hospital ne wani babban likita dan uwanta ya like mata wai shi Dr. Aryan dan jihar Minna ne, aiki ne ya kai shi Ibadan kuma karkashin team dinsa ta ke aiki. Rahinah ta yi duk iya kokarin ta don ta nunawa Aryan ba auren sa za ta iya ba, amma ya ki ganewa, mutum ne mai nacin gaske kuma girman mukamin aiki da ke tsakanin su ya sa ba ta isa ta wulakanta shi ba don ba ya shiga hurumin aikin ta sam-sam ya san lokacin da yake damunta da nacin kira da zarya a inda duk ya san zai ganta kasancewar sa ya manyanta don ya jima yana aiki a nan, matarsa ta mutu da jimawa ba shi da Da ko daya.
Don haka da Allah ya kawo lokacin kammala NYSC din ta, ji ta yi tamkar an raba ta da kaya, ta dawo gidan su a Kaduna a ranar matsayin cikakkiyar Otorhinolaryngologist mai lasisin aiki tare da Hukumar Lafiya ta kasa, ba da jimawa ba aka tura ta National Hospital Abuja matsayin ENT Surgeon. Dr. Rahinah Omar ta fara gudanar da ayyukanta na likitancin kunne, wuya da makogaro cikin dumbin nasara.
Ita ce likitar kunne ta farko a Africa da ta gudanar da dashen dodon-kunne (cochlear Implant) a Nigeria gabadaya. Kuma kafafen yada labarai suka yada nasararta a wannan surgery na kunne mai hadarin gaske, wanda ya zamo na farkon yi a kasar Najeriya. Kuma wanda ta sanyawa din ya ji magana sosai. Don haka manyan asibitoci masu zaman kansu na birnin tarayyah da wajen ta suka ankara da ita, ta yi attracting asibitocin kunne masu yawa suna masu gayyatar ta aikin part-time job tare da su. Amma duk ciki sai ta zabi babban asibitin NIZAMIYE ta hada da aikinta na gwamnati a National Hospital Abuja.
An bai wa Raheenah gidan likitoci a cikin National Hospital. Uncle ya ce bai son ta je ta zauna ita kadai ba muharrami don haka Aunty Badiya ta samo mata mai aiki a nan kaduna suka tare tare, wai ita Sahura. bazawara ce da ba ta fi shekaru arba'in ba.
Daga lokacin da Raheenah ta gane dangin ta zuwa yanzu ta zo Kaduna ya kai sau shida, amma cikin wani hukunci na Ubangiji ba ta taba haduwa da Abdallah ba, duk lokacin da ta zo yana Zamfara ko wajen mahaifin sa a Lagos inda harkokin sa suka fi karfi yanzu. Sai dai cikin hirarrakin su da Aunty Badiya da su Musaddiq ta fuskanci akwai dan kaninta da ta ke riko tare da Zarah, Baban sa bai cika barin sa ya zauna a Kaduna ba cikin hutu wanda ita lokacin take zuwa sai lokacin makaranta. Haka a bakin su Musaddiq tana yawan jin sunan Junior sunan da duk jamaar gidan suke kiran Abdallah, kasancewar shi ne karami a cikin su.
Tun komawar su Abuja ita da Baba Sahura Raheenah ta zama ba ta da lokacin kan ta, sabida documentation na kama aiki. Tana jin dadin zama da Sahura don kullum kafin ta dawo ta gyare musu dan madaidaicin gidan su tsaf! Ta kunna turaren wuta, ta kuma dafa musu abinci. In Raheenah ba ta ra'ayi daga waje ta ke taho da abin da za ta ci. Uncle ya mallaka mata karamar mota KiaPicanto don ta samu saukin zirga-zirgar ayyukan ta.
Wannan ya taimaka ainun wajen kwashewa Raheenah hankali a wannan dan tsakanin. Ba ta da lokacin da za ta zauna ta yi tunani. Ko bibiyar lamuran dan mutanen Nahuce. Aiki ta ke tukuru da kwarewa da patriotism domin saka wa gwamnatin Najeriya da ta tsaya mata, ta tallafi ilmin ta da (scholarship).
Ranar da ta fara daukan albashin ta na farko ko naira ba ta ci a ciki ba ta kasafta wa iyayen ta, bayan ta ware wa Ambasada kaso mafi tsoka, sannan Yafendo da Nene. Tana mai dakacen ina ma Daada tana raye?
Wannan ihsani da girma da Raheenah ta bai wa iyayen dakinta ya kara mata martaba a idanun su, ba don ba su da shi ba, sai don ganewa da suka yi ita din mutum ce mara manta alkhairi. Bayyanar iyayen ta bai sa su ta daina kallon su da matsayin iyaye ba.
Asibitin Nizamiye wani babban asibiti ne mai zaman kansa a birnin tarayyah. Suna matukar ji da Dr. Rahinah Omar wadda ke aiki part-time da su a matsayin ENT Surgeon (otorlaryngologist).
Nizamiye Hospital na nan a (Life-Camp). They have the latest technology for the treatment of most common ENT cases irin su Rhinitis, Sinusitis, Myringoplesty, Tympanoplasty, Mastoidectomy, Septoplasty da sauransu. The World Class Private Hospital wanda Turkawa suka kafa a birnin Tarayyah.
Don haka Raheenah ba karamar sa'a ta taka ba a rayuwarta da ta samu kujera a Nizamiye. Kudi sosai ya soma shiga account din yar mutanen Girei.
*****
Wata ranar Litinin, Dr. Raheenah ta dawo aiki a gajiye likis, tana yin parking a apartment din ta Baba Sahura na fitowa za ta zub da shara. Da sauri ta aje kwandon sharar ta iso ta karbi jakar uwargijiyar ta tare da (lab coat) da ke hannun ta tare da yi mata barka da zuwa, Rahinah ta bata mukullin booth din motar ta ce ta fidda cefanen da ta yo musu ta sanya a freezer.
Wayar Raheenah ta yi kara a lokacin da ta ke fidda leshin jikin ta za ta shiga wanka. Dakatawa ta yi ta dauki wayar inda ta ga Aunty Badiya ke kiran ta.
"Maman Musaddiq ya ku ke?"
Ta ce, "Muna lafiya cikin alkhairi Raheenah, Uncle ne ya ce in tambaye ki yaushe za ki samu shigowa Kd? Akwai muhimmiyar magana da ya ke so ku yi".
Raheenah ta ce, "Aunty a wannan watan duka ba zan samu lokacin shigowa ba, due to my tight schedules, amma insha Allahu weekend din karshen wata zan shigo".
Aunty Badiya ta ce, "Ni kuma zan je gida Zamfara lokacin, zan dauko dan kani na Junior daga wajen Hajiyar mu, Baban sa zai dawo daga Belarus ina so kamin ya wuce Lagos ya gan shi, amma kwana daya zan yi. So, insha Allah za mu hadu kafin ki koma, a kula da aiki, a kula da mutunci. Allah ya kara wa rayuwar ku da nema albarka".
Sati biyu bayan nan Ambasada Shehu da iyalinsa da mahaifiyarsa Yafendo suka sauka a kasar Nigeria. Sun jima a Bichi cikin 'yan uwa da danginsu kafin su yi relocating a gidan da Ambasada ya saya a Abuja tun kafin barowar shi Jamus. Gidan yana nan a unguwar Maitama.
Rabuwar Raheenah Omar da iyalin Ambasada wata irin rabuwa ce veryemotional. Wadda mai raguwar zuciya ba zai iya tsayawa a wajen ba. Abu daya ya kwantar musu da hankali, shi ne, su ma ahalin gidan na gab da dawowa Abuja bakidaya.
Suna sauka a Kaduna, Alhaji Usman ya sa direban sa ya wuce da ita Girei, kafin ta huta ta zo ta wuce NYSC, lokacin har an fara daukan batch A, don haka Uncle (yadda ta ke kiran sa) ya shigar da sunan Raheenah cikin masu tafiya hidimar kasa na wannan shekarar.
Ba ta fi sati biyu da dawowa Kaduna ba ta wuce NYSC a Ibadan inda suka yi posting dinta zuwa asibitin koyarwa na Ibadan.
Duk inda Raheenah ta shiga farin jinin ta da kyawun ta ke sayo mata soyayyar jama'a. Ga ta nan kamar ka taba jini ya yi tsartuwa (jazir sumul da ita) bafullatanar usli, wadda ta samu gogewa cikin zuzzurfan ilmin zamani. Ta wanke ta yi sumul ba za ka taba tunanin bafulatana ba ce, ta fi kama da larabawan Oman, Qatar haka, ko kuwa na Maghrib.
A Ibadan Teaching Hospital ne wani babban likita dan uwanta ya like mata wai shi Dr. Aryan dan jihar Minna ne, aiki ne ya kai shi Ibadan kuma karkashin team dinsa ta ke aiki. Rahinah ta yi duk iya kokarin ta don ta nunawa Aryan ba auren sa za ta iya ba, amma ya ki ganewa, mutum ne mai nacin gaske kuma girman mukamin aiki da ke tsakanin su ya sa ba ta isa ta wulakanta shi ba don ba ya shiga hurumin aikin ta sam-sam ya san lokacin da yake damunta da nacin kira da zarya a inda duk ya san zai ganta kasancewar sa ya manyanta don ya jima yana aiki a nan, matarsa ta mutu da jimawa ba shi da Da ko daya.
Don haka da Allah ya kawo lokacin kammala NYSC din ta, ji ta yi tamkar an raba ta da kaya, ta dawo gidan su a Kaduna a ranar matsayin cikakkiyar Otorhinolaryngologist mai lasisin aiki tare da Hukumar Lafiya ta kasa, ba da jimawa ba aka tura ta National Hospital Abuja matsayin ENT Surgeon. Dr. Rahinah Omar ta fara gudanar da ayyukanta na likitancin kunne, wuya da makogaro cikin dumbin nasara.
Ita ce likitar kunne ta farko a Africa da ta gudanar da dashen dodon-kunne (cochlear Implant) a Nigeria gabadaya. Kuma kafafen yada labarai suka yada nasararta a wannan surgery na kunne mai hadarin gaske, wanda ya zamo na farkon yi a kasar Najeriya. Kuma wanda ta sanyawa din ya ji magana sosai. Don haka manyan asibitoci masu zaman kansu na birnin tarayyah da wajen ta suka ankara da ita, ta yi attracting asibitocin kunne masu yawa suna masu gayyatar ta aikin part-time job tare da su. Amma duk ciki sai ta zabi babban asibitin NIZAMIYE ta hada da aikinta na gwamnati a National Hospital Abuja.
An bai wa Raheenah gidan likitoci a cikin National Hospital. Uncle ya ce bai son ta je ta zauna ita kadai ba muharrami don haka Aunty Badiya ta samo mata mai aiki a nan kaduna suka tare tare, wai ita Sahura. bazawara ce da ba ta fi shekaru arba'in ba.
Daga lokacin da Raheenah ta gane dangin ta zuwa yanzu ta zo Kaduna ya kai sau shida, amma cikin wani hukunci na Ubangiji ba ta taba haduwa da Abdallah ba, duk lokacin da ta zo yana Zamfara ko wajen mahaifin sa a Lagos inda harkokin sa suka fi karfi yanzu. Sai dai cikin hirarrakin su da Aunty Badiya da su Musaddiq ta fuskanci akwai dan kaninta da ta ke riko tare da Zarah, Baban sa bai cika barin sa ya zauna a Kaduna ba cikin hutu wanda ita lokacin take zuwa sai lokacin makaranta. Haka a bakin su Musaddiq tana yawan jin sunan Junior sunan da duk jamaar gidan suke kiran Abdallah, kasancewar shi ne karami a cikin su.
Tun komawar su Abuja ita da Baba Sahura Raheenah ta zama ba ta da lokacin kan ta, sabida documentation na kama aiki. Tana jin dadin zama da Sahura don kullum kafin ta dawo ta gyare musu dan madaidaicin gidan su tsaf! Ta kunna turaren wuta, ta kuma dafa musu abinci. In Raheenah ba ta ra'ayi daga waje ta ke taho da abin da za ta ci. Uncle ya mallaka mata karamar mota KiaPicanto don ta samu saukin zirga-zirgar ayyukan ta.
Wannan ya taimaka ainun wajen kwashewa Raheenah hankali a wannan dan tsakanin. Ba ta da lokacin da za ta zauna ta yi tunani. Ko bibiyar lamuran dan mutanen Nahuce. Aiki ta ke tukuru da kwarewa da patriotism domin saka wa gwamnatin Najeriya da ta tsaya mata, ta tallafi ilmin ta da (scholarship).
Ranar da ta fara daukan albashin ta na farko ko naira ba ta ci a ciki ba ta kasafta wa iyayen ta, bayan ta ware wa Ambasada kaso mafi tsoka, sannan Yafendo da Nene. Tana mai dakacen ina ma Daada tana raye?
Wannan ihsani da girma da Raheenah ta bai wa iyayen dakinta ya kara mata martaba a idanun su, ba don ba su da shi ba, sai don ganewa da suka yi ita din mutum ce mara manta alkhairi. Bayyanar iyayen ta bai sa su ta daina kallon su da matsayin iyaye ba.
Asibitin Nizamiye wani babban asibiti ne mai zaman kansa a birnin tarayyah. Suna matukar ji da Dr. Rahinah Omar wadda ke aiki part-time da su a matsayin ENT Surgeon (otorlaryngologist).
Nizamiye Hospital na nan a (Life-Camp). They have the latest technology for the treatment of most common ENT cases irin su Rhinitis, Sinusitis, Myringoplesty, Tympanoplasty, Mastoidectomy, Septoplasty da sauransu. The World Class Private Hospital wanda Turkawa suka kafa a birnin Tarayyah.
Don haka Raheenah ba karamar sa'a ta taka ba a rayuwarta da ta samu kujera a Nizamiye. Kudi sosai ya soma shiga account din yar mutanen Girei.
*****
Wata ranar Litinin, Dr. Raheenah ta dawo aiki a gajiye likis, tana yin parking a apartment din ta Baba Sahura na fitowa za ta zub da shara. Da sauri ta aje kwandon sharar ta iso ta karbi jakar uwargijiyar ta tare da (lab coat) da ke hannun ta tare da yi mata barka da zuwa, Rahinah ta bata mukullin booth din motar ta ce ta fidda cefanen da ta yo musu ta sanya a freezer.
Wayar Raheenah ta yi kara a lokacin da ta ke fidda leshin jikin ta za ta shiga wanka. Dakatawa ta yi ta dauki wayar inda ta ga Aunty Badiya ke kiran ta.
"Maman Musaddiq ya ku ke?"
Ta ce, "Muna lafiya cikin alkhairi Raheenah, Uncle ne ya ce in tambaye ki yaushe za ki samu shigowa Kd? Akwai muhimmiyar magana da ya ke so ku yi".
Raheenah ta ce, "Aunty a wannan watan duka ba zan samu lokacin shigowa ba, due to my tight schedules, amma insha Allahu weekend din karshen wata zan shigo".
Aunty Badiya ta ce, "Ni kuma zan je gida Zamfara lokacin, zan dauko dan kani na Junior daga wajen Hajiyar mu, Baban sa zai dawo daga Belarus ina so kamin ya wuce Lagos ya gan shi, amma kwana daya zan yi. So, insha Allah za mu hadu kafin ki koma, a kula da aiki, a kula da mutunci. Allah ya kara wa rayuwar ku da nema albarka".
Sati biyu bayan nan Ambasada Shehu da iyalinsa da mahaifiyarsa Yafendo suka sauka a kasar Nigeria. Sun jima a Bichi cikin 'yan uwa da danginsu kafin su yi relocating a gidan da Ambasada ya saya a Abuja tun kafin barowar shi Jamus. Gidan yana nan a unguwar Maitama.