Sashe 7
Nahuce Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Alhaji Usman Girei na tsaye a kofar tankareren gidan sa yana jiran isowarsu. A gefensa babban dansa ne Musaddiq dan kimanin shekaru goma sha biyar. Suna fitowa daga mota Alhaji Usman na karasowa, burin sa kawai ya dora idanun sa a kan diyar dan uwansa.
Raheenah na fitowa daga mota ta gane shi ne Alhaji Usman kani ga mahaifin da ba ta taba sani ba. Ya buda mata hannuwa ta tafi da sauri ta shige, Nene sai da ta ji hawayen tausayi da farin ciki ya cika idanunta.
Daidai lokacin da motar su Ambasada ta iso, suka jira har direban sa yayi parking ya bude masa mota ya fito, sannan Alhaji Usman yayi musu jagora zuwa babban falon sa, tarba ta girma da karamci sun ganta gun iyalin Alh. Usman, bayan an gaggaisa Sarkin Fulani ya sake maimaita labarin da ya basu a Girei, Ambasada kuma ya dora nasa na yadda aka yi Raheenah ta zo hannunsa a kasar Jamus.
A lokacin maidakin Alhaji Usman ta fita, tana kitchen tana hada-hadar hada abincin alfarmar da ta tanadarwa bakin nasu. Don haka bata ji labarin da Ambasada ya bayar ba. Amma ta san yar Yayan sa ce mai rasuwa data tafi karatu ketare aka kawo masa. Wadda ta dade tana jin labarin batan su a bakin sa tare da mahaiyar sa.
Hatta auren Raheenah da Habibu sai da Daddy ya labarta masa komai da yadda auren ya kare. Abinda ya hana Rahinah yarda da sulhun da komen ne shi har gobe bai sani ba.
Alhaji Usman ya ce ya zama dole su yi tracing Habibu, wannan ai zalunci ne, dauke yaron da ke shan nono daga uwar da ta haife shi ko kotu za a je sai ya kwatowa Raheenah dan ta. In ya koma wajen ubansa to ya balaga ne, yana bayan hukuncin da Rahinah ta yi wa aurenta da Habibu ta karbi 'yancinta, inda gaske yana son ta ya kasa hakurin ya nemi iyayenta ya nemi aurenta cikin mutunci a hannun su mana? Sai wata watsatsiyar mata Laura? Shi kwata-kwata bai ga laifin Raheenah ba. Maza-maza a ba shi lambar Habibu yanzu zai je ya karbo wa Raheenah dan ta.
Amma me?
Lambar Habibu da Daddy ke da ita ta kasar Jamus ce, sai a lokacin ya tuna tunda Habibu ya zo Nigeria bai kira shi a waya da lambar sa ta Najeriya kamar yadda suka yi alkawari ba. Haka ya yi ta gwada ta Jamus din duk da ya san ba shiga za ta yi ba. A karshe ya gaya wa Alhaji Usman tunda ya taho bai kira shi ba, amma yana da yakinin zai kira shi komai daren dadewa, domin yaro ne mai hankali da biyayya, sannan da zuciya daya yake son Rahinah. Ya kwantar da hankalinsa ya sa a ransa cewa, Dan Raheenah yana a kyakkyawan hannu. Domin yaron Uba ne har da rabi.
Daidai lokacin da Hajiya Badiya ta shigo masu aiki biyu a bayan ta dauke da kabakin abinci, suka shirya komai tare da ita a kan tebirin cin abinci, ta zo tana tsokanar Raheenah wai anya ko tana jin 'ZO' da harshen Hausa? Ta gan ta sullubebiya kamar sai ka wanke hannu kafin ka taba. Yafendo ce ta tare mata da cewa "ko jakar Kano nan ta ganta ta barta wajen jin hausa". Hajiya Badiya ta gabatar mata da kannenta, Musaddiq da Mubaraq da Mu'allim da Zarah. Raheenah ta rungume Zarah sosai kaunar yaran na shigar ta, tana ta yi musu tambayoyi a kan karatun su, sun tattauna muhimman abubuwa a kan Raheena tsakanin Daddy da Alhaji Usman kafin su yi sallama tare da amsar lambobin juna.
Shi da su Nene washegari da asubah suka juya zuwa Bichi a motar da Daddy ya zo, direban su Nene kuma ya juya da mutanen Girei zai maida su. An bar Raheenah sai za su wuce Jamus jibi ita da Safeenah direba zai tsaya ya dauke ta a nan Kaduna su karasa Abuja su hau jirgin Jamus.
******
Zaman Raheenah na kwana biyu a gidan Kawun ta tare da matar kanin mahaifinta Aunty Badiya da 'ya'yanta hudu gwanin ban sha'awa, ba ta bambanta Raheenah da Musaddiq ko magana za ta yi sai ta ce, sai Raheenah ta fara kaza sannan Musaddiq zai yi tunda ta girme shi. Jininta ya fi haduwa da na Musaddiq sabida ilminsa, ga Raheenah da son yara masu kwazo. Zarah ma suna shiri don sai ta ke kwatanta girmanta da na Abdallahnta a halin yanzu, ita in ba idonta ne ma ke mata gizo ba sai ta ce, Mu'allim yana mata yanayi da danta Abdallah. Sai dai yadda ta binne uban Abdallah a ranta a yanzu, haka ta ke so shi ma Abdallahn ta daina ko tuno shi duk da ta san hakan ba mai yiwuwa ba ne.
Lokaci-lokaci sai ta tsaya ta bar abin da ta ke yi tana tunanin Abdallah, ko me yake yi yanzu? Ko ya manta ta? Ko ya daina kiran sunanta? Wannan da wancan.... Amma ko ya ya tunanin Habibu ya kutso cikin kan ta da zuciyar ta sai tayi kokarin yakice shi da dukkan karfin ta.
Ba shakkah ta ji dadin zama da Aunty Badiya da yaranta da Kawun ta, tsayin kwana biyun, ji ta ke kamar kada ta koma Jamus, but she want to be that Otorhinolaryngologist she promised to be. Wannan ne kadai ya sa ta yarda ta koma Jamus tare da Safeenah a washegarin ranar da suka biyo don tafiya da ita, inda suka tashi ta filin jirgin saman Abuja.
Kudi mai yawa Alhaji Usman ya ba ta, ya ce ta rage wa Ambasada nauyi, kuma ya yi alkawarin aika mata kwatankwacin su duk karshen wata.
(Ranar da Rahinah ta tashi Abuja da safe, da yammacin ranar aka dawo da Abdallah daga Zamfara inda ya je ya yiwa Hajiyar Nahuce hutu).
*****
KOMAWAR RAHEENAH JAMUS
B
ayan sun koma Frankfurt ita da Safeenah, kowacce tana dakinta babu mai shiga shirgin kowa. Ko da ma can jininsu ba wai ya hadu ba ne, don haka kowa sabgar karatunta ta ke yi ita kadai a dakin ta. Ta kan dai ji wani lokacin Safeenah na waya da saurayin ta Muktar a barandar dakunan nasu. Raheenah Omar ta fuskanci karatunta da wani irin zeal saboda a halin yanzu ba ta da damuwa, tana cikin farin ciki na haduwa da danginta. Sai ta dauki hankalin ta da nutsuwarta kacokam ta mika wa MBBS dinta.
Har zuwa lokacin da su Daddy suka dawo, suka ci gaba da gudanar da rayuwar su cikin gidan yadda suka saba.
Amma me? Ita diya mace a yayin da ta samu contentment na rayuwa, nutsuwa da kwanciyar hankali, abin da ya saura mata shi ne, DA NAMIJI a gefenta. A matsayin mijin aure ko manemin aure.
Wannan ne kadai gibin Raheenah a rayuwa. Somehow, wani bangare na zuciyarta kewar Habeebu yake yi, tana karyatawa da gangan. Tana bai wa tunanin rashin muhimmanci, tana ganin she can overcome it by force, amma a hankali sai tunanin Habib Nahuce da wata sabuwar kakkarfar soyayyarsa suka zo suka soma cin karfintaba tare da ta ankara ba.
Wannan wani sirri ne tsakanin ta da zuciyar ta, wanda daga ita sai Ubangijin ta suka san da shi. Bata kuma fatan wani cikin gidan ya san da shi.
Raheenah Omar ta gama MBBS a wannan shekarar, da sakamako mai madaukakiyar daraja, ta kammala ne (as the overall best student). A wannan lokacin Alhaji Usman Girei sai da ya taka kafafunsa har Jamus da taimakon cuku-cukun visa da Ambasada ya yi masa ya taya Raheenah murnar karbar kwalinta.
A wannan ranar Raheenah sai da ta yi kuka don farin ciki amma duk da haka; ta rasa dalilin da ya sa farin cikin nata ya zama incomplete, tamkar tana missing someone important, musamman da ya kasance kusan duk abokan karatunta mazajen su ne suka taya su karbar nasu kwalin, wasu kuma fiances dinsu. Ita ce kadai mai Uncle da Daddy a gefe, babu mijin da ya taya ta karbowa ya karba a nashi hannun bayan ta karbo ya bi ta da murmushin kauna.
A hakan ma ta fi kowa godiyar Ubangiji domin ba ta taba tunanin haduwa da wani nata ba har zuwa sanda za ta bar Jamus kwata-kwata. Amma yau ga ta tare da kanin uban ta har Jamus din.
Kafin ta fara specialization dinta sai da ta zo Girei ta yi sati biyu da su Goggo Dudu, sannan ta wuce Kaduna can ma ta yi sati biyu. Ba tare da ta sani ba, a ranar da ta je Kaduna, a jiyan ranar Habibu Nahuce ya zo ya dauki Abdallah daga wajen Aunty Badiya zuwa Zamfara don ya yi hutun kirsimetin sa tare da Hajiyar Nahuce.
Satin ta biyu ta koma Jamus ta fara specialization din ta a otorhinolaryngology.
Daga lokacin da ta fara specialization din kasancewar wahalar sa bata kai ta MBBS ba ta kan samu lokacin kan ta da lokacin tunani, a lokacin abubuwa suka fara rikice mata. Soyayyar (her ex Habibu) ta kada ita wanwar. Ta soma tunani da neman hanyar samun labarin sa. Ba don ta kula shi ba, sai don kawai shes curious ga son ta san me yake ciki shi da gudan ran ta, don haka ta soma sha'awar bibiyar Habibu Nahuce a kafafen sadar da zumunta, amma ko daya ba ya kai. As the busy person that he is, bashi da lokacin wadannan abubuwan (social media platforms). A karshe ta yanke shawarar duba shi a yanar gizo (google) ta san bazata kasa samun wani abu da shafe shi ba komai kankantar sa.
A wani marece ne ana tafka ruwan sama mai karfi a garin Frankfurt, ta rufe tagogi da kofar dakin ta, ta saki fararen curtains din dakin, sannan ta kunna (room-heater), ta dauko kwamfutar bisa cinya (loptop) ta shiga google kawai ta rubuta sunan sa HABIBU MUSTAPHA NAHUCE. Ita kuma googlesai ta kai ta LinkedIn. Kasancewar sa (professional platform). A can bata samu wani cikakken bayanin sa ba sai na profession din sa (as a Hotel Administrator), sai kuma a wani website na hotels din sa. A canne ta ga cikakken sunansa da cikakken bayaninsa a halin yanzu.
Raheenah na fitowa daga mota ta gane shi ne Alhaji Usman kani ga mahaifin da ba ta taba sani ba. Ya buda mata hannuwa ta tafi da sauri ta shige, Nene sai da ta ji hawayen tausayi da farin ciki ya cika idanunta.
Daidai lokacin da motar su Ambasada ta iso, suka jira har direban sa yayi parking ya bude masa mota ya fito, sannan Alhaji Usman yayi musu jagora zuwa babban falon sa, tarba ta girma da karamci sun ganta gun iyalin Alh. Usman, bayan an gaggaisa Sarkin Fulani ya sake maimaita labarin da ya basu a Girei, Ambasada kuma ya dora nasa na yadda aka yi Raheenah ta zo hannunsa a kasar Jamus.
A lokacin maidakin Alhaji Usman ta fita, tana kitchen tana hada-hadar hada abincin alfarmar da ta tanadarwa bakin nasu. Don haka bata ji labarin da Ambasada ya bayar ba. Amma ta san yar Yayan sa ce mai rasuwa data tafi karatu ketare aka kawo masa. Wadda ta dade tana jin labarin batan su a bakin sa tare da mahaiyar sa.
Hatta auren Raheenah da Habibu sai da Daddy ya labarta masa komai da yadda auren ya kare. Abinda ya hana Rahinah yarda da sulhun da komen ne shi har gobe bai sani ba.
Alhaji Usman ya ce ya zama dole su yi tracing Habibu, wannan ai zalunci ne, dauke yaron da ke shan nono daga uwar da ta haife shi ko kotu za a je sai ya kwatowa Raheenah dan ta. In ya koma wajen ubansa to ya balaga ne, yana bayan hukuncin da Rahinah ta yi wa aurenta da Habibu ta karbi 'yancinta, inda gaske yana son ta ya kasa hakurin ya nemi iyayenta ya nemi aurenta cikin mutunci a hannun su mana? Sai wata watsatsiyar mata Laura? Shi kwata-kwata bai ga laifin Raheenah ba. Maza-maza a ba shi lambar Habibu yanzu zai je ya karbo wa Raheenah dan ta.
Amma me?
Lambar Habibu da Daddy ke da ita ta kasar Jamus ce, sai a lokacin ya tuna tunda Habibu ya zo Nigeria bai kira shi a waya da lambar sa ta Najeriya kamar yadda suka yi alkawari ba. Haka ya yi ta gwada ta Jamus din duk da ya san ba shiga za ta yi ba. A karshe ya gaya wa Alhaji Usman tunda ya taho bai kira shi ba, amma yana da yakinin zai kira shi komai daren dadewa, domin yaro ne mai hankali da biyayya, sannan da zuciya daya yake son Rahinah. Ya kwantar da hankalinsa ya sa a ransa cewa, Dan Raheenah yana a kyakkyawan hannu. Domin yaron Uba ne har da rabi.
Daidai lokacin da Hajiya Badiya ta shigo masu aiki biyu a bayan ta dauke da kabakin abinci, suka shirya komai tare da ita a kan tebirin cin abinci, ta zo tana tsokanar Raheenah wai anya ko tana jin 'ZO' da harshen Hausa? Ta gan ta sullubebiya kamar sai ka wanke hannu kafin ka taba. Yafendo ce ta tare mata da cewa "ko jakar Kano nan ta ganta ta barta wajen jin hausa". Hajiya Badiya ta gabatar mata da kannenta, Musaddiq da Mubaraq da Mu'allim da Zarah. Raheenah ta rungume Zarah sosai kaunar yaran na shigar ta, tana ta yi musu tambayoyi a kan karatun su, sun tattauna muhimman abubuwa a kan Raheena tsakanin Daddy da Alhaji Usman kafin su yi sallama tare da amsar lambobin juna.
Shi da su Nene washegari da asubah suka juya zuwa Bichi a motar da Daddy ya zo, direban su Nene kuma ya juya da mutanen Girei zai maida su. An bar Raheenah sai za su wuce Jamus jibi ita da Safeenah direba zai tsaya ya dauke ta a nan Kaduna su karasa Abuja su hau jirgin Jamus.
******
Zaman Raheenah na kwana biyu a gidan Kawun ta tare da matar kanin mahaifinta Aunty Badiya da 'ya'yanta hudu gwanin ban sha'awa, ba ta bambanta Raheenah da Musaddiq ko magana za ta yi sai ta ce, sai Raheenah ta fara kaza sannan Musaddiq zai yi tunda ta girme shi. Jininta ya fi haduwa da na Musaddiq sabida ilminsa, ga Raheenah da son yara masu kwazo. Zarah ma suna shiri don sai ta ke kwatanta girmanta da na Abdallahnta a halin yanzu, ita in ba idonta ne ma ke mata gizo ba sai ta ce, Mu'allim yana mata yanayi da danta Abdallah. Sai dai yadda ta binne uban Abdallah a ranta a yanzu, haka ta ke so shi ma Abdallahn ta daina ko tuno shi duk da ta san hakan ba mai yiwuwa ba ne.
Lokaci-lokaci sai ta tsaya ta bar abin da ta ke yi tana tunanin Abdallah, ko me yake yi yanzu? Ko ya manta ta? Ko ya daina kiran sunanta? Wannan da wancan.... Amma ko ya ya tunanin Habibu ya kutso cikin kan ta da zuciyar ta sai tayi kokarin yakice shi da dukkan karfin ta.
Ba shakkah ta ji dadin zama da Aunty Badiya da yaranta da Kawun ta, tsayin kwana biyun, ji ta ke kamar kada ta koma Jamus, but she want to be that Otorhinolaryngologist she promised to be. Wannan ne kadai ya sa ta yarda ta koma Jamus tare da Safeenah a washegarin ranar da suka biyo don tafiya da ita, inda suka tashi ta filin jirgin saman Abuja.
Kudi mai yawa Alhaji Usman ya ba ta, ya ce ta rage wa Ambasada nauyi, kuma ya yi alkawarin aika mata kwatankwacin su duk karshen wata.
(Ranar da Rahinah ta tashi Abuja da safe, da yammacin ranar aka dawo da Abdallah daga Zamfara inda ya je ya yiwa Hajiyar Nahuce hutu).
*****
KOMAWAR RAHEENAH JAMUS
B
ayan sun koma Frankfurt ita da Safeenah, kowacce tana dakinta babu mai shiga shirgin kowa. Ko da ma can jininsu ba wai ya hadu ba ne, don haka kowa sabgar karatunta ta ke yi ita kadai a dakin ta. Ta kan dai ji wani lokacin Safeenah na waya da saurayin ta Muktar a barandar dakunan nasu. Raheenah Omar ta fuskanci karatunta da wani irin zeal saboda a halin yanzu ba ta da damuwa, tana cikin farin ciki na haduwa da danginta. Sai ta dauki hankalin ta da nutsuwarta kacokam ta mika wa MBBS dinta.
Har zuwa lokacin da su Daddy suka dawo, suka ci gaba da gudanar da rayuwar su cikin gidan yadda suka saba.
Amma me? Ita diya mace a yayin da ta samu contentment na rayuwa, nutsuwa da kwanciyar hankali, abin da ya saura mata shi ne, DA NAMIJI a gefenta. A matsayin mijin aure ko manemin aure.
Wannan ne kadai gibin Raheenah a rayuwa. Somehow, wani bangare na zuciyarta kewar Habeebu yake yi, tana karyatawa da gangan. Tana bai wa tunanin rashin muhimmanci, tana ganin she can overcome it by force, amma a hankali sai tunanin Habib Nahuce da wata sabuwar kakkarfar soyayyarsa suka zo suka soma cin karfintaba tare da ta ankara ba.
Wannan wani sirri ne tsakanin ta da zuciyar ta, wanda daga ita sai Ubangijin ta suka san da shi. Bata kuma fatan wani cikin gidan ya san da shi.
Raheenah Omar ta gama MBBS a wannan shekarar, da sakamako mai madaukakiyar daraja, ta kammala ne (as the overall best student). A wannan lokacin Alhaji Usman Girei sai da ya taka kafafunsa har Jamus da taimakon cuku-cukun visa da Ambasada ya yi masa ya taya Raheenah murnar karbar kwalinta.
A wannan ranar Raheenah sai da ta yi kuka don farin ciki amma duk da haka; ta rasa dalilin da ya sa farin cikin nata ya zama incomplete, tamkar tana missing someone important, musamman da ya kasance kusan duk abokan karatunta mazajen su ne suka taya su karbar nasu kwalin, wasu kuma fiances dinsu. Ita ce kadai mai Uncle da Daddy a gefe, babu mijin da ya taya ta karbowa ya karba a nashi hannun bayan ta karbo ya bi ta da murmushin kauna.
A hakan ma ta fi kowa godiyar Ubangiji domin ba ta taba tunanin haduwa da wani nata ba har zuwa sanda za ta bar Jamus kwata-kwata. Amma yau ga ta tare da kanin uban ta har Jamus din.
Kafin ta fara specialization dinta sai da ta zo Girei ta yi sati biyu da su Goggo Dudu, sannan ta wuce Kaduna can ma ta yi sati biyu. Ba tare da ta sani ba, a ranar da ta je Kaduna, a jiyan ranar Habibu Nahuce ya zo ya dauki Abdallah daga wajen Aunty Badiya zuwa Zamfara don ya yi hutun kirsimetin sa tare da Hajiyar Nahuce.
Satin ta biyu ta koma Jamus ta fara specialization din ta a otorhinolaryngology.
Daga lokacin da ta fara specialization din kasancewar wahalar sa bata kai ta MBBS ba ta kan samu lokacin kan ta da lokacin tunani, a lokacin abubuwa suka fara rikice mata. Soyayyar (her ex Habibu) ta kada ita wanwar. Ta soma tunani da neman hanyar samun labarin sa. Ba don ta kula shi ba, sai don kawai shes curious ga son ta san me yake ciki shi da gudan ran ta, don haka ta soma sha'awar bibiyar Habibu Nahuce a kafafen sadar da zumunta, amma ko daya ba ya kai. As the busy person that he is, bashi da lokacin wadannan abubuwan (social media platforms). A karshe ta yanke shawarar duba shi a yanar gizo (google) ta san bazata kasa samun wani abu da shafe shi ba komai kankantar sa.
A wani marece ne ana tafka ruwan sama mai karfi a garin Frankfurt, ta rufe tagogi da kofar dakin ta, ta saki fararen curtains din dakin, sannan ta kunna (room-heater), ta dauko kwamfutar bisa cinya (loptop) ta shiga google kawai ta rubuta sunan sa HABIBU MUSTAPHA NAHUCE. Ita kuma googlesai ta kai ta LinkedIn. Kasancewar sa (professional platform). A can bata samu wani cikakken bayanin sa ba sai na profession din sa (as a Hotel Administrator), sai kuma a wani website na hotels din sa. A canne ta ga cikakken sunansa da cikakken bayaninsa a halin yanzu.