Sashe 6
Nahuce Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har ta kai karshen bayanin ta dattijon bai katse ta ba, sai ya kalle ta sannan ya kalli Raheenah, sannan ya kalli Nene, sai da ta dasa aya sannan ya ce,
"Allah mai iko, ikonSa da girma yake. Bana raba daya biyun wannan yarinyar jinin Adda Rahin ce. Don shi jinin mu karfi gare shi ba ya buya a ko'ina, balle a idanun mu.
Kwarai kun zo gidan su Adda Rahin, wadda ta kasance Yaya a gare ni. Kafin mu tattauna ku shiga cikin gida wajen iyali na a ba ku ruwa, ku yi sallah ku sha fura sannan mu zauna".
Suka mike suna godiya, farin ciki fal zuciyar Raheenah, ta kasa tashi daga gaban dattijon sai da ya ce je ki bada farali tukunna kin ji? Suna tafe zuwa cikin gida amma ba ta bar waiwayen dattijon ba don tsoro ta ke kada su shiga su fito su neme shi su rasa.
Har sai da ta ga ya dauko butar sa ya biyo bayan su sannan hankalin ta ya kwanta. Ta sa kai cikin gidan.
Matan aure hudu ne a gidan, Fulani duka farare sol da su kamar mijin su. Uwargidan na da tsagin kalangu a fuskar ta wadda Rahina ta ji an kira Dudu, sai Baba Amina da Goggo Tani da amaryar Sarki, Surbajo.
Cikin fulatanci ya yi wa matan nasa bayanin bakin, wadanda kowacce da aikin da suka samu tana yi a tsakar gida, ga yara da matasa suna ta shige da fice. Nan suka hau rige-rigen ba su ruwan alwala suna masu sannu da zuwa cikin karamci da girmama bako irin wanda Fulanin Girei suka gada.
A dakin uwargida Dudu aka shimfida musu karauni suka yi sallah, sannan kowacce cikin matan gidan ta shigo musu da kwanuka cike da kabakin abin da ta dafa wa iyalin ta, kasancewar 'yar tukunya ake yi a gidan wato kowacce tukunyar ta daban, Sarki kuma ya aiko musu da damammiyar fura ta ji kindirmo kwarya guda, da gasasshen nama mai laushi. Nan suka baje suna ci suna hirar karamcin mutanen gidan a tsakaninsu.
Rahinah kam farin ciki da doki sun hana ta iya cin komai, sun cika mata zuciya da ruhi taf! Sai furar ta sha bai fi ludayi uku ba da Nene ta matsa.
Sai da suka huta Sarkin Fulani ya shigo har tsakar gida aka shigo masa da kujerar shan iskar sa a waje tsakar gidan, ya zauna sannan ya ce Surbajo ta zo da bakin sa.
Sai da suka sake sabuwar gaisuwa sannan ya ce,
"Ko me ye dalilin su na zuwa neman gidan su Rahin?"
Yafendo ta nuna masa Raheenah da dan alin ta ta ce, "Domin mu sada wannan yarinya da dangin ta na uwa da uba, jikar Rahin ce, ba ta san kowa nata ba bayan Rahin, Allah bai sa Rahin ta taba gaya mata asalinta ba. Ni ma zance ne ya yi zance...to ka ji".
Ta ba shi labarin yadda aka yi ta yi zargin diya ce ga Umaru Modibbo, ta kwashe duk yadda suka yi da Raheenah shekarar baya ta fada masa, sannan ta dauko hoton Dada da Raheenah ta ba ta tun lokacin ta boye ta mika masa.
"Tsarki ya tabbata ga sarki Allah, wannan Yayata ce Rahin, uwarmu daya ubanmu daya. Ita ce ta haifi Umaru da Usmanu da Dije mai rasuwa.
Abinda ya faru shine, Umaru ya kasance bayan haihuwar wannan yarinya Raheenah uwar ta ta koma, sai ya auro wata mace daga zuwa ci rani Shagamu, ya taho da ita nan Girei, ya kawo ta gidan nan inda a da nan ne gidan da yake zaune tare da mahaifiyar sa (Rahin).
Wannan mata da ya aura babu tarbiyyah ko kankani a tare da ita, ta yi ta azabtar da Rahin da 'yar marainiyar Allah ba tare da sanin Umaru ba. Ko abinci ba su da kwanonshi a gidan nan. Ni lokacin bana nan don sana'ar mu ce kai shanu kudu ni da Ummaru, kuma in mun tafi muna jimawa ba mu waiwayi gida ba sai mun sayar da shanun da muka kai tas! A kan hanyar Umaru ta dawowa ya yi hatsari sai gawarsa aka kawo wa mahaifiyarsa, a lokacin ba a jima da ba shi sarkin Fulanin Girei ba.
Har gobe cikin mu babu wanda ya san abin da ya shiga tsakanin matar Umaru da Adda Rahin, bayan rasuwar Umaru ta hada komai nata da na yarinyar nan ta yi asubanci ta bar Girei. Matar Umaru kuma mai suna Kulu ta hada bakidaya shanun Umaru ta sayar ta kulle kudin ta bar garin nan kafin dawowa ta, don haka Rahin da jikanyar ta ba su karbi gadon Umaru ko kwandala ba. Kulu ta san makarkashiyar da ta yi mata ta korata inda har yau ba wanda ya kara ganinta cikinmu, don kawai ta wawashe gado ita kadai.
Bayan na dawo matata Dudu ta gaya min abin da suke zargi, cewa Kulu ta yi wa Adda Rahin barazanar kashe jikanyarta Rahinatu muddin ba ta bar Girei ba. Don dai ta cinye gado ita kadai. Ta sayar da komai na Umaru ta gudu cikin dare ba tare da sanin kowa ba.
Damuwar mu a lokacin ba ta ina Kulu ta tafi da dukiya ba ne ko dukiyar da ta handame sai ta ina Adda da Rahinatu suka fada?
Mun yi neman duniya ba mu same su ba. Abin kamar hadin baki, shi ma Usman bai kara zuwa ba tunda ya tafi Karatu Zaria.
In takaice muku zance, Usman bai waiwayi gida ba sai bayan shekaru biyar da barin Rahin Girei, a lokacin babu wayar tarho, san da ya dawo ya gama karatu har ya samu aiki a Kaduna.
Da ya dawo ya tadda tashin hankalin da muke ciki na mutuwar dan uwansa, da rashin sanin inda mahaifiyar su Rahin da Rahinatu suka fada.
Gari-gari haka muka dinga yawo neman su Rahin, ni da Usmanu, a lokacin babu kafafen yada labarai ban da radio duk wani gari da yake makwabtaka da mu mun je mun bincika ba mu same su ba.
Fadin halin da Usman ya samu kansa a ciki a wancan lokacin ba zai yiwu ba, don gara mutuwar iyaye a kan batansu da ransu. A karshe dole Usman ya koma Kaduna ya ci gaba da aikinsa, amma akai-akai yana zuwa muna kara bincikawa Allah bai sa an dace ba.
A shekaru biyu da suka gabata ne wani dan garin nan ya zo mana da labarin ya ga Rahin a cikin Adamawa a kasuwa, ko kafin ya yi mata magana ta bace masa.
Don haka na gaya wa Usman, wanda a halin yau ya zama babban ma'aikaci a gwamnatin tarayyah, ni kuma an jima da maida sarautar Modibbo Umaru a kaina. Wato dai ni ne sarkin Fulanin Girei tsayin shekarun nan bayan rasuwar Modibbo Ummaru.
Usman ya zo muka durfafi cikin Adamawa cike da bakin cikin ashe duk wahalhalun nan da muke sha wajen neman su Rahin ashe ba nisa ta yi ba, don dai bawa ba ya hada sani da UbangijinSa ne. Kasancewar zuwa lokacin an samu ci gaban zamani mun kai hotunan Rahin kafafen yada labarai na Adamawa, mun saka cigiya musamman a talbijin. Kuma ba a fi sati biyu ana cigiyar ba wani likita daga asibitin jihar Adamawa ya bayyana kansa a matsayin wanda tsohuwa Rahin ta mutu a hannunsa a dalilin cutar ciwon zuciya na farad daya. Ya bada dukkan shaidun da suka tabbatar mana cewa Rahin ce.
Daga nan ne muka yi ta bibiya har muka samo muhallin ta, makwabtanta sun tabbatar mana cewa ta rasun, kuma tana da jika budurwa wadda aka biya wa karatu a kasar waje ta tafi shekara guda kenan da tafiyar tata a lokacin binciken namu. Amma su basu san kowacce kasa ce ba.
Yau Allah cikin ikonsa ga Rahinatu ta dawo gidan su da kafafunta. Zan so ganin murmushin da zai bayyana a fatar bakin Usmanu, don haka tunda kun zo da mota, gobe in Allah ya kai mu za mu yi asubanci zuwa Kaduna, in sada Rahinatu ga Babanta Usmanu".
Raheenah ba ta san sanda ta karasa gaban dattijon ta rike kafafunsa tana kukan farin ciki ba. Yafendo da Nene sai kabbara suke yi suna gode wa Allah tare da yi wa Daada Rahin addu'ar neman rahma da gafarar Ubangiji.
Kafin su kwanta sai da Nene ta kira Ambasada ta gaya masa duk halin da ake ciki, cikin farin ciki ya ce shi ma zai same su a Kadunan don gobe zai baro Abuja, da sun shiga Kaduna ta shaida masa don za su tsaya a can su jira isowarsu.
A daren duk 'ya'yan Sarkin Fulani da ke gidan aure sai da iyayensu mata suka aika musu suka zo suka ga Raheenah duk da cewa dare ya yi. Nene ta yi alkawarin dawo musu da Raheenah in sun sake zuwa karshen shekara, idan kuma ta gama karatunta bakidaya za ta dawo Girei bakidaya ko wajen kanin Baban nata.
Godiya da fatan alkhairi gami da shi albarka su Yafendo sun sha shi daga Sarkin Fulani da iyalin sa, washegari bayan sun yi wanka sun karya kumallo daga tukwanensu Dudu suka kama hanyar Kaduna tare da Sarkin Fulani a gaban mota da babban dan sa Ilyasu.
Tun a hanya ya sanar da Alhaji Usman cewa ga su nan tafe tare da diyar Modibbo Ummaru ta hannun Adda Rahin, wadda aka ce ta tafi karatu ketare. A lokacin Alhaji Usman yana Abuja, amma haka ya ajiye duk ayyukan da ke gaban sa ya taho Kaduna a safiyar don su yi taho mu gama, ya kuma sanar da matar sa cewa ta shirya musu kyakkyawar tarba ta musamman.
Suna shiga Kaduna Nene ta kira Ambasada ta gaya masa, ya ce ai su tuni suna cikin kaduna suna jiran su, Ilyasu ne ya bai wa Nene lambar Alhaji Usman ta tura wa Ambasada don haka Alhajin da kan sa ya kwatanta wa direban Ambasada gidan sa wanda ke unguwar Sarki.
"Allah mai iko, ikonSa da girma yake. Bana raba daya biyun wannan yarinyar jinin Adda Rahin ce. Don shi jinin mu karfi gare shi ba ya buya a ko'ina, balle a idanun mu.
Kwarai kun zo gidan su Adda Rahin, wadda ta kasance Yaya a gare ni. Kafin mu tattauna ku shiga cikin gida wajen iyali na a ba ku ruwa, ku yi sallah ku sha fura sannan mu zauna".
Suka mike suna godiya, farin ciki fal zuciyar Raheenah, ta kasa tashi daga gaban dattijon sai da ya ce je ki bada farali tukunna kin ji? Suna tafe zuwa cikin gida amma ba ta bar waiwayen dattijon ba don tsoro ta ke kada su shiga su fito su neme shi su rasa.
Har sai da ta ga ya dauko butar sa ya biyo bayan su sannan hankalin ta ya kwanta. Ta sa kai cikin gidan.
Matan aure hudu ne a gidan, Fulani duka farare sol da su kamar mijin su. Uwargidan na da tsagin kalangu a fuskar ta wadda Rahina ta ji an kira Dudu, sai Baba Amina da Goggo Tani da amaryar Sarki, Surbajo.
Cikin fulatanci ya yi wa matan nasa bayanin bakin, wadanda kowacce da aikin da suka samu tana yi a tsakar gida, ga yara da matasa suna ta shige da fice. Nan suka hau rige-rigen ba su ruwan alwala suna masu sannu da zuwa cikin karamci da girmama bako irin wanda Fulanin Girei suka gada.
A dakin uwargida Dudu aka shimfida musu karauni suka yi sallah, sannan kowacce cikin matan gidan ta shigo musu da kwanuka cike da kabakin abin da ta dafa wa iyalin ta, kasancewar 'yar tukunya ake yi a gidan wato kowacce tukunyar ta daban, Sarki kuma ya aiko musu da damammiyar fura ta ji kindirmo kwarya guda, da gasasshen nama mai laushi. Nan suka baje suna ci suna hirar karamcin mutanen gidan a tsakaninsu.
Rahinah kam farin ciki da doki sun hana ta iya cin komai, sun cika mata zuciya da ruhi taf! Sai furar ta sha bai fi ludayi uku ba da Nene ta matsa.
Sai da suka huta Sarkin Fulani ya shigo har tsakar gida aka shigo masa da kujerar shan iskar sa a waje tsakar gidan, ya zauna sannan ya ce Surbajo ta zo da bakin sa.
Sai da suka sake sabuwar gaisuwa sannan ya ce,
"Ko me ye dalilin su na zuwa neman gidan su Rahin?"
Yafendo ta nuna masa Raheenah da dan alin ta ta ce, "Domin mu sada wannan yarinya da dangin ta na uwa da uba, jikar Rahin ce, ba ta san kowa nata ba bayan Rahin, Allah bai sa Rahin ta taba gaya mata asalinta ba. Ni ma zance ne ya yi zance...to ka ji".
Ta ba shi labarin yadda aka yi ta yi zargin diya ce ga Umaru Modibbo, ta kwashe duk yadda suka yi da Raheenah shekarar baya ta fada masa, sannan ta dauko hoton Dada da Raheenah ta ba ta tun lokacin ta boye ta mika masa.
"Tsarki ya tabbata ga sarki Allah, wannan Yayata ce Rahin, uwarmu daya ubanmu daya. Ita ce ta haifi Umaru da Usmanu da Dije mai rasuwa.
Abinda ya faru shine, Umaru ya kasance bayan haihuwar wannan yarinya Raheenah uwar ta ta koma, sai ya auro wata mace daga zuwa ci rani Shagamu, ya taho da ita nan Girei, ya kawo ta gidan nan inda a da nan ne gidan da yake zaune tare da mahaifiyar sa (Rahin).
Wannan mata da ya aura babu tarbiyyah ko kankani a tare da ita, ta yi ta azabtar da Rahin da 'yar marainiyar Allah ba tare da sanin Umaru ba. Ko abinci ba su da kwanonshi a gidan nan. Ni lokacin bana nan don sana'ar mu ce kai shanu kudu ni da Ummaru, kuma in mun tafi muna jimawa ba mu waiwayi gida ba sai mun sayar da shanun da muka kai tas! A kan hanyar Umaru ta dawowa ya yi hatsari sai gawarsa aka kawo wa mahaifiyarsa, a lokacin ba a jima da ba shi sarkin Fulanin Girei ba.
Har gobe cikin mu babu wanda ya san abin da ya shiga tsakanin matar Umaru da Adda Rahin, bayan rasuwar Umaru ta hada komai nata da na yarinyar nan ta yi asubanci ta bar Girei. Matar Umaru kuma mai suna Kulu ta hada bakidaya shanun Umaru ta sayar ta kulle kudin ta bar garin nan kafin dawowa ta, don haka Rahin da jikanyar ta ba su karbi gadon Umaru ko kwandala ba. Kulu ta san makarkashiyar da ta yi mata ta korata inda har yau ba wanda ya kara ganinta cikinmu, don kawai ta wawashe gado ita kadai.
Bayan na dawo matata Dudu ta gaya min abin da suke zargi, cewa Kulu ta yi wa Adda Rahin barazanar kashe jikanyarta Rahinatu muddin ba ta bar Girei ba. Don dai ta cinye gado ita kadai. Ta sayar da komai na Umaru ta gudu cikin dare ba tare da sanin kowa ba.
Damuwar mu a lokacin ba ta ina Kulu ta tafi da dukiya ba ne ko dukiyar da ta handame sai ta ina Adda da Rahinatu suka fada?
Mun yi neman duniya ba mu same su ba. Abin kamar hadin baki, shi ma Usman bai kara zuwa ba tunda ya tafi Karatu Zaria.
In takaice muku zance, Usman bai waiwayi gida ba sai bayan shekaru biyar da barin Rahin Girei, a lokacin babu wayar tarho, san da ya dawo ya gama karatu har ya samu aiki a Kaduna.
Da ya dawo ya tadda tashin hankalin da muke ciki na mutuwar dan uwansa, da rashin sanin inda mahaifiyar su Rahin da Rahinatu suka fada.
Gari-gari haka muka dinga yawo neman su Rahin, ni da Usmanu, a lokacin babu kafafen yada labarai ban da radio duk wani gari da yake makwabtaka da mu mun je mun bincika ba mu same su ba.
Fadin halin da Usman ya samu kansa a ciki a wancan lokacin ba zai yiwu ba, don gara mutuwar iyaye a kan batansu da ransu. A karshe dole Usman ya koma Kaduna ya ci gaba da aikinsa, amma akai-akai yana zuwa muna kara bincikawa Allah bai sa an dace ba.
A shekaru biyu da suka gabata ne wani dan garin nan ya zo mana da labarin ya ga Rahin a cikin Adamawa a kasuwa, ko kafin ya yi mata magana ta bace masa.
Don haka na gaya wa Usman, wanda a halin yau ya zama babban ma'aikaci a gwamnatin tarayyah, ni kuma an jima da maida sarautar Modibbo Umaru a kaina. Wato dai ni ne sarkin Fulanin Girei tsayin shekarun nan bayan rasuwar Modibbo Ummaru.
Usman ya zo muka durfafi cikin Adamawa cike da bakin cikin ashe duk wahalhalun nan da muke sha wajen neman su Rahin ashe ba nisa ta yi ba, don dai bawa ba ya hada sani da UbangijinSa ne. Kasancewar zuwa lokacin an samu ci gaban zamani mun kai hotunan Rahin kafafen yada labarai na Adamawa, mun saka cigiya musamman a talbijin. Kuma ba a fi sati biyu ana cigiyar ba wani likita daga asibitin jihar Adamawa ya bayyana kansa a matsayin wanda tsohuwa Rahin ta mutu a hannunsa a dalilin cutar ciwon zuciya na farad daya. Ya bada dukkan shaidun da suka tabbatar mana cewa Rahin ce.
Daga nan ne muka yi ta bibiya har muka samo muhallin ta, makwabtanta sun tabbatar mana cewa ta rasun, kuma tana da jika budurwa wadda aka biya wa karatu a kasar waje ta tafi shekara guda kenan da tafiyar tata a lokacin binciken namu. Amma su basu san kowacce kasa ce ba.
Yau Allah cikin ikonsa ga Rahinatu ta dawo gidan su da kafafunta. Zan so ganin murmushin da zai bayyana a fatar bakin Usmanu, don haka tunda kun zo da mota, gobe in Allah ya kai mu za mu yi asubanci zuwa Kaduna, in sada Rahinatu ga Babanta Usmanu".
Raheenah ba ta san sanda ta karasa gaban dattijon ta rike kafafunsa tana kukan farin ciki ba. Yafendo da Nene sai kabbara suke yi suna gode wa Allah tare da yi wa Daada Rahin addu'ar neman rahma da gafarar Ubangiji.
Kafin su kwanta sai da Nene ta kira Ambasada ta gaya masa duk halin da ake ciki, cikin farin ciki ya ce shi ma zai same su a Kadunan don gobe zai baro Abuja, da sun shiga Kaduna ta shaida masa don za su tsaya a can su jira isowarsu.
A daren duk 'ya'yan Sarkin Fulani da ke gidan aure sai da iyayensu mata suka aika musu suka zo suka ga Raheenah duk da cewa dare ya yi. Nene ta yi alkawarin dawo musu da Raheenah in sun sake zuwa karshen shekara, idan kuma ta gama karatunta bakidaya za ta dawo Girei bakidaya ko wajen kanin Baban nata.
Godiya da fatan alkhairi gami da shi albarka su Yafendo sun sha shi daga Sarkin Fulani da iyalin sa, washegari bayan sun yi wanka sun karya kumallo daga tukwanensu Dudu suka kama hanyar Kaduna tare da Sarkin Fulani a gaban mota da babban dan sa Ilyasu.
Tun a hanya ya sanar da Alhaji Usman cewa ga su nan tafe tare da diyar Modibbo Ummaru ta hannun Adda Rahin, wadda aka ce ta tafi karatu ketare. A lokacin Alhaji Usman yana Abuja, amma haka ya ajiye duk ayyukan da ke gaban sa ya taho Kaduna a safiyar don su yi taho mu gama, ya kuma sanar da matar sa cewa ta shirya musu kyakkyawar tarba ta musamman.
Suna shiga Kaduna Nene ta kira Ambasada ta gaya masa, ya ce ai su tuni suna cikin kaduna suna jiran su, Ilyasu ne ya bai wa Nene lambar Alhaji Usman ta tura wa Ambasada don haka Alhajin da kan sa ya kwatanta wa direban Ambasada gidan sa wanda ke unguwar Sarki.