← Book details Masarautar Qamar Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 24

Sashe 9

Masarautar Qamar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A hankali ta fito daga toilet din tana fitar da wani kamshi har tazo tsakiyar dakin da angyara shi tass kamar ba’a taba kwanciya ba vanity table ta zauna tana kallon kanta olive skin dinta sai glowing takeyi ringing din wayarta ne yayi kara wanda tasan ba kowa bace face kilan mahaifiyarta a hankali ta tashi kamar wadda batasan taka kasa saidai ba kasa bace batason takawa tsantsar sarautar dake yawo a jikinta ne bata fuska tayi ganin Mai kiranta kin dauka tayi har ta tsinke karar wayarta ne ta karayin kara dauka tayi ta kanga a kunnenta muryar mai dadi da sautin amo tana ratsa dakin don da tsiwa take maganarta liya wai lapia kike kirana kamar wadda ta ci maki bashi daga dayan Bangaren liya wadda tagama shiryawa tace I just missed my twin sister i decided to check on her ko nayi laifi ne Neela takirata da karfi tace liya da bacin rai a muryarta dariya liya tayi tace wallahi kiyi sauri ki fito ko In kira basai na fada ba kindai san sauran su idan na kirashi Neela tayi sauri ta dafe zuciyarta tace bansan kalar wasannan dariya liya tayi tace Don’t forget to wear green palazzo and white shirt

Tun jiya na sanya akawo maki kayan so kiyi sauri kinsan mu suke jira tunda Mai Martaba da kanshi yace Aikinmu ne Neela da take saurarenta cike da taikaici tace I know I know go to hell Liya I hate you liya dariya tayi tace I love you Neela kashe wayarta tayi . Twin sister dinta kenan she always gets on her Nerves shiryawa tayi cikin kayan da Liya tace akawo mata tun jiya wandon palazzo ne na prada da wata rigar gucci da takalma da scarf

Inner wears ta sanya sannan ta fesa turaruka masu tsananin tsada ta shirya cikin kayan wadanda elegance dinsu sun fito ko ta ina kayan ba karamin kyau sukayi mata ba don dan karamin scarf ta daura kusan duka rabin gashinta ya zuba a baya sai kamshin mai masu dadi takeyi Kallon kanta tayi A madubi sannan taga yadda tayi kyau murmushi tayi wanda ya fito mata da dimples dinta she’s proud of her beauty don masarautar tasu sai kana da kyau za’a san da existance dinka shiyasa subira tayi masu fintinkau saboda tsanin kyau da mulkinta Tunawa kawai da tayi da ita taji zuciyar ta na tashi bloddy Hell tace saboda tasan ta kusa dawowa ba dadewa Neela tace koda yake da da yanzu ba dayaba ,ba zata iya daukar iskancin subira ba zuciyarta ce tace kullum sai kince da da yanzu ba daya ba Amman kullum dayane saboda ba abinda kuke iyawa a gaban yarinya mai jin kan tsiya.

Tsoki tayi ta fito katon parlon ta wanda yake cike da abubuwan more Rayuwa tunda ga floor din parlon da chandeliers din da suke à sama wanda suke bama ko ina wani irin haske wall bracket din kuma masu wani irin designs na royalty masu bala’in kyau fitilu ne ko ta ina haske kam har zai iyayi ma mutum illa saboda parlon baida wani hayaniya sosai don American parlor ne ko royal chairs babu kujerun l-shape designs masu kyau

Tana fitowa kuyangin Dukansu suka dukar da kai kujerar dining daya daga cikin su ta ja mata ta zauna sai kuma daya daga cikinsu tazo da sauri ta zuba mata Irish da liver sauce sai coffee cewa tayi su ta zataci abinci don duk sunyi mata tsaye da sauri kuyangin suka fita waje suna jiranta tagama cin abinci ta take hankalin kwance saidai wayarta na hannunta tana duba wani abu a Instagram kara taji wadda karar ta kusa firgitata,Neela da tasan ba wanda zaiyi hakan sai liya don waye ya isa bama wanda ya isa liya janye plate din Neela tayi ta faracin chips din tace shey you’re here enjoying your breakfast nikuma banci komai ba haba Neela tana maganar tana dafe zuciyarta sannan tace Baki da kirki kallo daya zakayi Neela kasan ta gaji da halin yar Uwarta wadda kammanin su daya don idan zaka tsaya kana kallon su baka isa ka gane daya acikinsu ba,saboda kamanninsu. liya cin cips din take harda mugunta while Neela kallonta kawai takeyi har ta cinye sannan ta dauki coffee din dake gefenta ta shanye dariya tayi tace yanzu naji Daidai tashi mu tafi Neela hararta tayi tace liya daga yau kada ki kara shigo mani chamber dafe zuciyarta tayi sai ta bata fuska tace haba my twin kin sanya an raba mana chamber yanzu kuma so kike in daina shigowa chamber kwata kwata tana dafata tsoki Neela tayi ta ture ta dariya liya tayi tace muje

Tare suka jero suna tafiya Dukansu kuyangin a bayansu wasu kuma a gabansu olive skin dinsu sai shining yake with the help of the sun don Duk bala’inka baka isa kace ga Neela ba ,ko liya saboda tsananin kammannisu moto ci aka bude ma kowace a cikinsu sannan suka shiga baya Daidai inda su Bintu da sauran mutanen da suka zo dasu suka tsaya Bintu da sun kusa awa uku suna jira Dukansu sun gaji ga yunwar da sukeji kamar mi saidai hankalin ta baki daya yana wurin Hurriya da har yanzu bata ganta a wurin ba.

Kallon princesses guda biyu masu kama daya sukeyi su Dukansu kamar kauyawa maza da matan duka kallonsu sukeyi kyau, siga, gayu ,sa’ar rayuwa da mulki kawai suke gani lahaula wala kuwatta illah Billah kawai Bintu take cewa kamar rana haka suka fito don sun haske ko ina don kowa su yake kallo

Kuyangin a gaba da bayansu sukuma a tsakiya Har sukazo inda aka tanadar masu su kadai don su zauna kujerun kansu abin kallone

Su Bintu natsuwa sukai wurin ya dauki wani irin shiru liya da Neela kallon kowa sukeyi da isa kuma da sarauta da idanunsu masu kaifi
Kuyangin kuma duk sun dukar da kansu a tsaye magana liya tayi da kuyangar dake kusa da ita

Ita kuma ta isar da abinda tace ga uban kuyangu da bayi.

Hurriya tun dazu ta tashi lokacin da ta tashi sai taga ba kowa a dakin don haka ta fito ganin kuyangu tayi duk suna ta hidimar su kowa da abinda yakeyi wanka takeson tayi don jikinta duk yayi tsami bata matsa daga inda take ba tsaye saiga Kumurci yazo da ledar kayanta da mamaki yake kallonta Saboda yaga sauran yan uwanta wurin da suke jiran Gimbiya Batatuma da Gimbiya shawata cike da mamaki yace ya akayi Bakije ba banza tayi dashi,Hurriya kamar bada ita yake magana saida ta jima sannan cikin muryar ta Mai tsanani dadi tace bani kayana ta ida maganar tana tsotsar bakinta kadan
Kumurci kallonta yake yana kara tasbihi aranshi yarinyar Allah yayi mata tsananin kyau ga wani uban kwarjini da take dashi ita kam da tasan yadda daurewar fuska keyi mata kyau data rage daurewa tana dariya kilan mazan masarautar hankalin su bazai dauku da kyawunta ba

Kallon kayan jikinta yayi tun na jiya ne wanda yaganta dasu ba hijab ko dankwali babu don duka gashin yayi baya ya sauka a bayanta tsaki Hurriya tayi tace malam ka samu Tv ne?kumurci da yadan daburce cike da borin kunya yace ga kayanki Hurriya kallon kayan tayi sannan tace ka ajiye zan dauka da mamaki yake kallonta don ba’a taba yi mashi irin haka ba Hurriya kam ta rungume hannunta tana kallonshi ido cikin ido kwarjin tayi mashi sosai don haka ya janye idonshi akwai abinda yakeson gaya mata Amman bai iyawa saboda yadda bakinshi yayi mashi nauyi juyawa yayi ya tafi ita kuma Hurriya tayi tsoki ta kalli wata kuyanga sannan tace ina zata tayi wanki Kuyangar sakin baki tayi tana kallonta don sauran kadan ta ruga saboda kyauwunta da gashinta kallonta kuyangar kawai takeyi Hurriya da ranta ya fara baci don ta tsani kallo itama cike da rainin wayau tace wai Tv na Zamar maki ne hajajju Aa baiwar Allah kinada kyau ina jiye maki tsoro ne ga kuma kina da gashi kuma naga shigar kamar bata musulma ba tsoki Hurriya tayi tace akwai wata doka ta sanya kayane? Girgiza mata kai kuyangar Tayi tace ina guje maki karnunkan masarautar nan ne maza da mata

Hurriya tace kinsan fundamental Human right?girgiza kai tayi Hurriya akwai Right of choice yanzu idan naga dama zanyi yawo yadda nakeso kuma ba wanda ya isa yayi depriving right dina so shiga zanyi wadda nikeso hakajju iyakar ki kallo

Kuyangar tace iyakata kallo kuwa shiga kuma duk wadda kika ga dama kiyi zaki basu labari ne a masarautar Qamar Hurriya dage rigarta tayi ta daureta daga gefe shafafen cikin ta wanda sai daukar ido yake sai kuma wata yar sarka ta gold da take like a cibinta ta fito kallon matar tayi tace kafin In fara bada labari ke ya kamata ki fara basu labari tace munafuka magulmaciya kuyangar mutuwar tsaye tayi tana kallon shafaffen cikin Hurriya ko kyaftawa batayi Hurriya tsoki tayi ta saki rigarta tace sakara munafuka ta barta baki sake don kam taji kunya kuyangar sosai Hurriya tayi gaba abinta tabar ta tsaye tambayar wata tayi aiko ba bata lokaci ta rakata har inda suke wanki bata da sabulu don haka ta kalli wadanda suke wanki a wurin wanda suma suke ta kallonta
Tsoki tayi ta kalli wata da take kallonta kamar zata lasheta sabulu ta gani da ruwa a gefenta don haka Hurriya ta zuba ruwa cikin bokitin dake gefen yarinyar ta dauki kayan da tasan zata sanya yau saboda idan tace zata wanke duka zai dauketa lokaci don haka kala daya da zata sanya yanzu ta sanya wandone palazzo da yar top ta duka ta fara wankewa
Chapter 9 · 0% Book details