← Book details Masarautar Qamar Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 5 OF 24

Sashe 5

Masarautar Qamar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bulalar suka kara zuba ma laminde Hurriya zuwa tayi ta ture ta tana masu wani kallo Mai unguwa ne ya kalli dogarawan sannan idonshi na taruwa da kwalla yace don Allah kuyi hakuri ku taimaka kuyi hakuri ta gane kuskurenta yanzu Saminu ya kalli Kumurci wanda yake kallonsu yana kallon Hurriya wadda tayi ligis Kumurci yace sharadi dayane zamu baku Mai unguwa yace ka fadi koma wani irin sharadi ne zamu cikashi In Sha Allah murmushi yayi sannan yace ko matarka ta bimu masarautar Qamar ko kuma wannan matsiyaciyar ya nuna Hurriya shiru Mai unguwa yayi Hurriya da idonta sukayi jajir ta dago tana kallonshi wani murmushin mugunta yayi mata laminde tayi sauri tace ni zanje wallahi ku kyale yar marainiyar yar nan ku taimaka don Allah Hurriya kallon laminde take wadda banda kuka ba abinda take matar ta sota duk da hali na kin kulawa da take bata Amman bata taba gajiyawa da ita ba laminde ta kalli maiunguwa da idon shi sukai ja tace ga Hurriya nan don Allah ka kula da ita Maiunguwa cewa yayi laminde tare zamu tafi mubar Hurriya a garin nan ni zan biki murmushi tayi tace idan mun tafi kuma mubar ma wa ita? Hurriya da zuciyarta tagama karewa ta bude baki kamar tana tsoron magana tace I will go with them cewa tayi banji Mai kikace ba Hurriya tace zan bisu Kumurci wani murmushi ya saki yace da kin taimaki tsohuwar da take tsugune tana rokona Don wannan matar idan har ta bimu sai na sanya ta Zama baiwa mafi kaskanci a masarautar Qamar kuma sai na tabbatar da ko wani kaskantar bawa ya kusanceta yayi dariya Hurriya kam idonta kadai inda ka kalla zakasan tana cikin zallar bacin rai ga galabaitar da duk tayi laminde girgiza kai kawai take tace ba inda zaki ni zan tafi tana kuka tana girgiza kai Hurriya kam abinda bata tabayi ba shi tayi lallashi don bata iya ba ma kwata kwata Amman daga jin yanayin muryarta zakasan kokari ne take tana magana zan dawo zan kira shine abinda tace Kumurci kam kokarin turata ya farayi juyawa tayi ta kalleshi tace kada ka sake ka taba ni da kazamin hannunka a irin yanayin da tayi maganar zaka san ba abinda bazata iya ba idan har ya kara Kumurci kallonta yayi yaga yadda idonta ba wani abu wai shi tsoro shiru yayi sannan yace yarinya zaki gane kurenki a masarautar Qamar don karnukan suna da yawa ya fada a zuciyar shi.

Hurriya jikinta duk ya mutu saboda dukan da akayi mata laminde kuka kawai takeyi don abun yafi karfin ta Jikinta sai kyarma yake ledar dake yashe ta kayanta ta dauka

Kumurci ya kalli mutanen da dogarawan yace su fito su tafi kamarshi ake jira aka tasa kyayar samarin suna turasu kamar jakuna

Hurriya gashinta duk yayi budu budu saboda bata maida dankwalin da ta cire ba lokacin da zata rike hannun Kumurci shikam Kumurci da ya juyo ya kalli yadda take struggling yakejin gabanshi na faduwa saboda yadda yakejin zuciyar shi ya kosa su isa masarautar su Mai cike da zallar zalincin he can’t wait to have her in his bed

Cikin hiace din emirates din ake ta tura maza saida aka cika mota guda uku Hurriya dai tana tsaye bata matsa ba saboda duk duniya ta tsani taji jikin wani kusa da ita gashi duka marmatse suke saidai fa ko zata mutu a wurin bata shiga motar nan don waye ma baisan Hurriya Faisait hamood ba duk wanda yayi gigin tabata da hannunshi saidai yaji saukar mari

Daya daga cikin dogaren ne yazo ya zuba mata bulala ke yar matsiyaciya shiga banza tayi dashi don wani bansan kallo tayi mashi bata ko daga baki ba ballantana yayi tunanin zata bashi amsa kara mata wata bulala yayi har tana durkushewa kasa da kayanta shegiya matsiyaciya ki wuce ki shiga Dukanta ya fara kamar Allah ya Aiko shi yana zagin Hurriya da ta shiga motar Amman shiru tayi saidai fa ba hawaye amman idonta sunyi ja saboda radadi da azabar da take ciki Kumurci ne ya buga mashi tsawa yace shaho ya isa hakanan shaho badan ya gaji ba ya daina dukan ta ya lura wata isa gareta alhalin ita din ba kowa bace face kaskantarciya Kumurci ne yazo saitin da take yace Mai kike jira da bazaki shiga ba banza tayi dashi kamar batasan da ita yake magana ba kara tambayar ta yayi banza Hurriya tayi dashi har cewa yayi zai kira shaho ya kara mata still bata ko motsa ba Hurriya kam taki ko matsawa kowa mamakin Kumurci yake da aka ga yana lallabata saboda waye baisan Kumurci ba saida Hurriya ta mula sannan tace ban iya zama kusa da kowa cikin motar I want to seat alone kallon yadda take magana yake fuskar ta a daure kuma kamar tana bashi order abun ma dariya yaso ya bashi Amman da yake Kumurci ne yayi saurin murtuke fuska ya kalli motar da duk maza ne a ciki sannan ya fitoda mutum biyu yace ta shiga da kyar take tafiya Hurriya saboda dukan da tasha ,har ta kawo wurin cikin motar kayanta gam a hannunta kamar daman sune rayuwarta kusan duka mazan saida suka juyowa suna kallonta saboda kyaunta ga gashin dake yawo a bayanta tsawa Kumurci ya buga masu dukansu suka shiga taitayinsu Hurriya bayan ta zauna ta fara sauke ajiyar zuciya tunani take yanzu to ina rayuwa zata kaita lokacin da bata tsammani haka ya faru da ita saidai duk inda zata tana fatar Allah ya bata ikon jurewa don ga dukkan alama sun nuna ba wurin jin dadi bane a hankali ta duka ta nemo safa cikin kayanta ta sanya dukar da kanta tayi yadda ba wanda zai iya ganinta ta cire sarkar dake wuyanta da kuma dayar sarkar ta sanya su cikin safarta harda kudinta duka ta sanya su wayarta ce kadai ta bari a aljihunta tafiya ne suka fara Sosai don tunda ma aka fara tafiyar Hurriya wani bacci ya dauketa tafiya sukayi sosai don kusan tafiyar awa biyar sukai don lokacin har amfara kiran sallah la’asar shine suka tsaya domin yin sallah

Hurriya jin hayaniya ya sanya ta bude idonta a hankali nan taga sun tsaya masu gyada nata tallah masu rake panke awara duk da sauransu cikin rashin kuzari ta sauko Amman jikinta yayi mata mugun tsami don da kyar take tafiya wasu panke manya guda biyu ta siya aka bata canjin ta sannan ta koma chan gefe ta zauna ta fara cin abunta

A hankali take ci ba don dadi ba sai don yunwa Hurriya taji ankira ta da mamaki ta dago kanta sai taga Bintu.
[12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar

By Khadija (KMU)

Page 9&10

Mika ma Bintu fanke daya tayi kato cikin jin dadi ta amsa tace nagode Hurriya ,shiru Hurriya tayi tana kallon yadda Bintu ke cin panke a hankali ta kara kiran mai fanken cikin muryarta Mai dadi kara mika mashi kudin tayi tace ya bata na dari guda biyu ya kara bata mika ma Bintu tayi amsa tayi tace inason ki Hurriya sannan ta rinka cin fanken kamar bata taba cin abinci duniya ba Girgiza kai Hurriya tayi Bintu ce tace ma Hurriya kalli abinda dogarawa can keyi Hurriya mun bani Hurriya kallon saitin da dogarawan suke tayi taga sun sanya sun jera layi layin maza daban na mata daban Hurriya batasan ma cewar akwai mata ba sai yanzu da tagansu jere a layi kallon Bintu tayi tace tare dawa kukazo Bintu da har ta fara kuka ta kalli Hurriya tace da wadancan azzaluman dogarawan daga kai Hurriya tayi tace ya akayi kika biyosu kuka Bintu ta fara tace muna zaune a tsakar gida saiga kawar Larai nusaiba ta shigo daki suka shi itafa Larai nusaiba tace ga yan masarautar Qamar nan sunzo zasu dauki ma’aikata da bayi. Shine tace kawai ta tura ni aiki ba bauta ba suna biyan kudi Sosai kuma ita za’a rinka bama kudin ina labe inajin su har nusaiba ta fito kallona tayi tace kuma naji ance sun fison mata kyawawa kuma kinga Bintu ba daga baya ba sai Larai tayi dariya tace kedai bari ba karamin taimakona kikayi ba nusaiba zan yadda kwallan mangwaro In huta da kuda gshi kuma Abun riba biyu dariya kawai nusaiba tayi tace ai kin yanman albashin nata ko?? Larai tayi dariya tace abinda yafi albashi ma don bakaramin taimakona kikayi ba suka kalli Bintu Larai ai nasan ubanta baida matsala nusaiba kenan ya bani matsala ma yaga ikon Allah

Bintu ta kalli Hurriya dake kallonta shine fa suka sanya na biyo dogarawan Hurriya daga mata kai kawai tayi ta juya saitin dogarawan tana kallon tsantsar zalincin da sukeyi Maza da matan dake jere a layi ake cajewa duk abinda aka ganka dashi sai a amshe har cikin riga suke lalubar matan cikin tsantsar zalinci abun gwanin ban takaici Hurriya a hankali ta zaro sauran kudinta dake cikin aljihu ta sanya su cikin safarta gyara safar tayi yadda ba wanda zaiga abinda ke a cikin kafarta cikin sa’a kuma ba wanda ya kula da lokacin da ta dauke kudin Shaho ne da yake kusa da Kumurci suna zaune suna kallon duk abinda ake don kamar sune manya kaga wata yarinya Mai kyau kamar ita tayi kanta nifa bantaba ganin mai kyau irinta ba dogon gashinta ya bani mamaki nace anya bahaushiya ce kuwa ko yanayin shigarta kadai zata nuna maka haka saidai fa kaga yadda take kallonmu girgiza kanshi yayi Kumurci nifa idanuwanta tsoro suke bani Kumurci yarinyar can fa na cikin hadari saboda karnukan dake masarautar mu fa sunada yawa gashi ba babba ba yaro don ko nifa sai na lasa yana karasawa da lashe baki Kumurci wani kallon banza yayi mishi wanda ke hade da gargadi shiru shaho yayi cikin ranshi yace wallahi sai na lasa ai kaima nasan manufar ka munafuki
Chapter 5 · 0% Book details