← Book details Masarautar Qamar Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 24

Sashe 21

Masarautar Qamar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

sannan Hurriya ta fasa klin dinta guda daya ta zuba mata shi wani irin uban kara ta saki tana shure shure Hurriya murmushi tayi sannan ta barbada mata gishiri ta hada da matsa lemun tsami a ciwon

Saida ta sanya haule reza tayi mata yanka biyar sannan ta barbada mata ingredients dinta

Tun tana kuka har kukan ya daina fita ba imani kwata kwata tattare da Hurriya ta bude kular nan ta debo tafasassun ruwa ta watsa mata akafafunta duka biyun ai wasila suma tayi

Haule reza kallon irin launin azabar da Hurriya take mata tayi tana mamakin rashin tsoro da rashin imanin yarinyar nan. Ta tabbata zuwa gobe kafarta tayi mummunar konewa .

Haka Hurriya ta rinka binsu saida ta tabbata duka tayi masu azaba iri daya don duk saida haule ta daure masu baki sannan tayi masu yanka biyar biyar Hurriya ta zuba masu omo hade da gishiri da lemun tsami sannan ta kona kafafun da ruwan zafi

Bayan sun gama tace a a aske ma Hansa’u gashin kanta tass ita kuma wasila da Barira har yanzu tana binsu bashi ta wuce ta nufi makwancinta

Haule reza kallon bayanta tayi yadda take tafiya kamar tana tausayin kasa haka take takawa tunda take bata taba ganin mutum marar imanin Hurriya ba

Duk ihun da suke da neman ceton rai da suke ko dar bare gizau haka Hurriya ta rinkayi masu launin azaba don tasan ba wanda bai suma ba acikinsu

Tabb inji haule tace akwai kallo dai wurin nan saidai sune suka ja ma kansu daman ance in kasa wata ba kasan wataba.

Hello fans yanzu zan rinka posting from Monday to Thursday saidai daga Friday zuwa Sunday ba post

Idan kuma kun fiso a rinka skipping rana daya tohm I will be waiting for your opinions

Love xoxo❤️👼🏽
[12/02, 4:54 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar
A story about a mysterious palace

By Khadija (KMU)

27&28

Kwanciya tayi Hurriya tareda sauke ajiyar zuciya don yanzu ne zata iya Bacci cikin dadi don idan batayi masu hukunci ba gaskiya ba sunanta Hurriya Faisait Hamood ba.

Haule reza kam tana mamakin inda yarinyar nan ta samo kalar launin azabar datayi masu don bata taba ganin hakan ba saidai fa ba karya Hurriya muguwa ce tace sannan ta nufi makwancinta

Yau da safe da aka tashi aka iske duka yan click dinsu Barira suna jinya don kusan ihun wasila ya tadasu don azaba ta ko ina takeji kuka kam yinshi take kawai don a halin da take ciki da za’a cire kafar to da tanaso indai har zata rabu da ciwon da takeji.

Barira kam har garin Allah ya waye itada suwaiba to asume suke saida aka samu da kyar suka farfado irin ciwo daya ne Dukansu suke fama dashi Dukansu saidai kowa na mamakin wanda yayi masu wannan danyan aikin

Hurriya yau ta samu ta tashi da wuri don har sallahr asuba ta samu damar yinta da wuri. Tanajin sai jaje akeyi Bintu ce tazo da gudu tana haki ta kalli Hurriya sannan tace naji abinda ya faru gasu barira Amman don Allah kece?kice bake bace don Allah kice man haka Hurriya kallonta tayi sannan tace nice Bintu And idan suka kara koda hararata abun da zanyi masu sai yafi wannan Bintu kallon Hurriya tayi sannan tace haba Hurriya miyasa zakiyi haka kinga kafafunsu idan kika gani sai sun baki tausayi wallahi dama kin kyalesu sunje da halinsu tunda yanzu suma zasu ce zasu rama kema zaki ce zaki rama kuma ance sarkin yawa yafi sarkin karfi kuma ma kinsan kaura saurayin barira ne sai ance shaho saurayin Hansa’u ne

Bintu batasan duk maganar da takeyi Hurriya tayi tafiyarta

Juyawar da zatayi taga ba Hurriya saidai ganin inuwar Hurriya tayi

Hurriya tana fitowa saiga hauke reza wadda ta taya danyan aikin jiya

Kallon Hurriya tayi tana washe baki sannan tace Hurriya naga sako nagode kuma don Allah inson kibani dama yadda idon akace gobe su kara to bazasu kara ba

Hurriya shiru tayi mata har tagama babatunta batace komai ba

Kitchen taje inna hanne na kallonta tazo tace Hurriya an tashi naji danyan aikin da kika aikata baki kyauta ba

Hurriya dage girarta tayi tace banzo don inji kyautawa da rashin kyautawa wurin ki ba malama ki zuba min ruwan zafi in kama gabana

Inna Hanne kallonta take kamar statue zata iya cewa tunda Hurriya ta tashi daga rashin lafiya to yaune ta samu jin muryarta mai tsayi har haka inna hanne wadda tayi curr tana kallonta tsarki ya tabbata ga Allah sannan tace lallai kedin gimbiya ce duk aranta take maganar don kwata kwata bataji haushi ba

Inna Hanne daukar bokitin tayi ta zubo mata ruwan zafi suka jero tare inna hanne rike da ruwan Hurriya kuma rike da kayan wankanta har suka zo toilet

Hurriya wanka ta shiga tayi sannan ta fito ta nufi daki
Sai kallonta akeyi don ba inda maganar bataje ba ita tayi masu Hansa’u wannan hukuncin wasu ta burgesu wasu kuma ta basu tausayi wasu kuma zaginta kawai sukeyi but who cares

Shiryawa tayi cikin uniform dinta wadanda sukayi mata kyau Sosai

Comb ta dauka ta tsaga kanta hudu sannan tayi kalaba manya manya guda hudu wanda suka sauka har gadon bayanta nade gashin tayi har saida ya dawo Daidai keyarta sannan ta fesa turarenta ta fita

Sashen imad ta fara zuwa aikam cikin sa’a ta gyara ko ina har dayan dakin shi wanda yake bacci

Tanajin karar ruwa hakan ya tabattar mata da yana toilet don haka tana gama mopping ta fito ta wuce part din zinariya wanda tunda ta fara aiki bata taba gifta kofar data wuce ta kitchen ba

Don haka tana zuwa tayi wanke wanke sannan ta fara hada breakfast tanajinsu suna gulma murya can kasa kasa Amman sautim maganar su radam a kunnen Hurriya wata a cikin kuyangin ce tace hmmm labari da dumi duminsa fa

Kowa cewa yayi munajinki subira ta kusa dawowa fa ance sati mai zuwa zata dawo, wata acikinsu ta fara salati tana jajanta masu subira fa suna cikin matsala ta dade batazo kasar nan ba don haka dayawa kilan sun manta wacece subira AI kuma ba lallai kowa ya iya manta subira ba saboda irin record din da ta bari

Hurriya duk tanajinsu wata acikinsu tace shekara fa ta kusa zagayowa shiru Dukansu sukayi suna zare ido wata acikinsu tace nidai bani da kyaun da za’a rasani a masarautar nan

Jakadiyar zinariya ce ta shigo ta kallesu tace me kukeyi ku wuce ku kai abincin Dukansu daga mata kai sukayi itadai Hurriya na aikinta

Tana gama aikin ta fita ta nufi inda suke wanki tana zuwa ta iske wasba tana wasa da dan icce tana ganin Hurriya wasba ta saki iccen ta rugo wurinta tana dariya tace tun dazu nike jiranki Hurriya bata ko kalleta ba tayi gaba inda ta saba wanki

Kayan ta fara wankewa wasba kam ta samu wuri kusada Hurriya ta zauna tana ta bama Hurriya tatsuniya mai ban dariya duk intayi sai taga Hurriya fuskarta daure sai tace bari in canza haka wasba ta zauna tana bama Hurriya labarai masu ban dariya Amman Hurriya ko murmushi batayi ba bare dariya

Wasba kuma taki tafiya sai can wani yaro yazo ya kirata ance ana kiranta tashi tayi ta ruga tana tsalle ta juyo tayi ma Hurriya alama da hannu Inasonki

Hurriya tsoki tayi ta cigaba da wankinta tana waka

Yunwa ce ta fara galabaitar da Hurriya saboda tun tashinta yau bataci abinci ba don haka tana ida shanya kayan ta nufo dakinsu

Harabar wurin tagani tasan cewar ba lafiya ba don haka ba tare da bata lokaci ba kutso wurin

Kowa ita yake jira a taron mutanen da akayi ta riga tasan da haka bata damu ba taja kai tana niyyar shiga wurin shaho ne ya tare hanyar yana watsa mata idanunshi masu firgita ma mutane lissafi itama kalloshi tayi tare da tsirtar da miyau a kafarshi tace disgusting kaura ne yazo a 360 don ranshi yana matukar tafarfasa da wannan makirar yarinya mai kyau sai kace ita tayi kanta duk masarautar nan waye ya isa ya taba barirarshi ya kwana lafiya babushi
Sai ita ta watsa mata tuwo a fuska gashi kuma tayi masu wani irin salon launin azaba tabbas yau sai ya wulakanta

cikin zafin nama kaura ya daga dorinar shi zai zuba mata Hurriya da yau itama ranta yagama baci don bazata iya tuna when last tayi irin bacin ran nan ba ta rike dorinar da karfi tanayi mashi matsiyacin kallo wanda ke dauke da tsantsar mulki da kuma izza tace the moment you beat me with your filthy hands you’re going to be executed ta matso tana mashi whispering tace kana kuskuren dukana to hukuncika kisa

Ta saki bulalar ta tsotsi bakinta cikin isa da mulki tace duk wanda bai fasa dukana ba acikin ku Amman ku tabbata duk wanda yayi gigin kara tabani a masarautar nan da sunan duka to sai ya amshi laifin shi na taba lafiyar Hurriya Faisait Hamood this is a promise and try me and see ta watsa masu wani wukantacen kallo tace jakuna daku matsiyata ta shige cikin dakin tana barin kowa baki bude

Kaura da shaho kam kamar wasu duwatsu haka sukayi don sungani à idanun yarinyar duk wanda ya kara tabata to kilan lahira zai bakunta yadda ta furta kisa kuma yadda ta nuna hukunci mai tsanani mutum zai amsa saidai tayi matukar kunyata su

Shiru Dukansu sukayi tareda juyawa suka tafi cike da borin kunya

Ikon Allah yan wurin kowa ya rinka fada to miyasa basu daketa ba mi tace masu har haka watsewa akayi kowa da alajabin wannan Hurriyar

Sa’ade da karime suna kallon komai sa’ade ce tace wallahi na tsani waccar shegiyar Hurriyar karime tayi wata dariya tace naki akeji amman ki bari zamu yi maganinta a masarautar nan tunda kowa ya gagara maganin shegiyar

Bintu ce ta gifto matsawa tayi saitin su tace kafin kuyi maganinta ni Zan sanya tayi maganin ku mutanen kawai tana kallon yadda suka zare ido alamun shakka dariya tayi ta shige ciki

Sallah ta iske Hurriya nayi Bintu kallon yadda take sallar kawai tayi ta girgiza kai ta zauna tana jiran tagama sallahr
Chapter 21 · 0% Book details