Sashe 17
Masarautar Qamar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Amrah ce tace she really look like Layla Al- khasheem sai yanzu da ka fada na lura
Ammar ne ya kalli Hurriya yace sunyi kama Sosai ya sakar mata murmushi tare da cewa you look like Layla Khasheem daga yadda yayi maganar zakasan cewar Dukansu suna kaunarta don liya itama washe baki tayi
Hurriya kam duk ranta ya jagule don kamar tana zaune saman kaya ko garwashin wuta haka takeji tsoro da fargaba suna kara cikata
tanajin saukar idanunwan kowa akanta
Amrah ce tazo saitin Hurriya tareda dafa mata kafada tace mata can you be my friend da wani irin karfi Hurriya ta ture ta ta fadi kasa fuskarta na nuna zallar bacin rai tace wa ya baki damar taba ni tana binta da idanun masu nuna zallar bacin rai saidai tana kokarin saita kanta saboda batasan yanayi fuskarta ya canza saboda da wuya Hurriya ta canza yanayin fuskarta zuwa damuwa ko farin ciki ko firgice ko kuma gazawa ko gajiyawa da rayuwa fuskarta akoda yaushe a yanayi daya take wato ta daurewa wadda za’a iya kiranta bata da mutunci
Imad ne ya tashi yazo Daidai saitin Hurriya wadda take idonta har wani jaa yake kawowa
Shima imad din rannshi a matukar bace shida neela zuwa yayi zai dauke ta da mari Ammar yayi saurin rikeshi Imad please don’t touch her ba tarbiyya bane dukan mace.
Hurriya Dukansu kallonsu tayi ba tare da tace masu komai ba ta fita daga dakin Hamdan ne ya ruga zaibita Liya ta rikeshi
Amrah kam kuka takeyi sosai wanda yasanya duka hankalin su ya dawo kanta
Neela ta rungumota tana lallashinta Ammar shima lallashin yakeyi Imad tashi yayi ya shige daki zuciyarshi na tafarfasa sannan ya barsu a parlon
Hurriya har bata ganin gabanta da kyar take tafiya ga dare da yayi ga sanyi ga fargaba abubuwa duk sun hade mata
Da kyar ta kawo kanta dakinsu tsitt kakejin ko ina adakin wani irin shiru wurin ya dauka don da yawansu sunyi bacci .
Ahankali ta kwanta tare da lumshe idonta tana fadawa duniyar tunani tambayoyi take ma kanta ina wannan yaron ya iya yaren Amarich sannan yace suna kama da Princess Layla Al-Khasheem shin har yanzu kamarsu a bayyane take itada Layla
Zuciyar tace ta buga don tana tsoron kalubalen da zata iya fuskanta nan gaba idan har identity dinta ya fito fargaba tsoro kadaici duk sune suka suka cikata
Bacci ne ya fara fizgarta Mai cike da gajiya ahankali baccin ya fara nauyi saidai saukar Ruwa mai matukar sanyi ajikinta ne ya sanya ta farkawa da sauri kuma a firgice bata Ida warwarewa ba taji an kara zuba mata ruwan mai matukar sanyi ga yanayin sanyi irin na farkon January
Rungume jikinta tayi idanun ta da hakoranta na gab gab wani ruwan taji ankara zuba mata mai matukar sanyi numfashinta ne ya fara ja yana dawowa kirjinta yana wani irin duka gab gab kankame jikinta ta karayi numfashinta na rage sauri dariya suke a kunnenta suna ihu suna kashewa
Tafiya su barira sukayi suka barta tana kokarin saisaita numfashin ta saidai mi ba abinda take gani irin past dinta rayuwarta ta tabaya yadda kawunta yake zuba mata ruwan kankara yana dukanta ne ya dawo mata kanta ne ya farayi mata wani irin nauyi sai wani irin duhu da ta fara gani sannan numfashinta ya dauke.
Hello readers ya kuke tunanin salon labarin namu
Ya akayi Hamdan yayi wani yare wanda Hurriya kadai takejin yaren
Miye tsakanin Layla Al -Khasheem da Hurriya Faisait Hamood
Ga Amrah da Hamdan da suke tsanin son Hurriya mi yasa suke sonta?
Ga Barira da suke barazanar tsoma kansu a rayuwar Hurriya anya basu debo ruwan dafa kansu ba
Ga wasba yar yarinya Karama da Hurriya ke burgeta
Miye yake faruwa ne da kyauwawan masarautar Qamar wanda ya sanya ake kiran masarautar da mysterious palace
Wacece Hurriya?
Ku biyoni cikin labarin masarautar Qamar a hankali komai zai warware.
Waye star dinmu a maza?
Shaho,Kumurci,imad ko Ammar kuma Hamdan
Muje zuwa kawai don salon labarin namu ya bambamta da kowani irin labari.
[12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar
A story about a mysterious palace
By Khadija (KMU)
23&24
Kwance take male male cikin ruwa mai matukar sanyi wanda kwata kwata bata ko numfashi ba wanda ya lura bare ya ankara
Da kyar suka lallashi amrah aka sanya kuyangu suka tafi da ita chamber dinta Mai matukar kyau da daukar ido
ruwan wanka Neela tazo ta hada mata ta fito mata da kayan bacci sannan tayi mata addu'a tare da kashe mata wuta
Liya kam tare suka tafi itada Hamdan don ba wanda yace ma dan uwanshi komai har suka isa chamber dinshi
Ammar shima chamber dinshi ya nufa ya haye saman gado tare da lumshe ido yana tunanin duka abinda ya faru yau so yake ya hada komai wuri daya don samun ma'anar abun saidai ya kasa hada komai
Amman yarinyar tayi matukar bata mashi rai donmi zata ture Amrah shiru yayi yana tunanin kilan tana da uziri don kowa da uzirinshi.
Karfe 5:44 Allah ya kawo Bintu domin tada Hurriya sallah asuba saidai ganinta kwance ya sanya ta fasa ihu agigice tazo tarinka tadata tana Hurriya Hurriya ki tashi don Allah ki tashi ki daina bani tsoro inna lillah wa'inna ilaihi raji'un Bintu ta shiga furtawa tana bude ma Hurriya ido Amman shiru
Ruwa ta debo da sauri ta yayyafa mata tare da shafa mata a fuskarta bude idonta Hurriya tayi wanda sukayi matukar jaa wani seizure numfashin ta ya fara tana tari mai sarkewa don kamar zata mutu haka numfashin yakeyi ga kuma tarin yaki sassauta mata Bintu banda hawaye babu abinda yake kwarara daga idonta don ta rasa mi zatayi wanda zai taimaka ma Hurriya saidai kukan
Kirjin Hurriya taga yana sama yana kasa numfashinta yazama abnormal don abinda take yafi nada bintu sakinta tayi ta ruga ta fita aguje ta rasa ma inda zataje watar yar matashiyar budurwa tagani tace mata don Allah akwai likita anan yar budurwa tace Akwai inna hanne mai bada taimakon gargajiya idan ansamu mararsa lafiya godiya kawai tayi mata batasan ya akayi ba sai ganin ta tayi a kitchen. ganin kanta a kitchen datayi ya sanya ta fashe da wani irin kuka inna hanne ce ta kalleta tace ke kuma lafiya kike mana sintiri kina kuka
Bintu zuwa tayi ta rike mata kafafunta tace ki taimaka mani ki ceci rayuwar Hurriya ta kusa mutuwa ki taimkeni yatsine fuska hanne tayi sannan tace wacece kuma haka Hurriya yar doguwa mai kyau tureta hanne tayi tace ni likita ce da zaki zo ki tsareni da magiya
Ki taimake ni don Allah ko nawane nayi maki alkawarin idan ta warke zan baki shiru hanne tayi tana tunani kafin ahankali tace muje.
Barira dasu wasila ne sukaje wurin da Hurriya take yashe kwance Hansa'u ce ta ture mata dogayen kafafunta ahankali Hurriya ta bude idonta wanda suke rufe hakoranta suna gab gab kirjinta na sama na kasa binsu take kawai da kallo dariya suwaiba tazo tayi tana take mata yatsun hannunta ita kuma barira ta take dayan hannun da nuna itadin watace tayi dariya tace yau zan kwanta da wannan kaskantaciyar baiwar sannan na sanya a farfasa mata jikinta sai inbi tada gishiri a ko ina kuma kullum kowa da kowa acikinku zai kwanta da ita sannan zansa bawa mafi muni da kaskanci ya kwanta da ita ta fasa wata dariya su Hansa'u suma sukayi dariya Hansa'u ce ta kalli barira sannan tace ina fatar a aske mani gashi kanta murmushi barira tayi sannan tace angama
Wasila ce ta fashe da dariya tazo ta haye Hurriya tare da kama hannun rigarta zata farka mata riga
Hurriya kam ta kanta takeyi don numfashinta kiris ya rage ya kara daukewa Amman tana cikin tsananin tsoro don tabbas idan har ta bude mata baya dolene taga zanen tatoo din dake da tambarin daga inda ta fito nobody is allowed to see the tatoo idan ba haka ba rayuwarta will be at more risk don tatoo din shine yake rike da sirrin ko ita wacece miye zai faru da ita idan wani yaga sirrin dake Zane abayanta
Shiru tayi zuciyarta da kirjinta na wani irin bugawa hannun rigar aka farke wanda hakan ya kasance daidai da daukewar numfashinta.
Bintu da inna hanne da suka shigo yanzu wanda yayi Daidai da daukewar numfashin Hurriya da kuma ida farkewar hannun rigarta
Wani irin kyakyawan mari inna hanne ta dauke wasila dashi tana binsu da wani irin matsiyacin kallo rike kuncinta wasila tayi ta fita daga wurin a hankali Hansa'u ta bita a baya sauran ma Dukansu suka bita a baya duk a masarautar nan ba wanda Suke tsoro irin inna hanne da reza dan daya hatsabibiyace daya kuma fitinaniya ga uban karfi
Bintu kam rungume Hurriya tayi tana kuka inna hanne ta kalleta tace ta fita ta debo masu ruwan zafi Bintu ta tafi don samo ruwan zafin
Taba Hurriya inna hanne tayi saidai abinda tagani saida ya girgiza ta daman har yanzu tanada aljanun da suka so bude mata ido kenan to mi ya kawosu miyasa suka karantar da ita bayanin Hurriya abinda rabon da tasan wani abu game da rayuwar wani andade
Inna hanne kallon Hurriya take tana tunanin abinda tagani tattare da rayuwar yarinyar lallai Hurriya tana cikin hadari acikin masarautar nan don irin duhun da tagani da kalubalen dake lullube da ita sunan Allah kawai inna hanne take fada don ta dade bata ga Abu irin haka ba
Don kwata kwata aljanun da suke son bude mata ido sun tafi tare da karfin ikon Addu'a da azkar don bata ganin komai tafi shekara goma rabonta da budewar idon jinnu sai wannan karon mi hakan yake nufi Akwai matsala babbar matsala tattare da rayuwar yarinyar nan
Ammar ne ya kalli Hurriya yace sunyi kama Sosai ya sakar mata murmushi tare da cewa you look like Layla Khasheem daga yadda yayi maganar zakasan cewar Dukansu suna kaunarta don liya itama washe baki tayi
Hurriya kam duk ranta ya jagule don kamar tana zaune saman kaya ko garwashin wuta haka takeji tsoro da fargaba suna kara cikata
tanajin saukar idanunwan kowa akanta
Amrah ce tazo saitin Hurriya tareda dafa mata kafada tace mata can you be my friend da wani irin karfi Hurriya ta ture ta ta fadi kasa fuskarta na nuna zallar bacin rai tace wa ya baki damar taba ni tana binta da idanun masu nuna zallar bacin rai saidai tana kokarin saita kanta saboda batasan yanayi fuskarta ya canza saboda da wuya Hurriya ta canza yanayin fuskarta zuwa damuwa ko farin ciki ko firgice ko kuma gazawa ko gajiyawa da rayuwa fuskarta akoda yaushe a yanayi daya take wato ta daurewa wadda za’a iya kiranta bata da mutunci
Imad ne ya tashi yazo Daidai saitin Hurriya wadda take idonta har wani jaa yake kawowa
Shima imad din rannshi a matukar bace shida neela zuwa yayi zai dauke ta da mari Ammar yayi saurin rikeshi Imad please don’t touch her ba tarbiyya bane dukan mace.
Hurriya Dukansu kallonsu tayi ba tare da tace masu komai ba ta fita daga dakin Hamdan ne ya ruga zaibita Liya ta rikeshi
Amrah kam kuka takeyi sosai wanda yasanya duka hankalin su ya dawo kanta
Neela ta rungumota tana lallashinta Ammar shima lallashin yakeyi Imad tashi yayi ya shige daki zuciyarshi na tafarfasa sannan ya barsu a parlon
Hurriya har bata ganin gabanta da kyar take tafiya ga dare da yayi ga sanyi ga fargaba abubuwa duk sun hade mata
Da kyar ta kawo kanta dakinsu tsitt kakejin ko ina adakin wani irin shiru wurin ya dauka don da yawansu sunyi bacci .
Ahankali ta kwanta tare da lumshe idonta tana fadawa duniyar tunani tambayoyi take ma kanta ina wannan yaron ya iya yaren Amarich sannan yace suna kama da Princess Layla Al-Khasheem shin har yanzu kamarsu a bayyane take itada Layla
Zuciyar tace ta buga don tana tsoron kalubalen da zata iya fuskanta nan gaba idan har identity dinta ya fito fargaba tsoro kadaici duk sune suka suka cikata
Bacci ne ya fara fizgarta Mai cike da gajiya ahankali baccin ya fara nauyi saidai saukar Ruwa mai matukar sanyi ajikinta ne ya sanya ta farkawa da sauri kuma a firgice bata Ida warwarewa ba taji an kara zuba mata ruwan mai matukar sanyi ga yanayin sanyi irin na farkon January
Rungume jikinta tayi idanun ta da hakoranta na gab gab wani ruwan taji ankara zuba mata mai matukar sanyi numfashinta ne ya fara ja yana dawowa kirjinta yana wani irin duka gab gab kankame jikinta ta karayi numfashinta na rage sauri dariya suke a kunnenta suna ihu suna kashewa
Tafiya su barira sukayi suka barta tana kokarin saisaita numfashin ta saidai mi ba abinda take gani irin past dinta rayuwarta ta tabaya yadda kawunta yake zuba mata ruwan kankara yana dukanta ne ya dawo mata kanta ne ya farayi mata wani irin nauyi sai wani irin duhu da ta fara gani sannan numfashinta ya dauke.
Hello readers ya kuke tunanin salon labarin namu
Ya akayi Hamdan yayi wani yare wanda Hurriya kadai takejin yaren
Miye tsakanin Layla Al -Khasheem da Hurriya Faisait Hamood
Ga Amrah da Hamdan da suke tsanin son Hurriya mi yasa suke sonta?
Ga Barira da suke barazanar tsoma kansu a rayuwar Hurriya anya basu debo ruwan dafa kansu ba
Ga wasba yar yarinya Karama da Hurriya ke burgeta
Miye yake faruwa ne da kyauwawan masarautar Qamar wanda ya sanya ake kiran masarautar da mysterious palace
Wacece Hurriya?
Ku biyoni cikin labarin masarautar Qamar a hankali komai zai warware.
Waye star dinmu a maza?
Shaho,Kumurci,imad ko Ammar kuma Hamdan
Muje zuwa kawai don salon labarin namu ya bambamta da kowani irin labari.
[12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar
A story about a mysterious palace
By Khadija (KMU)
23&24
Kwance take male male cikin ruwa mai matukar sanyi wanda kwata kwata bata ko numfashi ba wanda ya lura bare ya ankara
Da kyar suka lallashi amrah aka sanya kuyangu suka tafi da ita chamber dinta Mai matukar kyau da daukar ido
ruwan wanka Neela tazo ta hada mata ta fito mata da kayan bacci sannan tayi mata addu'a tare da kashe mata wuta
Liya kam tare suka tafi itada Hamdan don ba wanda yace ma dan uwanshi komai har suka isa chamber dinshi
Ammar shima chamber dinshi ya nufa ya haye saman gado tare da lumshe ido yana tunanin duka abinda ya faru yau so yake ya hada komai wuri daya don samun ma'anar abun saidai ya kasa hada komai
Amman yarinyar tayi matukar bata mashi rai donmi zata ture Amrah shiru yayi yana tunanin kilan tana da uziri don kowa da uzirinshi.
Karfe 5:44 Allah ya kawo Bintu domin tada Hurriya sallah asuba saidai ganinta kwance ya sanya ta fasa ihu agigice tazo tarinka tadata tana Hurriya Hurriya ki tashi don Allah ki tashi ki daina bani tsoro inna lillah wa'inna ilaihi raji'un Bintu ta shiga furtawa tana bude ma Hurriya ido Amman shiru
Ruwa ta debo da sauri ta yayyafa mata tare da shafa mata a fuskarta bude idonta Hurriya tayi wanda sukayi matukar jaa wani seizure numfashin ta ya fara tana tari mai sarkewa don kamar zata mutu haka numfashin yakeyi ga kuma tarin yaki sassauta mata Bintu banda hawaye babu abinda yake kwarara daga idonta don ta rasa mi zatayi wanda zai taimaka ma Hurriya saidai kukan
Kirjin Hurriya taga yana sama yana kasa numfashinta yazama abnormal don abinda take yafi nada bintu sakinta tayi ta ruga ta fita aguje ta rasa ma inda zataje watar yar matashiyar budurwa tagani tace mata don Allah akwai likita anan yar budurwa tace Akwai inna hanne mai bada taimakon gargajiya idan ansamu mararsa lafiya godiya kawai tayi mata batasan ya akayi ba sai ganin ta tayi a kitchen. ganin kanta a kitchen datayi ya sanya ta fashe da wani irin kuka inna hanne ce ta kalleta tace ke kuma lafiya kike mana sintiri kina kuka
Bintu zuwa tayi ta rike mata kafafunta tace ki taimaka mani ki ceci rayuwar Hurriya ta kusa mutuwa ki taimkeni yatsine fuska hanne tayi sannan tace wacece kuma haka Hurriya yar doguwa mai kyau tureta hanne tayi tace ni likita ce da zaki zo ki tsareni da magiya
Ki taimake ni don Allah ko nawane nayi maki alkawarin idan ta warke zan baki shiru hanne tayi tana tunani kafin ahankali tace muje.
Barira dasu wasila ne sukaje wurin da Hurriya take yashe kwance Hansa'u ce ta ture mata dogayen kafafunta ahankali Hurriya ta bude idonta wanda suke rufe hakoranta suna gab gab kirjinta na sama na kasa binsu take kawai da kallo dariya suwaiba tazo tayi tana take mata yatsun hannunta ita kuma barira ta take dayan hannun da nuna itadin watace tayi dariya tace yau zan kwanta da wannan kaskantaciyar baiwar sannan na sanya a farfasa mata jikinta sai inbi tada gishiri a ko ina kuma kullum kowa da kowa acikinku zai kwanta da ita sannan zansa bawa mafi muni da kaskanci ya kwanta da ita ta fasa wata dariya su Hansa'u suma sukayi dariya Hansa'u ce ta kalli barira sannan tace ina fatar a aske mani gashi kanta murmushi barira tayi sannan tace angama
Wasila ce ta fashe da dariya tazo ta haye Hurriya tare da kama hannun rigarta zata farka mata riga
Hurriya kam ta kanta takeyi don numfashinta kiris ya rage ya kara daukewa Amman tana cikin tsananin tsoro don tabbas idan har ta bude mata baya dolene taga zanen tatoo din dake da tambarin daga inda ta fito nobody is allowed to see the tatoo idan ba haka ba rayuwarta will be at more risk don tatoo din shine yake rike da sirrin ko ita wacece miye zai faru da ita idan wani yaga sirrin dake Zane abayanta
Shiru tayi zuciyarta da kirjinta na wani irin bugawa hannun rigar aka farke wanda hakan ya kasance daidai da daukewar numfashinta.
Bintu da inna hanne da suka shigo yanzu wanda yayi Daidai da daukewar numfashin Hurriya da kuma ida farkewar hannun rigarta
Wani irin kyakyawan mari inna hanne ta dauke wasila dashi tana binsu da wani irin matsiyacin kallo rike kuncinta wasila tayi ta fita daga wurin a hankali Hansa'u ta bita a baya sauran ma Dukansu suka bita a baya duk a masarautar nan ba wanda Suke tsoro irin inna hanne da reza dan daya hatsabibiyace daya kuma fitinaniya ga uban karfi
Bintu kam rungume Hurriya tayi tana kuka inna hanne ta kalleta tace ta fita ta debo masu ruwan zafi Bintu ta tafi don samo ruwan zafin
Taba Hurriya inna hanne tayi saidai abinda tagani saida ya girgiza ta daman har yanzu tanada aljanun da suka so bude mata ido kenan to mi ya kawosu miyasa suka karantar da ita bayanin Hurriya abinda rabon da tasan wani abu game da rayuwar wani andade
Inna hanne kallon Hurriya take tana tunanin abinda tagani tattare da rayuwar yarinyar lallai Hurriya tana cikin hadari acikin masarautar nan don irin duhun da tagani da kalubalen dake lullube da ita sunan Allah kawai inna hanne take fada don ta dade bata ga Abu irin haka ba
Don kwata kwata aljanun da suke son bude mata ido sun tafi tare da karfin ikon Addu'a da azkar don bata ganin komai tafi shekara goma rabonta da budewar idon jinnu sai wannan karon mi hakan yake nufi Akwai matsala babbar matsala tattare da rayuwar yarinyar nan