Sashe 6
Masarautar Qamar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani dogari ne ya kalli saitin dasu Hurriya suke kai tsinanu yan gidan matsiyata kuzo nan Hurriya ko motsi batayi ba Bintu tace mata Hurriya ki taso don Allah mu tafi kadasu dake mu banza Hurriya tayi da ita don maganar duniya taki ta tashi su Kumurci da shaho duka suna kallon abinda ke faruwa Bintu zuwa tayi ta shiga layi kwalla na zubo mata dogarin kau cikin hasala yazo saitin Hurriya kallon shi tayi cikin ido shine ke sanya hannunshi acikin rigar mata tashi tayi tsaye tace da uwarka da ubanka sune manyan matsiyata da har suka haifo wanda baisan dajar halitar mata ba kaskantarce kuma duka halayenka ke defining kaskanci Bullock wata muguwar ashariya shaho ya saki yace kaga wannan yarinyar Kumurci shuru yayi kowa ma shiru yayi yana jira yaga abinda zai faru Azuciye dogarin ya daga bulalar ya zuba mata a baya,mata da mazan wurin duka tsigar jikinsu tashi tayi suka juya itakam Hurriya kwalla ce ta zubo mata abinda ta dade batayi ba a rayuwarta wato kuka ta kasance a kullum rayuwarta ita Mai kukan zuci ce har tana jin dama zata iya irin kukan da Bintu keyi kilan ta samu sanyi ko yayane a ranta bulalar da yayi mata har cikin kanta taji azaba matuka wanda ta durkusa kasa hawaye na zubowa Daga hannunshi yayi da niyyar kara dukanta Kumurci ya rike hannun yace ya isa haka Garba ajiye hannunshi yayi ba don yaso ba sannan Kumurci ya yace tayi shiru sannan yace ki iya bakin ki idan ba haka ba to kina hanyar da bazata bullar dake ba don masarautar Qamar sai yayi murmushin mugunta Hurriya tana durkushe a hankali ta shafo hawayen don ta tabbatar da idan nagaske ne kallon hawayen tayi fa dagaske sune tasan ba lallai ta kara maimaita irin wannan kukan ba saboda yau sau biyu tayi kuka sannan ta kasance zuciyar ta Mai rauni ce saidai idan kaganta zakayi mamakin minene ya sauyata har haka da ba abinda yake girgiza ta ko ya bata mamaki kuma fa rashin ganin mutumcin kowa duk girman ka Daidai take da kowa don ko yaro yajefeta da magana sai ta maida mashi martani da wadda tafi tashi zafi shine kawai abinda ke sanya ta magana ko sai kuma idan tana tare da Bintu don Bintu zata iya awa tana mata magana baifi ta bata amsa daya ba saboda miskilancin ta Bintu har ta saba.
Kumurci kallonta yake saboda yasan akwai matsala a masarautar nan idan har Hurriya ta shige ta don ya lura bazata taba saukar da kanta kasa ba don haka yake tunanin hanya daya zai bi don tasamu barin masarautar batare da ansamu matsala ba shine yace baiwa ya samota kuma yaroki alfarmar ta zama Baiwa hakimi shine kawai mafita anma ta cigaba da haka baisan a hannun wazata mutu ba don princes da princesses din masarautar nan basu da imani ga kuma dayar matsalar don Kumurci yayi nadamar tahowa da Hurriya don yasan ba karamar wuya zatasha ba don ko yaran sarki kadai sun isheta don sun tsani wani yafisu kyau duk da daman masarautar kyawawa akafi kaiwa saidai ba wanda san dalili to zai iya rantsewa tunda ake kai kyawawan mata a masarautar baitaba ganin Mai kyaun wannan yarinyar ba don su kansu yaran mai martaba sai sun raina kansu.
Kallo daya zakayi mata kasan ta jigata ba karamar jigatuwa ba ma don wandon dake jikinta duk yayi datti fuskar ta kuma duk ta kumbura ga babu annuri kwata kwata saida fa annurin kyanta nan don sai salki takeyi Kumurci yace ki tashi ki shiga mota mu tafi yanzu bada hargagi yayi mata maganar ba don zuciyar shi ta dan karye kadan Kallonshi tayi da idanunta masu kyau da wani kaifi Kumurci ya daga mata kai tare da fatar kada tayi kafiya irin wadda tayi dazu.
A hankali take takawa amman zaka iya hango zallar mulki dake cikin tafiyar tata har ta shiga motar a hankali Kumurci girgiza kai yayi don ya hango kurar dake tafe da ita saidai Allah ya kyauta don aikin gama ya riga ya gama.
Bintu kam lokacin da ta koma layi cikin sa’a ba ba wanda ya lalubeta saboda hankalin kowa da ya koma kan Hurriya tanajin su karime dake gabanta cikin layi suna dariya suna cewa Allah ya kara sa’ade ce tace kinsan dadin da nikeji yadda ake bugun Hurriya karime tayi murmushi tace naki kika sani ni yarinya ta dade tana bani haushi shegiya ga isa ga iko sai kace wata shegiya sa’ade tace bata da mutunci Hurriya kinga cin mutunci da tayi ma mahaifina kuwa harda watsa mashi man awara akafa bayan tagama zazzageshi cikin mutane karime yo naji maganar tana yawo agari ki bari idan munje mu hade kai mu ci ubanta don ni ta dade tana bani haushi don kiga duk anguwar mu ace mazan ita kadai suke kallo to yanzu lokacin mune idan munje muyi maganin karuwa Mai ma maza jiki.
Bintu duk tanajinsu don harda kukan ta wurin da suka ce mata karuwa don tasan karya sukeyi Allah ya saka maki Hurriya inji Bintu ta fada cikin ranta.
Hurriya da ta koma wurin zamanta ta jinginar da kanta jikin window tana rufe idonta saidai kyarma kawai takeyi tana harhade hakoranta ga sanyi da ya isheta dankwalin da ta daura ta rufe gashinta dashi ta koma ta kwanta saidai sanyi ya matsa mata don bata daina jinshi ba ledar kayanta dake gabanta ta jawo saboda Asabe hada kyautar doguwar hijab tayi mata don lokacin har ta kawo zaure Asabe ta kwala mata kira a hankali asabe ta mika sabuwar hijab doguwa maroon tace Hurriya ko bazaki sanya ki fito ba ai nasan kina sallah to ki rinka sallah da ita inda so samu ne ki rinka fita da ita sai kuma ta tabe baki tace nasan yaudarar kaina nike ba inda zaki da ita tace Hurriya ki godema Allah don wallahi inasonki duk wanda yaji nayi kyauta sai ya kusa suma saboda mamaki kindai sanni da san kudin tsiya Hurriya batace mata komai ba har tagama maganar ta sai Hurriya ta mika mata ledar alamun ta sanya Asabe kam sauri ta dauko ta sanya Hurriya ta tafi ba godiya bare sallama.
Hijabin ta lalubo ta sanya ta dunkune kanta ciki a hankali bacci ya dauketa.
Sosai suka sha tafiya har suka iso Babbar masarautar Qamar bata sani ba don kowa ya fita a motar ya barta Kumurci ne ya kula da babu ita don har anfara kada kyayoyinsu Kumurci ya bude motar yazo inda take bacci da yake bai san sunanta ba don haka yace ke ki tashi mun iso shiru Hurriya tayi saida yayi mata magana kusan sau uku sannan ta bude idon wadanda sukayi mata nauyi Sosai har lokacin tana jin jikinta na kwankwatsa Kumurci yace ki fito munzo kuma kada kiyi ma mutane kafiya da rashin kunya don kece zaki sha wahala Hurriya da batajin karfin jikinta kwata kwata don ko yadda take numfashi zaka iya lura tashi tayi ta rungumo kayanta saidai tana tafiya biyu ta sake su Kumurci da yayi gaba yaji karar kayan da tasaki don haka ya juyo ya kalleta sannan ya daukar mata kayan suka fita duk da suna zuwa ana sallahr magriba don duhu har yafara Bayyana Amman bazaka iya gane cewa rana ce ko dare ba saboda haske da ya wadaci ko ina a babbar masarautar Qamar Masarautar kanta abun kallo ce girmanta gari guda ne tunda ga floor din dake kasan masarautar da ginin da akayi mutum zai gane cewar masarauta ce maiji da tsantsar dukiya kuma da karfin mulki .saidai Hurriya ba Abu daya wanda ya burgeta don kallo daya tayi ma komai wanda bata kara kallon wani Abu ba
Su Bintu da su karime kam Murna sukeyi kamar su ciji duwawunsu basu san masarautar Qamar, bawuri bane da ya kamata ace ya burgesu ba ko su kasance masu farin ciki Don masarauta ce wadda take cike da tsantsar zalinci da rashin imani.Kusan duk wadanda sukazo dasu sakin baki suke suna kallon ko ina.
Tasa keyarsu akayi ana bugunsu kamar tumaki suka shigo ciki inda ba abinda kake gani sai dagorawa dake tsaitsaye fuskar su hade kamar zasu je yakin basasa hannunsu daya narka narkan bulali Dayan kuma hannu dogayen bindigu kowane,Ba wanda bai firgita ba da ganin wadanan dogarawan don fuskar su babu alamun sassauci
Hurriya da da kyar take tafiya saboda zazzabin da take wani bakin dogari ne ya sakar mata bulala wadda saura kadan ta fadi da kyar ta cigaba da tafiya
Kumurci da yaga banda dukansu ba abinda akeyi yayi dauriya yace basu bane bayin ,Dukansu tsaya sukayi suna kallon Kumurci saboda dokar masarautar ce duk wanda yafi ka matsayi dole kabi umarninshi kuma duk abinda zaiyi ba wanda ya isa ya dakatar dashi saidai idan har akwai wanda yafika matsayi zai iya hanaka to
Kallon Kumurci suke da idanunsu masu sawa mutum ya shiga zullumi Kumurci da duk ya tsure yace Allah ya gafarce ku Kumurci yana Neman sassauci. Saminu ne ya iso don kusan duk yafi su matsayi ya kallesu yace lapya?cike da rusunawa ya fara mashi bayanin abinda ya faru wani kallo Saminu yayi masu wanda nan take suka bar wurin ya kalli Kumurci yace ka shiga dasu ciki kuma duk wanda ya tareka kace ni na baka umarni shiga dasu daga ciki sannan ya bar wurin.
Kallon su shaho yayi da yan matan da suka taho dasu da mazan,saitin Hurriya ya kalla yaga tanajan numfashi da kyar ta hade gwiwar ta da kanta,tunda aka tsaidasu ta kwanta Kumurci ba karamin dadi yaji ba lokacin da yaganta da hijab ya tabbata da ace ba hijab jikinta da yanzu wani ya shiga dakinshi da ita gashinta kuma da tuni an datse saidai cikin ikon Allah ta rufe duka jikinta harda kusan rabin fuskarta.
Kumurci kallonta yake saboda yasan akwai matsala a masarautar nan idan har Hurriya ta shige ta don ya lura bazata taba saukar da kanta kasa ba don haka yake tunanin hanya daya zai bi don tasamu barin masarautar batare da ansamu matsala ba shine yace baiwa ya samota kuma yaroki alfarmar ta zama Baiwa hakimi shine kawai mafita anma ta cigaba da haka baisan a hannun wazata mutu ba don princes da princesses din masarautar nan basu da imani ga kuma dayar matsalar don Kumurci yayi nadamar tahowa da Hurriya don yasan ba karamar wuya zatasha ba don ko yaran sarki kadai sun isheta don sun tsani wani yafisu kyau duk da daman masarautar kyawawa akafi kaiwa saidai ba wanda san dalili to zai iya rantsewa tunda ake kai kyawawan mata a masarautar baitaba ganin Mai kyaun wannan yarinyar ba don su kansu yaran mai martaba sai sun raina kansu.
Kallo daya zakayi mata kasan ta jigata ba karamar jigatuwa ba ma don wandon dake jikinta duk yayi datti fuskar ta kuma duk ta kumbura ga babu annuri kwata kwata saida fa annurin kyanta nan don sai salki takeyi Kumurci yace ki tashi ki shiga mota mu tafi yanzu bada hargagi yayi mata maganar ba don zuciyar shi ta dan karye kadan Kallonshi tayi da idanunta masu kyau da wani kaifi Kumurci ya daga mata kai tare da fatar kada tayi kafiya irin wadda tayi dazu.
A hankali take takawa amman zaka iya hango zallar mulki dake cikin tafiyar tata har ta shiga motar a hankali Kumurci girgiza kai yayi don ya hango kurar dake tafe da ita saidai Allah ya kyauta don aikin gama ya riga ya gama.
Bintu kam lokacin da ta koma layi cikin sa’a ba ba wanda ya lalubeta saboda hankalin kowa da ya koma kan Hurriya tanajin su karime dake gabanta cikin layi suna dariya suna cewa Allah ya kara sa’ade ce tace kinsan dadin da nikeji yadda ake bugun Hurriya karime tayi murmushi tace naki kika sani ni yarinya ta dade tana bani haushi shegiya ga isa ga iko sai kace wata shegiya sa’ade tace bata da mutunci Hurriya kinga cin mutunci da tayi ma mahaifina kuwa harda watsa mashi man awara akafa bayan tagama zazzageshi cikin mutane karime yo naji maganar tana yawo agari ki bari idan munje mu hade kai mu ci ubanta don ni ta dade tana bani haushi don kiga duk anguwar mu ace mazan ita kadai suke kallo to yanzu lokacin mune idan munje muyi maganin karuwa Mai ma maza jiki.
Bintu duk tanajinsu don harda kukan ta wurin da suka ce mata karuwa don tasan karya sukeyi Allah ya saka maki Hurriya inji Bintu ta fada cikin ranta.
Hurriya da ta koma wurin zamanta ta jinginar da kanta jikin window tana rufe idonta saidai kyarma kawai takeyi tana harhade hakoranta ga sanyi da ya isheta dankwalin da ta daura ta rufe gashinta dashi ta koma ta kwanta saidai sanyi ya matsa mata don bata daina jinshi ba ledar kayanta dake gabanta ta jawo saboda Asabe hada kyautar doguwar hijab tayi mata don lokacin har ta kawo zaure Asabe ta kwala mata kira a hankali asabe ta mika sabuwar hijab doguwa maroon tace Hurriya ko bazaki sanya ki fito ba ai nasan kina sallah to ki rinka sallah da ita inda so samu ne ki rinka fita da ita sai kuma ta tabe baki tace nasan yaudarar kaina nike ba inda zaki da ita tace Hurriya ki godema Allah don wallahi inasonki duk wanda yaji nayi kyauta sai ya kusa suma saboda mamaki kindai sanni da san kudin tsiya Hurriya batace mata komai ba har tagama maganar ta sai Hurriya ta mika mata ledar alamun ta sanya Asabe kam sauri ta dauko ta sanya Hurriya ta tafi ba godiya bare sallama.
Hijabin ta lalubo ta sanya ta dunkune kanta ciki a hankali bacci ya dauketa.
Sosai suka sha tafiya har suka iso Babbar masarautar Qamar bata sani ba don kowa ya fita a motar ya barta Kumurci ne ya kula da babu ita don har anfara kada kyayoyinsu Kumurci ya bude motar yazo inda take bacci da yake bai san sunanta ba don haka yace ke ki tashi mun iso shiru Hurriya tayi saida yayi mata magana kusan sau uku sannan ta bude idon wadanda sukayi mata nauyi Sosai har lokacin tana jin jikinta na kwankwatsa Kumurci yace ki fito munzo kuma kada kiyi ma mutane kafiya da rashin kunya don kece zaki sha wahala Hurriya da batajin karfin jikinta kwata kwata don ko yadda take numfashi zaka iya lura tashi tayi ta rungumo kayanta saidai tana tafiya biyu ta sake su Kumurci da yayi gaba yaji karar kayan da tasaki don haka ya juyo ya kalleta sannan ya daukar mata kayan suka fita duk da suna zuwa ana sallahr magriba don duhu har yafara Bayyana Amman bazaka iya gane cewa rana ce ko dare ba saboda haske da ya wadaci ko ina a babbar masarautar Qamar Masarautar kanta abun kallo ce girmanta gari guda ne tunda ga floor din dake kasan masarautar da ginin da akayi mutum zai gane cewar masarauta ce maiji da tsantsar dukiya kuma da karfin mulki .saidai Hurriya ba Abu daya wanda ya burgeta don kallo daya tayi ma komai wanda bata kara kallon wani Abu ba
Su Bintu da su karime kam Murna sukeyi kamar su ciji duwawunsu basu san masarautar Qamar, bawuri bane da ya kamata ace ya burgesu ba ko su kasance masu farin ciki Don masarauta ce wadda take cike da tsantsar zalinci da rashin imani.Kusan duk wadanda sukazo dasu sakin baki suke suna kallon ko ina.
Tasa keyarsu akayi ana bugunsu kamar tumaki suka shigo ciki inda ba abinda kake gani sai dagorawa dake tsaitsaye fuskar su hade kamar zasu je yakin basasa hannunsu daya narka narkan bulali Dayan kuma hannu dogayen bindigu kowane,Ba wanda bai firgita ba da ganin wadanan dogarawan don fuskar su babu alamun sassauci
Hurriya da da kyar take tafiya saboda zazzabin da take wani bakin dogari ne ya sakar mata bulala wadda saura kadan ta fadi da kyar ta cigaba da tafiya
Kumurci da yaga banda dukansu ba abinda akeyi yayi dauriya yace basu bane bayin ,Dukansu tsaya sukayi suna kallon Kumurci saboda dokar masarautar ce duk wanda yafi ka matsayi dole kabi umarninshi kuma duk abinda zaiyi ba wanda ya isa ya dakatar dashi saidai idan har akwai wanda yafika matsayi zai iya hanaka to
Kallon Kumurci suke da idanunsu masu sawa mutum ya shiga zullumi Kumurci da duk ya tsure yace Allah ya gafarce ku Kumurci yana Neman sassauci. Saminu ne ya iso don kusan duk yafi su matsayi ya kallesu yace lapya?cike da rusunawa ya fara mashi bayanin abinda ya faru wani kallo Saminu yayi masu wanda nan take suka bar wurin ya kalli Kumurci yace ka shiga dasu ciki kuma duk wanda ya tareka kace ni na baka umarni shiga dasu daga ciki sannan ya bar wurin.
Kallon su shaho yayi da yan matan da suka taho dasu da mazan,saitin Hurriya ya kalla yaga tanajan numfashi da kyar ta hade gwiwar ta da kanta,tunda aka tsaidasu ta kwanta Kumurci ba karamin dadi yaji ba lokacin da yaganta da hijab ya tabbata da ace ba hijab jikinta da yanzu wani ya shiga dakinshi da ita gashinta kuma da tuni an datse saidai cikin ikon Allah ta rufe duka jikinta harda kusan rabin fuskarta.