← Book details Masarautar Qamar Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 24

Sashe 16

Masarautar Qamar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

hada wanda mama rabi tayi da wanda tayi don abinci suna da matukar yawa mutum ashirin zasu iyacin abinci don different varieties of food ne a wurin

Bayan tagama sai ta nufi hanyar fita mama RaBI kamar tasan niyyarta don haka tace Hurriya kune zaku tsaya har su hakimi sugama cin abinci koda suna bukatar wani abu sai ku mika masu

Bata matsa ba kuma bata dawo ba Amman ga dukkan alamu maganar ta shigeta zubaida da mama rabi da wasu kuyangu guda ukku suka fara fitar da tray din abincin da drinks da wasu manya manya non alcoholic wines

Hurriya zuwa tayi ta dauki trays din wanda yake cike da wasu matsiyatan plate ta shiga parlon saida ba kowa a parlon it looks like Dukansu suna parlon gaba don haka Bata wani Bata lokacin ba ta shiga ba excuse ba sallama kallon mutanen dake zaune a tsakiyar parlon tayi duk twins ne kusan set uku masu matukar kama da juna.

Liya wadda ta daura kafafunta saman jikin Neela in an annoying way itace ta fara lura da Hurriya kallonta take from head to toe shiru tayi batace komai ba duka sauran hankalin su yana akan abinda sukeyi Neela hankalinta duka yana Akan wayarta sai Amrah da imran da suke playing ps 5game duka hankalisu yana a wurin game din

Liya kam satar kallon Hurriya kawai take wadda take jera abinda ta shigo dasu a dining kutt The girl is unparalleled beauty su zubaida duk sun dukar da kansu da kuyangin da suka shigo tare

Kallon kafafunta wanda suke bude tayi tana kallon sumarta da take bude fuskar nan a hade take kamar an aiko mata da sakon mutuwa tanayi tana cije lebe wanda ga dukkan alamu sararta ce Liya kasa janye idonta tayi daga kallon Hurriya don tunda take masarautar Qamar bata taba ganin halitta mai kyaun Hurriya ba saidai gabanta ne yayi mugun faduwa tunawa da tayi ana jita jitar cewar masu kyaun masarautar su mutuwa sukeyi don ko a ma’aikata indai matane to ba’a cika kawo marar sa kyaun hallita ba saidai tunda take bata taba ganin Mai kyaun da ta kama kafar Hurriya ba wane subira an dade acikin masarautar Qamar ana bama subira sarauniyar kyau Amman wannan yarinyar tayi ma subira fintinkau don indai za’a hada kyaun subira da Hurriya to subira zata iya samun 30percent ita kuma Hurriya 70percent

Babu abinda Allah ya rageta dashi don ita jikinta irin na models ne wanda turawa suke iya barnar da ko nawa ne garesu saboda su mallaki irin jikinta

Sauke ajiyar zuciya tayi farar daya tausayin yarinyar yana kamata don tana da kyaun da ba kowani namiji bane zai iya dauke ido akanta ba sai kuma babban kalubalen dake masarautar duk da jita jita ne Amman ta dade tana tunanin anya abun ba gaskiya bane don itama ta rasa ma’aikantata Sosai wanda suka shaku kuma ta saba dasu saidai duk idan hakan ta faru akwai abinda jakadiya take fada mata saidai tun tana yadda har tazo tana putting Question mark.

Imad ne ya shigo kallonsu yayi Dukansu sannan yace guys let’s eat dinner ku tafi kubar min part dina don duk kun cikamin part dina Ammar ne ya ajiye wayarshi wadda take hannunshi sannan yazo Daidai inda Imad yake ya dafa shi yace ya akayi ka kosa MU tafi kodai kodai sannan ya fashe da dariya Imad daure fuska yayi dagajin maganar Hurriya don yarinya ta bata mashi rai kuma ta rainashi shida ma’aikatan masarautar Qamar ke shakkar shi Amman yarinya yar Qarama tana Neman rainashi har sanyawa fa yayi a kira mashi ita kuma dagagan ya shanyata so yayi sai tayi awa goma tana jiranshi amman tayi tafiyarta idonshi idon Hurriya Amman sai yayi mata wukanci

Dariya ammar ya cigaba dayi yace kodai har ka folla ne? Naga yarinya is beautiful ya ida da maganar da wata irin dariya

Neela itama dariya tayi tazo saitin ammar tace who’s the girl dan dungurinta ammar yayi sannan yace magulmaciya yace ban fadi sannan yayi mata gwalo

Dariya Liya tayi sannan tazo saitin ammar itama tace who’s the girl bro please tell me kasan ba ajin kanmu dariya yayi sannan itama ya dungureta yace magulmata bazan fada ba

Dukansu tare suka jero sai yan kananun kannansu wadanda suke uwa daya uba daya masu bala’en kyau Amrah da hamdan kenan miskilai ne na karshe kuma yaran da basuyi ma kowa magana don duk da irin tsantsar kauna da take zagaye dasu wurin yayyayensu wadanda suke jinsu kamar kwai to idan ba yayyensu ba wanda sukeyi ma magana sun shaku da yayyansu Sosai saidai sarauta ajinisu take don wata sa’in miskilancin su harga yayyansu don tunda sukazo dinner a chamber imad wadda ta kasance duk sati sukeyinta saboda kowa yanada sashen shi to suna dadewa basu hadu ba sai Ammar ya kawo shawarar every Friday night suyi arranging cin abincin dare tare tohm haka sukeyi dukk satin duniya sai kuka suji damuwar junansu

Tare suka iso katon dining din wanda yake cike da abinci kala kala zubaida kansu a kasa suka farayi masu kirari Allah ya taimake ku Allah ya kara maku nasara sunata yi masu kirari

Duk acikinsu ba wanda ya amsa masu don ko kallon inda su zubaida suke basuyi ba

zama dukansu sukayi ta Liya ce ta juyo tace masu we will serve ourself

Hurriya tana tsaye tana kallonsu ita ba wanda tayi ma magana Liya dai na kula da ita su Imad hankalisu ma bai kai kan ma’aikatan ba bare suga Hurriya don su ma’aikatansu ko kallo basu ishesu ba.

Hurriya tsaye tayi tana kallon kowane acikinsu ba tare da ta dukar da kanta ba

Hamdan ne ya dago idanunshi daga kan iPad din dake rike a hannunshi cikin sa’a kam ya saukesu akan Hurriya da take tsaye fuskarta babu annuri kallonta yake Ko kyaftawa bayayi itama kallonshi take cikin idanu

Neela ce ta kalli Amrah tace ki ajiye iPad dinan muci abinci turo baki Amrah tayi sannan ta ajiye iPad din muryar hamdan ce ta doki dining din dasuke yace you alamar yana kiran wata Dukansu yayyanshi dagowa sukayi suna kallon wadda yake kira kasancewar shi ba mai yawan magana ba don sukansu hardly ne su ji maganar shi saboda miskilancin shi

Hurriya da take tsaye tasan da ita yake kallonta yayi sannan ya kara nunata da yatsa still banza tayi ta kyaleshi tana zuba mashi idanunta

Imad wanda shima hankalin shi nakan wayarshi ya dago ya kalleta saida ya kalleta tundaga farko har karshenta aranshi yace Lallai ma yarinyar nan waye zata burge tazo masu a haka kamar zata club saidai bai iya yaudarer zuciyar shi ba Amman yarinyar gaskiya tana da kyau toh kila shiyasa take raina ma mutane wayau amman bari zaiyi maganinta aiko nan take ya bata rai ya hade fuska yana kallonta

Ammar wanda shima kallonta yake bai ko kyaftawa saida ya tabbatar ya saisaita kanshi sannan ya kalli Imad da yake ta cin magani ya kwashe da dariya
Hamdan ahankali ya karayi mata magana yace please come and join us banza ta karayi dashi

Imad ne ya tashi ranshi bace Ammar yayi saurin rikeshi yana dannah dariyar shi

Amrah ce ta taso tazo saitin Huriya cikin muryarta ta yarinta tace kizo muci abinci tare don Allah tana pleading dinta da hannu in a cute way Hurriya kallon yarinyar tayi mai bala’en kyau amman kallo daya zakayi mata kasan akwai kadaici tattare da ita shiru Hurriya tayi tana kallon hamdan da amrah wanda shima ita yake kallo da alamar tazo tayi joining dinsu Neela ce ta kallesu ta bata fuska sannan tace what are you doing Amrah

Amrah bata fuska tayi haka zalika hamdan Liya ce ta taso tazo saitin Hurriya sannan tace please join the poor babys they love you

Hurriya daga mata kawai tayi ta zauna family dinner din

Zubaida kam kamar ta mutu saboda bakin ciki yarannan da basu tabayi mata magana ba don yaran Allah ya zuba masu mulki da sarauta basu kula kowa gashi yayyansu kamar su cinyesu haka sukejin su aransu idan sun soka tohm tohm yayyen sun soka idan sunki ka tohm suma sunki ka

Hamdan ne ya kalleta cikin mulki da sarauta don kusa da kujerar da yake tazauna ahankali yace mata you’re beautiful shiru wurin ya dauka kowa yana saka Abu aranshi Imad kam zuciyarshi banda bugawa ba abinda takeyi saboda tsanin bacin rai

Imad magana zaiyi Amrah ta rigashi ta hanyar dawowa saitin Hurriya tace ya sunanki please?hurriya kallonta tayi da idanunta masu kwarjini Amrah dafe zuciyar ta tayi ta hanyar cewa please stop looking at me like that way,you look intimidated .i know you’re more beautiful when you smile ok can you smile for me just once tana mata wink

Hamdan dariya yayi wadda ta fito tundaga zuciyar shi sakin baki su Ammar sukayi suna kallon kannansu

yare Hamdan yayi ma Hurriya ta hanyar cewa zaki bani diyarki idan kika haihu you’re beautiful but you’re lonely ta ko ina
gaban Hurriya ne ya shiga faduwa tana kallon hamdan da ya tsare ta da idanunshi yana jiran amsarta

Rabon da taji kalar yarenan har ta manta innallilahi wa’ina ilahi raji’un ta shiga furtawa cikin zuciyarta wadda take duka kamar ganga rabon da ta ambaci sunan Allah rayuwarta ta manta saidai acikin Sallah wadda batada tabbacin tana amsuwa ko bata amsuwa

Hamdan ya saki wani killer smile wanda idan ka kalleshi zaka iya cewa babba ne wanda dudu shekararshi sha biyu a duniya shida twin sister shi

Saidai Allah yayi mashi baiwa wadda ake kira wato smartness

Shiru duka wurin ya dauko suna kallon Hurriya da Hamdan murmushi Hamdan yayi yace mata you look like princess Layla Al-Khasheem she’s my role model because speech dinta yana matukar taimakona did you know her ?dan murmushi yayi sannan yace i know you will not know her saboda celebrity ce a duniya baki daya duk wanda ya kalli Hurriya alokacin zaisan a tsoroce take don sam takasa boye firgicin dake fuskarta salati take Sosai acikin ranta
Chapter 16 · 0% Book details