← Book details Masarautar Qamar Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 24

Sashe 19

Masarautar Qamar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hurriya bata da dadi ko kadan idan ka tabata zatayi masu salon azabar da ko a masarautar Qamar ba’a tabayi ma waninsu irinta ba because they almost killed her lamoniyar dake gareta is not an ordinary lamoniya ciwo ne mai hade da poison wanda yake babbar barazana ga rayuwarta all this while tasan Allah ke tsareta and nobody knows about her health condition don ko a masarautar Heral ciwonta is a secret duk wanda yasan da ciwonta sai yabar masarautar tare dayin nesa sosai da masarautar zatayi masu abinda idan akace gobe su kara bazasu kara ba tayi alkawarin sai sun biyata with bigger price Dukansu sai sunyi jinyar da tafi tata tayi wani evil smirk tare da rufe idonta masu kyau tana taune lebanta.
[12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar
A story about a mysterious palace

By Khadija (KMU)

25&26

Bintu kallom Hurriya kawai take with pure love Hurriya lumshe ido tayi tana yamutsa fuska alamar jikinta na damunta Bintu tace bari in kira maki baba hanne ta kara dubaki

Bintu aguje taje kitchen ta kira Baba hanne wadda take tuka tuwo ai tanajin ance Hurriya ta farfado ta saki muciyar ta rugo aguje sai dakinsu Bintu murmushi tayi tana biyota a baya

A kwance suka iske Hurriya tadan tada kanta da bango ta lumshe idanunta dogayen lashes dinta kwance sai kyalli suke sai pink lips dinta da take dan cijewa Inna hanne kara kallon Hurriya tayi don ba karya tanada kyau kallonta ta karayi ganin irin kwarjini da kuma tsantsar mulki da yake bayyane ajikinta dama saidai idan baka gani Amman kallo daya zakayi ma Hurriya kasan jini sarauta ce bude idonta Hurriya tayi aiko da sauri inna Hanne ta sadda kanta kasa duk tasha jinin jikinta ta kasa motsi Hurriya kallo daya tayi mata ta kauda kanta

Hurriya Bintu ta kalla tace Bintu ki samo man ruwan zafi inyi wanka da sauri Bintu tace to inna hanne ce tace kije kitchen kice nice na aiko ki a zuba maki ruwan zafi Bintu juyawa tayi ta fita domin amso ma Hurriya ruwan wanka

Inna Hanne kam kanta duke a kasa Hurriya batasan ma Allah yayi wata hallita a wurin ba har Bintu ta kawo mata ruwan a hankali ta sauko kafarta wadda tayi mata nauyi da sanyi

Bintu har tazo zata taimaka mata girgiza mata kai Hurriya tayi alamar bataso da kyar ta iya tashi ta fara tafiya a hankali Bintu ta shiga ta ajiye mata ruwan sannan ta bata brush da macline sai sabulun wanka

Saida tayi brush sannan ta mika ma Bintu brush din ita kuma ta shiga toilet domin yin wanka

Ta dade cikin toilette tana wanke jikinta saboda kyankyamin da takeji saida tayi kamar zataji ma kanta ciwo saboda yadda take dirzar jikin sannan ta dauraye jikinta ta fito tana mai jin matukar kyankyamin kayan da ta maida

Hurriya dakinsu ta shigo inda tayi sa’a Bintu da inna hanne basu nan don inna hanne ce tacema Bintu suje kitchen tare domin dafa ma Hurriya abinci dajin haka Bintu taita murna sannan tabi inna hanne kitchen din kallon Bintu tayi sannan tace mi Hurriya tafiso acikin abinci shiru Bintu tayi sannan ta girgiza ma inna hanne kai alamar batasani ba don bata taba ganin Hurriya na cin abi da farin ciki ba don kullum cikin dacin rai take cin abinci kamar dole

Inna hanne murmushi tayi ta debo dankali wanda bai kai goma ba sannan ta fere.

Hurriya kallon ko ina tayi da yayi datti cikin yanayin natsuwarta ta amso tsintsiya wurin uwale da murna uwale ta farayi mata ya jiki daga mata kai Hurriya kawai tayi tazo ta gyara dan wurin ta share wurin tass

Sannan ta cire kayan jikinta vaseline ta shafa ta bude ledar kayanta ta zaro jeans dark blue sai farar top mai shara shara saida ta sanya inner wears hade da vest sannan ta sanya rigar

Kwanciya tayi ta mike kafafunta ta lumshe idonta tunani take neman ta farayi wanda sam babu lisaafin tunani a rayuwarta bude idonta tayi sai kam ga giftawar su barira kallonsu tayi Dukansu tana karantar su

Inna hanne ce ta shigo itada Bintu inna hanne rike da yar karamar kula mai kyau Bintu kuma hannunta rike da ruwa da plate

Da sallama suka shigo kallo daya Hurriya tayi mata tagane ta don itace matar da ta fara bata ruwan zafi. acikin zuciyar ta take tambayar kanta mi takeyi anan Shiru tayi tana kallon matar sai sadda kai take kamar munafuka tana durkusa mata alhalin ranar farko ba haka tayi mata ba

Inna hanne ta zuba mata faten dankalin da tayi mata wanda yaji kayan miya ta mika mata Hurriya kallonta tayi ba tare da ta amsa ba don haka Bintu da sauri ta amsa tazo ta mika mata amsa Hurriya tayi sannan tace Bintu ta miko mata ledar kayanta ba musu Bintu ta miko mata ledar kayanta spoon ta dauka cikin kayanta saida ta daurayeshi sannan ta faraci lumshe ido tayi ta cigaba daci wanda alama ke nuni da tana enjoying abinci

Dukansu kallonta suke inna hanne kanta a kasa saida taci Sosai sannan ta ture plate din Bintu ta kalleta sannan tace kin koshi daga ma Bintu kai Alamar Eh ta koshi

Pure water inna hanne ta miko mata alamar ta ajiye tayi mata inna hanne ta ajiye mata dauka tayi ta fasa ta shanye

Inna hanne ta miko ma Hurriya magani ba tare da tayi musu ba ta amsa tayi chokali uku ta mika mata murmushi inna hanne tayi tana mai jin dadi ganin Hurriya har tayi acknowledging dinta

Kwanciya Hurriya tayi tareda lumshe idonta tana mai neman fadawa duniyar tunani tana tuna lokacin da idan ciwon ta ya tashi yadda iyayenta ke shiga tashin hankali sosai ganin tana Neman ta fada duniyar tunanin wanda bata cika son haka ba don haka ta tashi wayarta ta dauko wadda ta dade batayi amfani da ita ba ta kunna waka sannan lumshe ido tana bin wakar fire on fire by sam smith a haka har bacci ya dauketa

Inna hanne bayan tagama aikinta ta shigo ta iske Hurriya kwance tana Bacci kamar karamar yarinya duk da bacci take amman zaka iya gane yadda ta hade fuska murmushi tayi sannan tace rigimar Duniya

Hurriya bayan ta warke saida tayi kusan sati biyu bata fara zuwa aiki ba don so take sai sanyi ya gama fita daga jikinta tasss don a lamarinta batasan weakness ko kuma ace wani ya gane weak point dinta shiyasa saida ta tabattar da ta warke tasss sannan zata koma aiki

Bangaren kam inna hanne kam hidima takeyi mata babu kakautawa don abinci masu dadi kala kala takeyi ma Hurriya Ruwan wanka kam kullum ita take tafasa mata ta kai mata toilet hatta kayan Hurriya kwana uku sukeyi sai ta daukesu ta wanke mata

Duk hidimar da take ma Hurriya bata taba ce mata ta gode ba don kamar daman dolen ta ne ita kuma Inna hanne bata taba kallon Rashin kulawar da Hurriyyar take mata ba as wani abu ba

Tana addu’a kullum Allah ya bama Hurriya ikon yadda da ita duk da ta fahimci Hurriyar kamar bata yadda da kowa ba

A bangaren su Imad sun baza ido suna taso suga ko ta ina zata bullo don Liya ta bincika masu ance ta warke don Hamdan da Amrah kullum sai sunce zasu je Amman yan’uwan sunki barinsu saboda zai zama abun fadi a masarautar duk dasu ba ruwansu

Fitowar ta daga wanka kenan daga ita sai zani sai kuma doguwar hijab dai dai zata shiga ciki su kuma suna fitowa Dukansu kallonta sukeyi tundaga dogayen kafafunta har zuwa kyakyawar fuskarta wadda babu fara’a saidai zallah kyau da annurin dake fita kafe su tayi da idanunta masu masifar kyau saidai baka iya jure kallonsu saboda yadda suke imnating danger flames ne kawai ke fita daga idanun acikinsu ba wacce bataji shakkarta ba saboda wani kwarjini da ta karayi masu

Saida ta kare masu kallo tass sannan ta shiga daga ciki inna hanne da Bintu na ganin dawowarta suka tashi inna hanne ta kalli Hurriya sannan tace mi zakiyi yanzu cewa tayi sallah shimfida mata dadduma tayi sannan suka fita domin bata wurin saboda shiryawa don sun san bata sanya kaya wani na kallonta

Wata doguwar riga ta sanya mai kyau saidai tana kama da abaya yau kawai taji tanason dan decent dressing dankwali ta daura ma gashinta wanda yake ta kamshin mai na soulmate don Hurriya na yawan wanke gashinta sai ta jirashi ya bushe ya gama shan iska tukuna ta shafa mai ta sharce shi.

Hijab ta sanya tayi sallah hade da rama sallahr da ake binta don daman yaune karshe idan ta rama la’asar tohm sauran magriba da isha’i

Tana gama sallahr inna hanne ta shigo wadda dama dama yanzu Hurriya na kula ta saboda tana kula da ita duk wani motives nata tana kallo duk da tana nuna halin rashin damuwa gareta ganin batada wani motives shiyasa ta kyaleta ta shigo rayuwarta kuma she knew she’s too smart itadin fa sunanta Hurriya Faisait Hamood she’s her fathers daughter wanda zai iya cutar da ita yanzu ai sai yayi babban shiri beside ba wanda yasan kowacece ita saidai she have to be very cautious duk dama ita din she’s always cautious

Turarenta ta fesa mai saukin kudi sannan ta fito domin samun iska wayarta kirar burin yar garuwa sai a hannunta sai earpieces dake makale a kunnenta wakarta takeji wasba ce tazo inda take tana kuka tana sharbar majina kallo daya Hurriya tayi mata taganeta

wasba yar karamar yarinyar ta dukar da kanta tanata sharbar kuka Hurriya batace mata komai ba har ta gama kukanta
Chapter 19 · 0% Book details