← Book details Masarautar Qamar Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 24

Sashe 15

Masarautar Qamar Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Mama RaBI ta shigo kitchen din tare da zubaida dukansu bude baki sukayi da mamaki suna kallon Hurriya da tagama cin abincinta hankali kwance salati mama rabi ta farayi tana kallonta sannan tace waye ya baki izinin cin abincin nan kinsan abinci waye kuwa kallonta Hurriya tayi da idanunta masu haske ba tare da tace komai ba ta dauki ruwan da yake jere a saman tray din ta fita.

Mama RaBI kam ba’a tabayi mata irin abinda Hurriya tayi mata ba
Kallon zubaida tayi wadda har lokacin bakinta bude yake sannan tace wai ina aka samo wannan shegiyar yarinyar ne mama rabi kinga wani kallon banza datayi maki sannan ta juya ta tafi shiru mama rabi tayi sannan ta Sauke ajiyar zuciya tace lallai yaro baisan wuta ba sai ya taka sannan ta kyalkyace da dariya zubaida wata dariyar gefen baki tayi itama sannan suka bar wurin

Mama RaBI taji haushi sosai da hakimi bai basu fuska
Ko kara bai basu damar wani ya kaimashi bare munafunci da tsaegumi
Da wallahi sai tagaya ma Imad kaskantaciyar mai-aikin shi taci mashi abinci kwata tayi sannan tace ajuri zuwa rafi watarana tulu zai fashe

Hurriya tafiyar ta Tayi wanda gari har ya fara duhu magrib ta gabato saida tayi tafiya mai nisan gaske sannan tazo bangarensu ta shiga

Ta gaji sosai don ba abinda take bukata irin tayi wanka tayi bacci kallon bintu da take zaune tana hamma tayi wanda dama ga dukkan alamu Hurriya take jira

Wuri ta samu ta zauna Bintu ta kalleta tace sannu Hurriya kindawo ne kinci abinci ? Daga mata kai Hurriya tayi batace ma Bintu komai ba

Bintu kallonta tayi hamma tayi sannan tace saida safe daman jiran dawowar ki nike bari in tafi har ta juya tajiyo sautin muryar Hurriya daga bayanta tace kinci abinci da wata irin murna Bintu tajuyo tace naci a hankali Hurriya ta zaro naira dari biyu ta mika mata

Bintu amsa tayi tana kallon Hurriya domin jin karin bayani lumshe idonta Hurriya tayi sannan ta tsotsi bakinta saida ta dauki lokaci sannan ta bude idonta masu kyau ta zuba ma bintu su tace idan kina bukatar wani abu ki siya can kasan makoshin tace ki kula da kanki sannan ta kara rufe idonta kamar mai bacci

Bintu murmushi tayi tana kallon Hurriya da zallar kauna a idonta wadda idonta suke rufe dan tsalle Bintu tayi kamar karamar yarinya tace Ina kaunar ki Hurriya sannan ta juya ta tafi dakinsu

Saida Hurriya taji tafiyarta sannan ta mike ta nufi babban kitchen din da ake dafa ko wani irin abinci

Dubawa tayi ko zata ga matar jiya saidai akasin haka baba haule reza tagani don duk tafi kowa zama kusa da ita don haka ta nufi wurinta da bokitin baba haula reza kallo daya zakayi mata kasan cewar masifarfa ce ta ajin karshe

Hurriya bokoti ta ajiye ahankali sannan ta kalleta in a commanding tone tace ruwa zaki zuba min

Baba haule reza ta dago idonta a kankance ta fara surfa mata ashariya Hurriya bata janye idonta daga kallonta ba kuma batace mata kala ba

Har saida tagama kumfar bakinta kowa kallon baba haule reza yayi acikin kitchen din sannan kowa ya cigaba da hidimar shi don inda sabo ta saba

Hurriya saida ta tabattar da cewar baba haule tagama masifarta sannan ta zaro naira dari ta ajiye mata tana kulleta da idonta

Baba haule kam kamar an daure mata baki don dauke darin tayi a inda Hurriya ta ajiye tana saka kudin cikin skirt dinta

Bokitin ta janyo ta zuba ma Hurriya ruwan zafi masu yawan gaske ba tare da Hurriya tace kala ba taja bokitin ta nufi toilet ta gasa jikinta sosai da ruwan zafi.

[12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar
A story about a mysterious palace

By Khadija (KMU)

Page 21&22

Bata wani dauki lokaci sosai ba ta fito daga toilet din tana mai ya mutsa fuskarta don duk batajin dadi don kayan dake jikinta sune ta maida dalili kam da akwai zanen tatoo a bayanta bata kaunar ko wani dan mutum yaga tatoo din sam she’s not comfortable cikin masarautar Qamar don kwata kwata batada yancin dan adam kuma ita a rayuwarta ba abinda takeso irin yanci don haka ta tashi a rayuwarta tunda ta taso ba wanda ya taba depriving right dinta tanada ko wani irin freedom

Tana da matukar tsafta don kaya basu iya mata 24hrs ajikinta bare kuma ace kuma tayi wanka ta maimaita kaya saidai da ace ta fita da daurin zani wanda duk zanen dake bayyane a bayanta zai bayyana ga idon mutane gwara ta maida kayanta

Don haka da kayan ajikinta ta fito sannan tayi alwala ta shiga dakin

Cikin natsuwa ta Cire kayan jikinta kallon inner wears din da ta siya dazu dasu sabulun wanka da brush tayi har da turare mai sanyi kamshi batasan ana kasa haja ba sai dazu da safe inda har tazo wucewa taga haule reza ta kasa kaya masu kyau har ta wuce ta dawo haule reza ba abinda bata saidawa saida Hurriya ta bata kudi sosai wurin siyen abinda takeso don saida ta tabbatar duk abinda take bukata ta siya sannan ta nufi bangaren Imad

under wears ta sanya masu kyau sannan ta shirya cikin wata blue half gown da iyakarta gwiwar kafarta ta tsaya

doguwar hijab dinta ta sanya sannan ta kabbara sallah rama sallolinta tayi duka bayan tagama sallarh ta kishingida jikin katifar ta lumshe idonta ba bacci take ba Amman dai tayi lamo

Sunanta taji ana kira saidai ko motsawa batayi ba bare tayi tunanin bude idonta saida tayi mintuna Sosai kafin ta bude idonta ta zuba ma zubaida su da take tsaye wanda tagama kulewa don tunda tazo tasan ba bacci take ba Amman don bakin rainin wayau ace tanajinta tayi shiru ta kyaleta

Zubaida ta kalleta tace Lallai ma Hurriya shine zaki zo ki kwanta wakike tunanin kinbar ma aiki sai ki taso tunda ba bayi kika ajiye ba

Don ana bukatar ki a Aikin dare shiru Hurriya tayi batace kala ba don yaddda tayi kamar ma da dutse ake maganar

Hurriya magana fa nike inji zubaida shiru Hurriya tayi saita lumshe idonta

Zubaida kam iya jin haushi takai don cikin zuciyarta banda la’anar Hurriya ba abinda take saidai tayi mata wani irin mugun kwarjinin da bata iya maida mata magana

Gajiya tayi da tsayuwa zubaida taja tsoki tayi tafiyar ta

Hurriya kam shiru tayi don saida tayi kusan minti talatin kwance idonta kuma rufe kamar mai bacci
Tashi tayi ahankali cikin yanayin natsuwarta ta sanya takalminta ta fita

A hankali take tafiya wadda idan ka kalli yadda take tafiyar zaka dauka jinin sarauta ce dogayen kafafunta da suke bude sai salki suke sai tulin bakin sumarta wadda baka iya ganin jelar gashin saidai kwantaccen gashinta wanda ya fara tundaga goshinta farin wata ya haskata wanda ya taimaka wurin fito mata da tsantsar kyau na hallita duk wanda ya kalleta ya kara kallonta yasan mai kyau ce wato mai asalin kyau

Kallonta ake gabas da yamma kudu da arewa duk da kasancewar darene

Daidai saitin su barira da suke zaune a tabarma suna shan rake tazo zata wuce tanajin duka idanunsu dake yawo a kanta Amman ko a kwalar rigarta ta cigaba da tafiya tayi abunta

Muryar Hansa’u ce ta doki kunnenta wadda take cewa barira gafa mutuniyar

Barira shiru tayi tana kallon bayan Hurriya da dogayen kafafunta lashe baki tayi ta gyara zamanta batace komai ba

Wasila ce tace har yanzu bamu dauki fansar abinda tayi maki barira ba Amman na rantse bataci banza ba

Don ko yadda ta bata mana suna sai mun gyara mata zama sai na wulakanta yar matsiyaciyar can wulakanci mai muni sai kuma na hada mata tuggun da bazata iya warwareshi ba duka rayuwarta a masarautar nan sai na wulakantata wulakanci mafi wulakanci sannan in kaskantata kaskanci mafi kaskanci

Sannan tazo har gadon baccinki barira sai yadda kikayi da ita

Dukansu dariya suka sheke da ita tare dayin na’am da alkawarin da tayi kuma Dukansu sunce zasu tayata

Hurriya duk tanajin abinda suke cewa duk da kam tafiya takeyi kuma tayi masu nisa kallon sakarkaru marar sa aikinyi tayi masu ta cigaba da tafiyarta

Saida tayi tafiya mai nisan gaske kafin ta kawo chamber Imad

Ahankali ta shiga kitchen din wanda tana shiga kamar hadin baki duka ma’ikatan da suke aiki a kitchen din suka jiyo suka kalleta acikin su ba wanda bai bude baki ba yana kallonta ba tunda daga sama har kasa

Amman Hurriya shin ita ko ajikinta don idanun mutane basu daureta kwata kwata ko alama itadai Allah ya bata wani irin confindence wanda ba ko wani dan mutum yake da irinshi ba

Hurriya bata fasa tafiya ba don tsakiyar kitchen din tazo sannan sai taga tukunyar da ake shredded beef din don haka cikin natsuwa taje ta fara motsa tukunyar

Zubaida ce wadda ta kasa yin shiru cike da rashin kunya da wulakanci tace wai casu zaki ko coci Hurriya dagowa tayi ta zubama zubaida idonta masu kama da zaiba sannan ta tsotsi bakinta a hankali tace casu zamuje nida tsohuwarki da tsohonki idan mugama sheke aya sai mu tsaya ta coci muyi ibada

Tayi maganar hankali kwance tana kallon kowa acikinsu wanda fuskarsu take dauke da mamaki

Dukansu ba wanda bai saka wani abu acikin ranshi ba
Wasu kuma cewa suke daman tana magana?

Hurriya bayan ta tabbatar da shredded beef din yayi ta juyeshi a cikin food flask sannan ta dauki tukunya ba abinda ba’a nuna mata ba a bayani don haka tasan inda komai yake

Ruwa ta zuba a tukunya sannan ta shiga store ta debo basmati ta kunna gas ta daura tukunya hadaddiyar biryani tayi masu don tana abincin tana rera waka nike gani tanayi tana dan juya kugunta har ta gama don kamar abincin na tura mata memories don tana enjoying

Tazo ta kwaba pancake dinta ta soyashi mini sannan ta dauko chocolaté tayi dizzling dashi

Tana aikinta tana wakarta tanajin idanunsu a kanta Amman kamar babu kowa a wurin

Saida tagama yin komai ta dauko kula ta juye don abinci bai dauki wani lokaci ba tagama saboda karfin gas din dake da ci sosai

Hadawa tayi a tray don dakanta ta jera
Chapter 15 · 0% Book details