Sashe 9
Masarautar Mu Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da wannan ya samu ya lallashe ta. Amma shi kansa Yareeman tsoronsa ta ke ji, ta daku a hannun Ziyad koina na jikinta ciwo yake yi, ba ta gaya wa Yareema ba ne don kada ta kara daga masa hankali, ganin mawuyacin halin da yake ciki, amma kanta ciwo yake sosai sabida yadda Ziyad ya buga shi da bango.
Duk yadda ya so ya samu yadda yake so a daren yau, Saadatu ta ki, shi kuma yana so ne ya yi amfani da soyayya ya gusar da tsananin tsoron da ya dankare mata a zuciya, amma ta ki bada damar hakan.
Ya gaji da kokawa da ita, ya mike ya kunna fitilar dakin. Sai kuka ta ke mai ban tausayi. Ya ce,
For Gods sake Saadatu, ni ma rapist din ne?
Kukanta ya karu, ta ce, Yau daya dai ai sai ka kyale ni in ji da abin da ya dame ni, I cantdo it, gida nake son tafiya.
Yareema ya dawo ya zauna daidai kafafun ta, ya debi kafafun ya aza bisa cinyoyinsa, ai kuwa ta saki wata kara don azaba, wannan ya tabbatar masa akwai targade a yatsar kafarta.
Sosai ya ci gaba da jan yatsun kafarta a hankali har ya gane mai targaden. Ba tun yau ba ya iya gyaran targade, tana kuka tana komai haka ya gyara mata. Sai lokacin ya lura cewa, goshinta ma ya kumbura sosai. Hawaye suka ciko idonsa, ya ce,
Im sorry Saadatu, ni na jawo miki, one is responsible for the consequences of what he have done. Amma ke kam ba ki da laifi, tsarkakakkiya ce aka wanke aka bani cikin girma da daraja.
Dole gobe mu je asibiti a binciki lafiyarki, in ma yayi kika boye min ayi miki wankin ciki.
Ni ba inda za ni, kuma na gaya maka bai yi ba. Ta fada cikin kuka, ciwo har cikin kokon kanta.
Kawai ka sa ni a jirgi in tafi Maiduguri, daga can sai a dauke ni a filin jirgi, bazan iya kara kwanaki uku a gidan nan ba.
Ya kara sassauta murya mai nuna ya fi ta damuwa da abin da ya same ta.
Na rage kwanakin ki ba ni kwana biyu mu tafi tare, in ma kin ce kada mu sake zuwa garin Abuja ba za mu sake ba!.
Da wannan ya samu ya lallashe ta ta hakura ta yi barci.
Washegari da asubah a firgice ta tashi tana tambayarsa aljanin nan ya sake dawowa? Ya kankame ta yana gaya mata, Relax Saadatu ba fa aljani ba ne, abokina ne Dr. Ziyad wanda yake karbar abinci a wajenmu.
Mamaki da tsoro ya kashe Saade a kwance, ta kasa cewa komai, har duniya ta yi lalacewar haka? Aboki kuma makwabci mafi kusanci ya nemi raping matar amininsa? Wannan wace irin rayuwa ce? Tsoronta ya nunku fiye da tunanin ta na cewa Ziyad aljani ne.
Abuja ta kara fice mata a ka, ba abin da ta ke so irin ta bude ido ta ganta a dakin ta na unguwar Fulani Bilkisu.
Da gari ya waye ya yi wanka ya shirya, sannan ya rubuta resignationletterdaga NTNU. Da ya zo fita ne Saade ta ce, bai barinta ita kadai sai dai su tafi tare, tana da paper din karfe takwas.
Duk da ba ta karanta komai ba, a matsayinta na matar Dr. Sageer wadda ko a kwance suke ba ya rabo da tisa mata karatun fannin su na Pure and Applied Chemistry, ta san ba za ta kasa rubuta wannan takardar ta Inorganic Chemistry ba.
Shi ma ya fi so su tafi taren, don haka ya taimaka mata ta yi wanka.
Tana fitowa daga paper ta same shi a mota yana jiranta, dukkansu ba mai walwala, suka nufo gida. A daren ba ta bari sai gobe ba ta hade kayanta tsaf ta daure. Lamarinta har da na shagwaba kuma, ya yi - ya yi su je asibiti a duba ta ta ki.
Washegari ya shiga don ya gama cike sauran takardun ajiye aiki, ya ce mata insha Allahu ba zai wuce awanni biyu ba. Da kyar ya lallabata ta yarda bayan ya ba ta mukullan kofar kitchen da na kofar shigowa duka a hannunta.
******
Yareema Sageer bai dade da fita ba Ya Gumsu da kanwarta Aunty Daja wadda ke aure a nan Abuja tana auren wani ministan yada labarai, suka zo gidan cikin wata zabgegiyar mota. Ya Gumsu ta zo auren babbar yar Aunty Daja ne Abuja tun shekaranjiya. Tun da ta iso ta ke ce da Daja a kai ta gidan Yareema, Daja na ba ta hakuri kan ta bari a kai amarya ko me za su yi sai su yi, ita ma ba ta bayan hada zuria da yar annamimiya Fulanin Askirama.
Suna sauka daga mota suka karaso kofar shiga falo, suka soma yi mata wani irin mahaukacin bugu, wanda ya karasa razana razananniya Saade, wadda da ma ta ke zaune a darare tana jiran dawowar Yareema da trollies dinta uku a gabanta. Ta gama sa wa a ranta yau komai dadin bakinsa a Askira za ta kwana.
Sai kuma ga wannan mahaukacin bugun, ba abin da ta kawo a ranta sai Ziyad ne ya dawo. Idanunta suka raina fata, hawaye ya soma malalowa. Ba ta so ta yi ihu ma kada ya san tana cikin gidan, sai mazari jikinta yake daga tsayen da ta ke, wani fitsari ya kwace mata. Amma me?
Sai ta jiyo murya kamar ta mata suna kiran sunanta. Ba ta yi wa Ya Gumsu farin sanin da za ta dau muryarta ba, amma sai ta ji tana fadin,
Ni da gidan Dana aka bar ni ina buga kofa da mutuncina na Gumsun gari da komai?
Da sauri Saade ta karasa ta bude kofar da mukullan da dama suke rike a hannunta. Ta gane Ya Gumsu, dayar ce ba ta sani ba. Tana kokarin yi musu barka da zuwa ta ji wani lafiyayyen mari ya sauka a kan kuncinta, Aunty Daja ma ta kai mata nata.
Shegiya karuwa yar karuwa, tsintattun bisa titi. Idan ba Bilkisun ce ta haifa min Yareema ba, ba kuma ita ta ajiye ki a gidan nan ba, to sawunki a likkafa ki kama hanyar gidan ubanki, tunda an ce kina da shi.
Idan na ganki a masarautar Askira sai na sa an nakasta ki yadda ba Yareema ba babu wani namiji da zai kwashe ki. Fice mana a gida ki san inda dare ya yi miki kafin in sassaba miki kamanni.
Ta hankado ta waje, Daja kuma ta dauki hijab dinta ta jefo mata suka dinga hankada ta har kofar fita gidan, bayan Daja ta kara zazzabga mata mari. Farar fuskar nan ta yi jawur tayi kitumur kamar gauta. Marukan da ta sha sun kai goma. Yatsunsu ya kwanta lambam a kan farar fatar fuskar Saade.
Kuka ma wani lokacin rahma ne ga dan Adam, a lokacin da zuciyarsa ta rasa abin yi. To Saade ta kasa ko da fidda hawaye, tana nadamar yarda da aure da soyayyar Yareema Sageer alhalin tana da masaniya kan cewa, mahaifiyarsa ba ta kaunar tata kamar ajalinta.
Ya yi amfani da dukkan dabarunsa na wayayyen Da namiji ya sanya soyayyarsa a zuciyarta, ya ribace ta ya kassara zuciyarta. Yau mahaifiyarsa ta yi mata wulakancin da ko ita mayya ce dole ta hakura da Yareema Sageer sai a wannan lokacin ne ta ji hawaye masu dumi sun zubo mata.
Ya ya za ta yi ta je Askira? Duk da Ya Gumsu ta ce kada ta je din, amma ba ta da inda ya fi can, tunda uwarta tana can, za ta bar masarautar Askira ne only ranar da babu Fulani a can ko ranar da ita ma Askirama ya kore ta.
Ko kudin mota babu a tare da ita, daga ita sai hijabin sallarta. Amma ta tabbata za ta iya kai kanta Askira, idan ta ganta a Maiduguri. Ko da da rarrafe da jan ciki ne.
Tana wannan tunanin tana kuka, ba ta san cewa ta hau bisa titi ba ta bar tafiya a gefen hanya.
Daidai lokacin da shi kuma ya fito daga NTNU yana sharara gudu don tafiya gida, ya hango wata mace na tafiya tsakiyar titi kamar bata ji ba ta gani, motoci na ta kauce mata, wasu su bi ta da zagi, wasu su kunna mata fitilar zagi, amma ba ta ko san suna yi ba.
Ya sakar mata kakkarfan horn don ta sha gabansa, ta juya a firgice sai ya ga Saade. A hankali ya sauka a gefen titi, ya fito da sauri ya bi bayanta yana kiran sunanta.
Saadatu Hashim, Saadatu Askira ina za ki je haka?
Muryar Said abokinta, Saidu-Saidunta. Yau da shi ta aura wa zai yi mata wannan wulakancin da cin zarafin? Wani hawayen ya sake zubo mata, ta sa fuska cikin hijabinta tana kuka.
Said ya hau waiwaye cikin tsoro. Har zai ce ta shiga motarsa ya kai ta inda za ta je ya tuna gargadin Yareema Sageer.
Kada ka kara daukar matata a motarka ko da da niyyar taimako ne.
Said ya naushi hannun damansa da hannun hagu, ga shi kuma ba zai iya tafiya ya barta a kan titi ba, ko da kuwa supreme court Dr. Sageer Askira zai kai shi a dalilin hakan. Da ganin halin da ta ke ciki tana tsananin bukatar taimako, ba zai barta ta ragaita a babban birni irin Abuja ba.
Wane irin taimako zan iya ba ki?
Said ya fada cikin tsoro, yana tsaye nesa-nesa da Saade yana kuma waiwayawa dama da hauni kada Dr. Sageer ya zo ya same shi.
Kudin mota.
Ba ta san lokacin da ta furta ba.
Ina za ki je? Ya tambaya da sauri.
A hankali ta ce, Garinmu Askira.
In aka sauke ki a Maiduguri za ki iya zuwa har can Askiran?
Da sauri ta gyada kai.
Said ya ce, Zan sa ki a tasi zuwa airport, sai in bi bayanku, sai mu je in yankar miki ticket din Maiduguri.
Saade ta hau godiya, tana yi masa addua. Ji ta ke kamar ma ga ta ga Fulani a gabanta.
Duk yadda ya so ya samu yadda yake so a daren yau, Saadatu ta ki, shi kuma yana so ne ya yi amfani da soyayya ya gusar da tsananin tsoron da ya dankare mata a zuciya, amma ta ki bada damar hakan.
Ya gaji da kokawa da ita, ya mike ya kunna fitilar dakin. Sai kuka ta ke mai ban tausayi. Ya ce,
For Gods sake Saadatu, ni ma rapist din ne?
Kukanta ya karu, ta ce, Yau daya dai ai sai ka kyale ni in ji da abin da ya dame ni, I cantdo it, gida nake son tafiya.
Yareema ya dawo ya zauna daidai kafafun ta, ya debi kafafun ya aza bisa cinyoyinsa, ai kuwa ta saki wata kara don azaba, wannan ya tabbatar masa akwai targade a yatsar kafarta.
Sosai ya ci gaba da jan yatsun kafarta a hankali har ya gane mai targaden. Ba tun yau ba ya iya gyaran targade, tana kuka tana komai haka ya gyara mata. Sai lokacin ya lura cewa, goshinta ma ya kumbura sosai. Hawaye suka ciko idonsa, ya ce,
Im sorry Saadatu, ni na jawo miki, one is responsible for the consequences of what he have done. Amma ke kam ba ki da laifi, tsarkakakkiya ce aka wanke aka bani cikin girma da daraja.
Dole gobe mu je asibiti a binciki lafiyarki, in ma yayi kika boye min ayi miki wankin ciki.
Ni ba inda za ni, kuma na gaya maka bai yi ba. Ta fada cikin kuka, ciwo har cikin kokon kanta.
Kawai ka sa ni a jirgi in tafi Maiduguri, daga can sai a dauke ni a filin jirgi, bazan iya kara kwanaki uku a gidan nan ba.
Ya kara sassauta murya mai nuna ya fi ta damuwa da abin da ya same ta.
Na rage kwanakin ki ba ni kwana biyu mu tafi tare, in ma kin ce kada mu sake zuwa garin Abuja ba za mu sake ba!.
Da wannan ya samu ya lallashe ta ta hakura ta yi barci.
Washegari da asubah a firgice ta tashi tana tambayarsa aljanin nan ya sake dawowa? Ya kankame ta yana gaya mata, Relax Saadatu ba fa aljani ba ne, abokina ne Dr. Ziyad wanda yake karbar abinci a wajenmu.
Mamaki da tsoro ya kashe Saade a kwance, ta kasa cewa komai, har duniya ta yi lalacewar haka? Aboki kuma makwabci mafi kusanci ya nemi raping matar amininsa? Wannan wace irin rayuwa ce? Tsoronta ya nunku fiye da tunanin ta na cewa Ziyad aljani ne.
Abuja ta kara fice mata a ka, ba abin da ta ke so irin ta bude ido ta ganta a dakin ta na unguwar Fulani Bilkisu.
Da gari ya waye ya yi wanka ya shirya, sannan ya rubuta resignationletterdaga NTNU. Da ya zo fita ne Saade ta ce, bai barinta ita kadai sai dai su tafi tare, tana da paper din karfe takwas.
Duk da ba ta karanta komai ba, a matsayinta na matar Dr. Sageer wadda ko a kwance suke ba ya rabo da tisa mata karatun fannin su na Pure and Applied Chemistry, ta san ba za ta kasa rubuta wannan takardar ta Inorganic Chemistry ba.
Shi ma ya fi so su tafi taren, don haka ya taimaka mata ta yi wanka.
Tana fitowa daga paper ta same shi a mota yana jiranta, dukkansu ba mai walwala, suka nufo gida. A daren ba ta bari sai gobe ba ta hade kayanta tsaf ta daure. Lamarinta har da na shagwaba kuma, ya yi - ya yi su je asibiti a duba ta ta ki.
Washegari ya shiga don ya gama cike sauran takardun ajiye aiki, ya ce mata insha Allahu ba zai wuce awanni biyu ba. Da kyar ya lallabata ta yarda bayan ya ba ta mukullan kofar kitchen da na kofar shigowa duka a hannunta.
******
Yareema Sageer bai dade da fita ba Ya Gumsu da kanwarta Aunty Daja wadda ke aure a nan Abuja tana auren wani ministan yada labarai, suka zo gidan cikin wata zabgegiyar mota. Ya Gumsu ta zo auren babbar yar Aunty Daja ne Abuja tun shekaranjiya. Tun da ta iso ta ke ce da Daja a kai ta gidan Yareema, Daja na ba ta hakuri kan ta bari a kai amarya ko me za su yi sai su yi, ita ma ba ta bayan hada zuria da yar annamimiya Fulanin Askirama.
Suna sauka daga mota suka karaso kofar shiga falo, suka soma yi mata wani irin mahaukacin bugu, wanda ya karasa razana razananniya Saade, wadda da ma ta ke zaune a darare tana jiran dawowar Yareema da trollies dinta uku a gabanta. Ta gama sa wa a ranta yau komai dadin bakinsa a Askira za ta kwana.
Sai kuma ga wannan mahaukacin bugun, ba abin da ta kawo a ranta sai Ziyad ne ya dawo. Idanunta suka raina fata, hawaye ya soma malalowa. Ba ta so ta yi ihu ma kada ya san tana cikin gidan, sai mazari jikinta yake daga tsayen da ta ke, wani fitsari ya kwace mata. Amma me?
Sai ta jiyo murya kamar ta mata suna kiran sunanta. Ba ta yi wa Ya Gumsu farin sanin da za ta dau muryarta ba, amma sai ta ji tana fadin,
Ni da gidan Dana aka bar ni ina buga kofa da mutuncina na Gumsun gari da komai?
Da sauri Saade ta karasa ta bude kofar da mukullan da dama suke rike a hannunta. Ta gane Ya Gumsu, dayar ce ba ta sani ba. Tana kokarin yi musu barka da zuwa ta ji wani lafiyayyen mari ya sauka a kan kuncinta, Aunty Daja ma ta kai mata nata.
Shegiya karuwa yar karuwa, tsintattun bisa titi. Idan ba Bilkisun ce ta haifa min Yareema ba, ba kuma ita ta ajiye ki a gidan nan ba, to sawunki a likkafa ki kama hanyar gidan ubanki, tunda an ce kina da shi.
Idan na ganki a masarautar Askira sai na sa an nakasta ki yadda ba Yareema ba babu wani namiji da zai kwashe ki. Fice mana a gida ki san inda dare ya yi miki kafin in sassaba miki kamanni.
Ta hankado ta waje, Daja kuma ta dauki hijab dinta ta jefo mata suka dinga hankada ta har kofar fita gidan, bayan Daja ta kara zazzabga mata mari. Farar fuskar nan ta yi jawur tayi kitumur kamar gauta. Marukan da ta sha sun kai goma. Yatsunsu ya kwanta lambam a kan farar fatar fuskar Saade.
Kuka ma wani lokacin rahma ne ga dan Adam, a lokacin da zuciyarsa ta rasa abin yi. To Saade ta kasa ko da fidda hawaye, tana nadamar yarda da aure da soyayyar Yareema Sageer alhalin tana da masaniya kan cewa, mahaifiyarsa ba ta kaunar tata kamar ajalinta.
Ya yi amfani da dukkan dabarunsa na wayayyen Da namiji ya sanya soyayyarsa a zuciyarta, ya ribace ta ya kassara zuciyarta. Yau mahaifiyarsa ta yi mata wulakancin da ko ita mayya ce dole ta hakura da Yareema Sageer sai a wannan lokacin ne ta ji hawaye masu dumi sun zubo mata.
Ya ya za ta yi ta je Askira? Duk da Ya Gumsu ta ce kada ta je din, amma ba ta da inda ya fi can, tunda uwarta tana can, za ta bar masarautar Askira ne only ranar da babu Fulani a can ko ranar da ita ma Askirama ya kore ta.
Ko kudin mota babu a tare da ita, daga ita sai hijabin sallarta. Amma ta tabbata za ta iya kai kanta Askira, idan ta ganta a Maiduguri. Ko da da rarrafe da jan ciki ne.
Tana wannan tunanin tana kuka, ba ta san cewa ta hau bisa titi ba ta bar tafiya a gefen hanya.
Daidai lokacin da shi kuma ya fito daga NTNU yana sharara gudu don tafiya gida, ya hango wata mace na tafiya tsakiyar titi kamar bata ji ba ta gani, motoci na ta kauce mata, wasu su bi ta da zagi, wasu su kunna mata fitilar zagi, amma ba ta ko san suna yi ba.
Ya sakar mata kakkarfan horn don ta sha gabansa, ta juya a firgice sai ya ga Saade. A hankali ya sauka a gefen titi, ya fito da sauri ya bi bayanta yana kiran sunanta.
Saadatu Hashim, Saadatu Askira ina za ki je haka?
Muryar Said abokinta, Saidu-Saidunta. Yau da shi ta aura wa zai yi mata wannan wulakancin da cin zarafin? Wani hawayen ya sake zubo mata, ta sa fuska cikin hijabinta tana kuka.
Said ya hau waiwaye cikin tsoro. Har zai ce ta shiga motarsa ya kai ta inda za ta je ya tuna gargadin Yareema Sageer.
Kada ka kara daukar matata a motarka ko da da niyyar taimako ne.
Said ya naushi hannun damansa da hannun hagu, ga shi kuma ba zai iya tafiya ya barta a kan titi ba, ko da kuwa supreme court Dr. Sageer Askira zai kai shi a dalilin hakan. Da ganin halin da ta ke ciki tana tsananin bukatar taimako, ba zai barta ta ragaita a babban birni irin Abuja ba.
Wane irin taimako zan iya ba ki?
Said ya fada cikin tsoro, yana tsaye nesa-nesa da Saade yana kuma waiwayawa dama da hauni kada Dr. Sageer ya zo ya same shi.
Kudin mota.
Ba ta san lokacin da ta furta ba.
Ina za ki je? Ya tambaya da sauri.
A hankali ta ce, Garinmu Askira.
In aka sauke ki a Maiduguri za ki iya zuwa har can Askiran?
Da sauri ta gyada kai.
Said ya ce, Zan sa ki a tasi zuwa airport, sai in bi bayanku, sai mu je in yankar miki ticket din Maiduguri.
Saade ta hau godiya, tana yi masa addua. Ji ta ke kamar ma ga ta ga Fulani a gabanta.