Sashe 15
Masarautar Mu Part 4 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Kowannensu da kalar kulawar da yake nuna mata a falon, duk suka yi mata sannu da jiki.
Awaisu ya yi sallama ya shigo, ya duba Ya Gumsu da jiki sannan ya dubi Yareema da ke gefe kusa da Yaa Maira yana hagunta Saade na damanta (babbar Ya, UWA). Tana ta tsokanar su;
Princess Saa Allah ya sa ki haifo min mai kama da ni ba mai irin hancin Yareema ba (pointed noise), kin san in hanci ya cika tsayi muni yake komawa.
Ahmad ya ce, Kai Yaa Maira! A dinga yi ana tsoron Allah, ko makaho ya shafa ya san Yaya Yareema ya fi ki kyau nesa ba kusa ba.
Awaisu ya katse hirar tasu da cewa, Yareema bakinka na Neitherland sun iso airport din Maiduguri, zan je in taho da su. Gidanka zan sauke su ko guest house din Maimartaba?
Yareema ya harare shi, ya ce, Awaisu! Kana shiga lokacina fa, this is family time, ka je ka ji da customers dinka kai kadai. Duk inda ka ga ya dace, ka kai su.
Family ba za su ji dadi ba sai da kudi. A nemi kudi a bai wa family Malam, ina zan sauke su?
Gabadaya aka yi dariya ban da Yareema da Saade wadda ke satar kallon Yareema ta kasan idonta, tana mai alhinin muguwar ramar da ya yi cikin sati guda kacal. Duk da haka kyawunsa da kwarjininsa suna nan, sai ma abin da ya karu.
Sai lokacin Awaisu ya lura da Saade a falon tana daga gefen Yaa Maira, ya ce,
Aah! Madame, are you here? Dole idanun Yareema su rufe, ga masoyiya a kusa me zaa yi da kudi? Don Allah ki yi masa magana ya gaya min inda zan kai bakin turawanshi.
Saade ta yi dan murmushi ba ta ce komai ba, sai ma kara kasa da ta yi da kanta, gabadaya ta takura domin duk motsin da ta yi sai ta ji kaifafan idanun Yareema a kanta. Maganar Turawa da Awaisu ya yi ita ta sa Yaa Maira tunawa da Aisha-Sultana.
Da sauri ta ce, Yareema, ina Sultana? Ban ganta ta zo duba Ya Gumsu a Abuja ba?
Ai kuwa duk suka tattaro hankalinsu a kanshi, sai yanzu duk suka tuna ba su ganta din ba, including Saade ta dau ido ta dora masa, ita dai ta san sun yi tafiya tare, kuma ya dawo shi kadai bai kara yin zancenta ba.
Yareema ya dubi Yayar sa Yaa Maira sannan sauran kannensa maza da mata, sannan matar sa Saadatu da aminin sa Awaisu, ya ce,
Dukkanku ba bare a nan. Ba wanda zan boye wa sirrin gidana, muddin wanda ya dace ku ji ne. Aisha-Sultana (Rose) mun rabu. Na maida ita kasarsu.
Gabadaya suka sa salati domin babban zunubi ne saki a masarautar, tun daga iyaye da kakanni.
A kan wane dalili? Askirama ya sani? In ji Yaa Maira.
Yareema ya yi ajiyar zuciya, calmly ya shiga ba su labarin halin da yake ciki da Sultana tun komawarsu Abuja da ta sarki shan giya ta kuma cire mahaifa ba da izininsa ba. Ya ce,
Na yi ta hakuri ne da shan giyarta saboda nobody is perfect. Dukkanmu masu sabo ne in one way or the other. Sabida ni ma kaina din Im not perfect either. Amma sallah fa? Ba zan iya jure rayuwar aure da wadda ba ta sallah ba, sabida yayana da lahira ta.
Ya ci gaba da gaya musu yadda Askirama da kansa ya zo har gidansu ya same ta drunkard, ya ce,
bai ce in sake ta ba, amma bacin ran da na gani cikin idanunsa da gaisuwata da ya daina amsawa ya sa na ga duk son da nake mata gara in hakura da ita. (Ya boye musu abu guda daya, cewa ba zai iya adalci tsakanin kowacce mace da Saadatu ba, don ya sirranta soyayyar da yake wa matarsa ga yan uwansa, wanda hakan shi ya kamata ga duk namijin da ya san ciwon kansa).
Yaa Maira ta fahimce shi, amma sai ta ce, Wani hanzari ba gudu ba, Sultana ba ta ce ta yi RIDDA ba, sakin da ka yi mata saboda shan giyarta zai sa ta kullaci musulmi, ta ga cewa, tukuicin soyayyarta gare ka kenan, ta baro kowa nata da addininta ta biyo ka a karshe ga abin da ka saka mata da shi.
Ban sake ta saboda giya kadai ba. Na gaya miki ta karbi musulunci, amma ba ta sallah, mene ne marabarta da addininta na baya? Addinin ma da babu shi sam domin kuwa ba kirista ba ce, bayahudiyya ce (Jew). To cut it short, na yi nadamar aurenta tun farko, ban taba zaton Alanguburo zai amince ba, amma tashi guda ina fada bai turza ba, sai ya amince.
Had I know akwai Saade, kamar yadda ya ce tun farko ita ya so na aura ba zan taba yin wani aure ba.
Saade ba ta san lokacin da ta mike ta yi kofar fita ba, inda ta baro Fanna, kunya kamar ta yi ya ya. Tana ji Yaa Maira na fadin, Ka kore ta ka ji dadi. Saadatu dawo kin ji, yanzu zan sa Awaisu ya tattara shi su tai su ba mu wuri.
Ina! Saade ta kai kofa. Cewa ta ke, Yaa Maira zan dawo ne, idan na kara jin sauki.
Yareema ya daga murya yadda za ta jiyo shi ya ce,
In zo zance anjima bayan isha?
Ai saade kadan ya rage ta zura da gudu, suka dinga yi mata dariya.
Tana komawa unguwar su ta tadda Fulani ta dafa mata lafiyayyen faten acca da ya ji ganyen alayyahu da kabewa, ta zuba a faranti tana firfitawa da kanta tana jiran shigowarsu. Tana shigowa ta nufe ta da sauri.
Allah Sarki UWA! Saade ta fada a ranta, ta karbi cokali tana shan faten Fulani na tambayarta jikin Ya Gumsu, ta ce, ita ma tana jira Askirama ya shigo gida ne su shiga tare su dubo ta.
Saade ta tambayi Fulani, Ya ya aka kare ne da zancen auren Hanne?
Ta ce, An kai zancen kotun musulunci an yi mata gaiba, mun rabu a kan cikin watannin in ta gama iddah za ta dawo nan gabana, yaron a kai wa iyayen mijin. Plan dina akan ta shi ne a kai ta El-Kanemi, ta samu kwalin kammala sakandire sai a sama mata UNIMAID. Ta zauna hostel in sun yi hutu ta zo nan wajena ta yi hutun, har Allah ya ba ta mijin aure.
Saade ta gode wa Fulani, godiya maras adadi, tsarin da ta yi a kan rayuwar Hanne ya yi mata.
Ta ce, Su Raheema ko waya?
Ta ce, Kusan kullum muna magana da Maman, Raheema ta koma makaranta (university of Heartfordshire) wannan watan za ta kammala daga nan ku sha biki. Zan tambayi Maman lambarta na UK tunda yanzu akwai waya a hannunki.
Ta kyabe baki ta ce, Ni da na ji zafin maruka ina na tuna da wata waya?
(Tana nufin marin da su Ya Gumsu suka yi mata).
Fulani ta ce, Mari?
Nan ta gaya mata duk yadda aka yi, amma ba ta manta rokon da Yareema ya yi mata ba na ta boye zancen Dr. Ziyad ga iyayen su, it will create a serious problem idan suka ji, tunda dai mun bar NTNU din gabadaya shi ke nan. In ji yareema Sageer.
Sai dai tana tantama idan hukuncin da Yareema ya yanke musu is geniune, da gaske Abuja ta fice mata a ka, shi ma kuma Yareema haka, Dr. Ziyad yayi shattering zuciyar sa into pieces ya karya masa zuciya, ita kuma ya jefa tsoron rayuwar Abuja mai tsanani a tata zuciyar.
To amma makomar karatunta ta ke hangowa, shekaru ukun da ta kwashe cikin wahala da fadi-tashi sun tashi a banza ke nan? Above all aka ce sabo turken wawa. Ta saba da NTNU. Babu wata jamia da za ta bi bayan Nigerian Turkish Nile University a wurinta.
Fulani da ta ji duk abin da ya faru tsakanin Saade da su Ya Gumsu, sai ta jinjina kudirar Ubangiji. Ya Gumsu mai ja da ikon Allah dare daya yau gata ta zama sai dai a kwantar a tayar. Shin wannan bai ishi dan Adam ishara ba ya yarda cewa shi ba a bakin komai yake ba? Duk mulkinsa da izzarsa bai wuce talalar Ubangiji ba a duk lokacin da ya so? Bai isa ya sa, bai sa ya hana abinda Ubangiji ya hukunta ba?
Awaisu ya yi sallama ya shigo, ya duba Ya Gumsu da jiki sannan ya dubi Yareema da ke gefe kusa da Yaa Maira yana hagunta Saade na damanta (babbar Ya, UWA). Tana ta tsokanar su;
Princess Saa Allah ya sa ki haifo min mai kama da ni ba mai irin hancin Yareema ba (pointed noise), kin san in hanci ya cika tsayi muni yake komawa.
Ahmad ya ce, Kai Yaa Maira! A dinga yi ana tsoron Allah, ko makaho ya shafa ya san Yaya Yareema ya fi ki kyau nesa ba kusa ba.
Awaisu ya katse hirar tasu da cewa, Yareema bakinka na Neitherland sun iso airport din Maiduguri, zan je in taho da su. Gidanka zan sauke su ko guest house din Maimartaba?
Yareema ya harare shi, ya ce, Awaisu! Kana shiga lokacina fa, this is family time, ka je ka ji da customers dinka kai kadai. Duk inda ka ga ya dace, ka kai su.
Family ba za su ji dadi ba sai da kudi. A nemi kudi a bai wa family Malam, ina zan sauke su?
Gabadaya aka yi dariya ban da Yareema da Saade wadda ke satar kallon Yareema ta kasan idonta, tana mai alhinin muguwar ramar da ya yi cikin sati guda kacal. Duk da haka kyawunsa da kwarjininsa suna nan, sai ma abin da ya karu.
Sai lokacin Awaisu ya lura da Saade a falon tana daga gefen Yaa Maira, ya ce,
Aah! Madame, are you here? Dole idanun Yareema su rufe, ga masoyiya a kusa me zaa yi da kudi? Don Allah ki yi masa magana ya gaya min inda zan kai bakin turawanshi.
Saade ta yi dan murmushi ba ta ce komai ba, sai ma kara kasa da ta yi da kanta, gabadaya ta takura domin duk motsin da ta yi sai ta ji kaifafan idanun Yareema a kanta. Maganar Turawa da Awaisu ya yi ita ta sa Yaa Maira tunawa da Aisha-Sultana.
Da sauri ta ce, Yareema, ina Sultana? Ban ganta ta zo duba Ya Gumsu a Abuja ba?
Ai kuwa duk suka tattaro hankalinsu a kanshi, sai yanzu duk suka tuna ba su ganta din ba, including Saade ta dau ido ta dora masa, ita dai ta san sun yi tafiya tare, kuma ya dawo shi kadai bai kara yin zancenta ba.
Yareema ya dubi Yayar sa Yaa Maira sannan sauran kannensa maza da mata, sannan matar sa Saadatu da aminin sa Awaisu, ya ce,
Dukkanku ba bare a nan. Ba wanda zan boye wa sirrin gidana, muddin wanda ya dace ku ji ne. Aisha-Sultana (Rose) mun rabu. Na maida ita kasarsu.
Gabadaya suka sa salati domin babban zunubi ne saki a masarautar, tun daga iyaye da kakanni.
A kan wane dalili? Askirama ya sani? In ji Yaa Maira.
Yareema ya yi ajiyar zuciya, calmly ya shiga ba su labarin halin da yake ciki da Sultana tun komawarsu Abuja da ta sarki shan giya ta kuma cire mahaifa ba da izininsa ba. Ya ce,
Na yi ta hakuri ne da shan giyarta saboda nobody is perfect. Dukkanmu masu sabo ne in one way or the other. Sabida ni ma kaina din Im not perfect either. Amma sallah fa? Ba zan iya jure rayuwar aure da wadda ba ta sallah ba, sabida yayana da lahira ta.
Ya ci gaba da gaya musu yadda Askirama da kansa ya zo har gidansu ya same ta drunkard, ya ce,
bai ce in sake ta ba, amma bacin ran da na gani cikin idanunsa da gaisuwata da ya daina amsawa ya sa na ga duk son da nake mata gara in hakura da ita. (Ya boye musu abu guda daya, cewa ba zai iya adalci tsakanin kowacce mace da Saadatu ba, don ya sirranta soyayyar da yake wa matarsa ga yan uwansa, wanda hakan shi ya kamata ga duk namijin da ya san ciwon kansa).
Yaa Maira ta fahimce shi, amma sai ta ce, Wani hanzari ba gudu ba, Sultana ba ta ce ta yi RIDDA ba, sakin da ka yi mata saboda shan giyarta zai sa ta kullaci musulmi, ta ga cewa, tukuicin soyayyarta gare ka kenan, ta baro kowa nata da addininta ta biyo ka a karshe ga abin da ka saka mata da shi.
Ban sake ta saboda giya kadai ba. Na gaya miki ta karbi musulunci, amma ba ta sallah, mene ne marabarta da addininta na baya? Addinin ma da babu shi sam domin kuwa ba kirista ba ce, bayahudiyya ce (Jew). To cut it short, na yi nadamar aurenta tun farko, ban taba zaton Alanguburo zai amince ba, amma tashi guda ina fada bai turza ba, sai ya amince.
Had I know akwai Saade, kamar yadda ya ce tun farko ita ya so na aura ba zan taba yin wani aure ba.
Saade ba ta san lokacin da ta mike ta yi kofar fita ba, inda ta baro Fanna, kunya kamar ta yi ya ya. Tana ji Yaa Maira na fadin, Ka kore ta ka ji dadi. Saadatu dawo kin ji, yanzu zan sa Awaisu ya tattara shi su tai su ba mu wuri.
Ina! Saade ta kai kofa. Cewa ta ke, Yaa Maira zan dawo ne, idan na kara jin sauki.
Yareema ya daga murya yadda za ta jiyo shi ya ce,
In zo zance anjima bayan isha?
Ai saade kadan ya rage ta zura da gudu, suka dinga yi mata dariya.
Tana komawa unguwar su ta tadda Fulani ta dafa mata lafiyayyen faten acca da ya ji ganyen alayyahu da kabewa, ta zuba a faranti tana firfitawa da kanta tana jiran shigowarsu. Tana shigowa ta nufe ta da sauri.
Allah Sarki UWA! Saade ta fada a ranta, ta karbi cokali tana shan faten Fulani na tambayarta jikin Ya Gumsu, ta ce, ita ma tana jira Askirama ya shigo gida ne su shiga tare su dubo ta.
Saade ta tambayi Fulani, Ya ya aka kare ne da zancen auren Hanne?
Ta ce, An kai zancen kotun musulunci an yi mata gaiba, mun rabu a kan cikin watannin in ta gama iddah za ta dawo nan gabana, yaron a kai wa iyayen mijin. Plan dina akan ta shi ne a kai ta El-Kanemi, ta samu kwalin kammala sakandire sai a sama mata UNIMAID. Ta zauna hostel in sun yi hutu ta zo nan wajena ta yi hutun, har Allah ya ba ta mijin aure.
Saade ta gode wa Fulani, godiya maras adadi, tsarin da ta yi a kan rayuwar Hanne ya yi mata.
Ta ce, Su Raheema ko waya?
Ta ce, Kusan kullum muna magana da Maman, Raheema ta koma makaranta (university of Heartfordshire) wannan watan za ta kammala daga nan ku sha biki. Zan tambayi Maman lambarta na UK tunda yanzu akwai waya a hannunki.
Ta kyabe baki ta ce, Ni da na ji zafin maruka ina na tuna da wata waya?
(Tana nufin marin da su Ya Gumsu suka yi mata).
Fulani ta ce, Mari?
Nan ta gaya mata duk yadda aka yi, amma ba ta manta rokon da Yareema ya yi mata ba na ta boye zancen Dr. Ziyad ga iyayen su, it will create a serious problem idan suka ji, tunda dai mun bar NTNU din gabadaya shi ke nan. In ji yareema Sageer.
Sai dai tana tantama idan hukuncin da Yareema ya yanke musu is geniune, da gaske Abuja ta fice mata a ka, shi ma kuma Yareema haka, Dr. Ziyad yayi shattering zuciyar sa into pieces ya karya masa zuciya, ita kuma ya jefa tsoron rayuwar Abuja mai tsanani a tata zuciyar.
To amma makomar karatunta ta ke hangowa, shekaru ukun da ta kwashe cikin wahala da fadi-tashi sun tashi a banza ke nan? Above all aka ce sabo turken wawa. Ta saba da NTNU. Babu wata jamia da za ta bi bayan Nigerian Turkish Nile University a wurinta.
Fulani da ta ji duk abin da ya faru tsakanin Saade da su Ya Gumsu, sai ta jinjina kudirar Ubangiji. Ya Gumsu mai ja da ikon Allah dare daya yau gata ta zama sai dai a kwantar a tayar. Shin wannan bai ishi dan Adam ishara ba ya yarda cewa shi ba a bakin komai yake ba? Duk mulkinsa da izzarsa bai wuce talalar Ubangiji ba a duk lokacin da ya so? Bai isa ya sa, bai sa ya hana abinda Ubangiji ya hukunta ba?