Sashe 13
Masarautar Mu Part 4 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Askirama ya kura wa matarsa Bilkisu ido, yana mamakin kyawawan halayenta. Matansa sun kasa fahimtarta ne, amma duk ta fi su kyan hali, ba ta taba dauko zancen wata cikinsu ta kawo masa. Su kuwa basu da aiki sai fadin aibunta. Sun dauki kishin duniya su duka sun dora a kanta. Sun kasa gane ba kyawun halitta kadai ke rudarsa a kan Fulani Bilkisu ba, har da kyawawan halayenta.
Amma duk yadda ta so Askirama ya barta zuwa Abuja duba Ya Gumsu ya ki amincewa da hakan.
Yaa Maira ce ta zo ta hada kan sauran kannenta mata da maza aka ba su motoci da dogarai suka kama hanyar Abuja. Cikin tashin hankali. Hibbani da Yakirjinoma jirgi daya suka bi tare da Ahmad da Suhail wadanda za su kula da su.
Fulani ta kira Yareema a waya bayan ta koma dakinta. Muryar Yareema har ba ta fita sosai, kamar ta wanda ke fama da mura, shi kadai ya san halin da yake ciki. Ciwon da jikin sa ke masa sakamakon buguwar mota bai dame shi ba kamar hukuncin da Askirama ya yanke akan sa na nesanta shi da Saade.
Yana gidansa tun isowarsa ko falo bai leko ba tunda Askirama ya aiko Awaisu ya gaya masa sakon kada ya sake ya ganshi a fada ko shigifar sa, kuma kada ya sake ya je inda Saade ta ke. Har sai mahaifiyarsa ta bada hakurin cin zarafin da ta yi mata har dakin auren ta.
Ta kuma yi alkawarin karbar Saadatu matsayin suruka sannan ne shima zai janye nasa takunkumin.
Shi ya san wannan decision ba mai sauki ba ne ga Ya Gumsu, a yadda ya san kafaffiyar zuciya irin tata in tana kin abu. Kuma bai fita daga wannan zullumi da tashin hankalin ba a daren jiya Aunty Daja ta kira shi tana kuka, wai Ya Gumsun ta fadi a toilet ta samu stroke.
Ya kwana cikin wani hali na kaka-ni-ka-yi, and he is speachless.Wordless. Moodless. Ko magana ba ya iya yi. Awaisu ya so ya taya shi hira a daren ranar bayan ya bashi magani ya kira likita ya duba shi ya tabbatar babu mummunan rauni a jikin sa, ya ce ya tafi kawai ba ya bukata, sai kuma yanzu da wayewar garin yau ya samu wayar Fulani Bilkisu.
Yareemah, kana lafiya?
Ta fada cikin tausayawa. Ji ya yi idanunsa sun cicciko da kwalla, bai zaci wannan rahmar daga gare ta ba. Abin da bai sani ba shi ne, ita halinta ya bambanta da na sauran mata. Mace ce mai hangen nesa da tsananin kawaici da maida dan kowa nata.
Im sorry Fulani, Im sorry. Ya furta in a subdued voice.
Ta yi murmushi, ta ce, Ba zancen Saade ya sa na kira ka ba. Na kira ka ne in jajanta abin da ya faru da Ya Gumsu. Da accident da aka samu, Allah ya tsayar haka, Ya sa kaffara, Allah ya ba ta lafiya.
Na so in bi su Yaa Kirjinoma Abujan, Askirama ya hana ni, sabida ita ma Saade kwance ta ke babu lafiya tun isowarta.
Tamkar zuciyarsa za ta fito ta bakinsa sabida zullumi, ya ce cikin wata marainiyar murya,
Me ke damunta?
Fulani ta yi dan jimm! Kafin ta ce,
Na dauka ka sani ai.
Gabansa ya yi mugun faduwa, kada dai Saade ta gaya musu maganar Dr. Ziyad ne? Yau da ya shiga uku in Askirama ya ji zancen nan ya san aurensa da Saade ya kare.
Hawaye suka fito daga idanun Yareema Sageer ba tare da ya shirya ba. Amma sai Fulani ta fadi abin da ya gigita shi, ya wanke zuciyarsa daga duk wani rudani da dimauta da ta ke ciki.
Ciki ne tare da ita na kusan watanni biyu.
Yareema sai da ya cire wayar daga kunnensa, don ya tabbatar da wanda yake magana, My inlaw ba gizo kunnuwansa ke masa ba. Ya wani irin lumshe idanunsa yana karbar wani irin excitement a cikin kirjinsa.
Don haka ka kwantar da hankalinka ka koma Abuja ka kula da lafiyar mahaifiyarka. Saade tana karkashin kulawarmu insha Allah. Kafin sannan zuciyar Askirama ta huce sai a ba shi hakuri.
Abin da nake so yanzu shi ne ka koma Abuja ka yi jinyar mahaifiyarka.
Insha Allah, I will. Ya fada cikin girmamawa.
Har sun yi sallama ya kasa jurewa. Cikin jin nauyi ya ce,
Fulanin Sarki zan iya magana da Saadatu?
Fulani ta ce, Ta samu barci, in ka koma Abuja ka samu nutsuwa ka kira ni, zan ba ta wayar insha Allahu.
Da wannan suka yi sallama.
A washegarin ranar ya tattara ya koma Abuja.
*****
Yau asibitin national hospital Abuja ya ga iyalin masarautar Askira, ko ina ka wulga motoci ne cike da dogarai masu rubutun Askira Emirate. Tabbacin mara lafiyar na da alaka da hamshakiyar masarautar Askira. Lokacin da Yareema ya iso an kai Ya Gumsu daki na musamman (V.I.P room) an ba ta kwanciya.
Sanda suka shiga shi da Awaisu Ya Gumsu barci ta ke yi. Amma jin muryar Yareema na magana da likita sai ta hau kokarin bude idonta.
Duk da barcin da ya ci karfinta kokarin magana ta ke yi da bakinta da ya karkace, amma ta kasa. Yareema ya matsa daidai kanta yana hawaye yana fadin,
Ki yafe ni ya Gumsu, na kasa cika alkawarin da na yi miki, amma na alakanta hakan da rabon gaggawar da ya rantse a tsakaninmu.
Ya Gumsu Saadatu ciki gare ta, na kasa cika alkawarin ki Ya Gumsu na kasa. Ya saka kuka tare da kifa kansa a kan cikinta.
Da hannunta mai lafiyar ta mika tana shafa sumar kansa, tana ci gaba da kokarin furta magana abu ya gagara, sai hawaye ke bi ta gefen idonta. Amma daga yadda ta kama shi da hannu daya ta kankame tana hawaye ya san alheri ta ke son fada.
“Is ok Ya Gumsu, ki yi barci. Ni dai fatana ki fahimci cewa Saadatu alkhairi ce a gare mu kamar yadda Alanguburo ya hango. Ya Gumsu ki kwantar da hankalinki a kan Fulani Bilkisu da ahalinta, wallahi ba ta nufinki da sharri. Idan Askirama ya fi sonta ba ya nufin ke uwar yayansa ba ya sonki. Yana son ta ne saboda kyautatawar ta gareshi tafi taku. Amma kowa da gurbinta, kuma kowa da matsayinta.
Sai ki duba ki tace ki ga shin me take yi wanda Askirama ke so? Kema sai ki kwaikwaya.
Shaidan ne ya ke kambama miki soyayyar Askirama ga Fulani Bilkisu, amma ita in ya sa ta tana yi, in ya hana ta tana hanuwa. Ke kuwa fa Ya Gumsu? Abin da ki ka ga dama shi ki ke masa, yana hakuri saboda mu, Ya Gumsu lokaci bai yi ba da girma zai bayyana a halayenki?
Hawayenta ya dadu, sai gyada masa kai ta ke akai-akai kamar kadangaruwa. Yarima ya ci gaba da cewa.
Ya Gumsu ki yafe mini ban cika alkawarin da na yi miki ba, musamman da na ji kin ce bayan watanni uku za ki raba mu. Na kasa Ya Gumsu, na kasa Saadatu ciki ne da ita, zan yi azumin kaffara ki yafe mini.
Tana so ta ce masa babu kaffara a kanka, tunda ba fadar Ubangiji ba ce, sannan baka sabi Allah ba, amma ta kasa. Yarima ya rungume ta yana ci gaba da rokonta rangwame da afuwa a kan aurensa da Saadatu wanda ya kara karya zuciyar Ya Gumsu, ta amince soyayyar danta ga yar Fulanin Askirama wani hadi ne daga Allah, domin ya dinke barakar da ke tsakaninsu. Ya kawo maslaha da fahimtar juna ga iyalan Maimartaba Sarkin Askira.
Amma duk yadda ta so Askirama ya barta zuwa Abuja duba Ya Gumsu ya ki amincewa da hakan.
Yaa Maira ce ta zo ta hada kan sauran kannenta mata da maza aka ba su motoci da dogarai suka kama hanyar Abuja. Cikin tashin hankali. Hibbani da Yakirjinoma jirgi daya suka bi tare da Ahmad da Suhail wadanda za su kula da su.
Fulani ta kira Yareema a waya bayan ta koma dakinta. Muryar Yareema har ba ta fita sosai, kamar ta wanda ke fama da mura, shi kadai ya san halin da yake ciki. Ciwon da jikin sa ke masa sakamakon buguwar mota bai dame shi ba kamar hukuncin da Askirama ya yanke akan sa na nesanta shi da Saade.
Yana gidansa tun isowarsa ko falo bai leko ba tunda Askirama ya aiko Awaisu ya gaya masa sakon kada ya sake ya ganshi a fada ko shigifar sa, kuma kada ya sake ya je inda Saade ta ke. Har sai mahaifiyarsa ta bada hakurin cin zarafin da ta yi mata har dakin auren ta.
Ta kuma yi alkawarin karbar Saadatu matsayin suruka sannan ne shima zai janye nasa takunkumin.
Shi ya san wannan decision ba mai sauki ba ne ga Ya Gumsu, a yadda ya san kafaffiyar zuciya irin tata in tana kin abu. Kuma bai fita daga wannan zullumi da tashin hankalin ba a daren jiya Aunty Daja ta kira shi tana kuka, wai Ya Gumsun ta fadi a toilet ta samu stroke.
Ya kwana cikin wani hali na kaka-ni-ka-yi, and he is speachless.Wordless. Moodless. Ko magana ba ya iya yi. Awaisu ya so ya taya shi hira a daren ranar bayan ya bashi magani ya kira likita ya duba shi ya tabbatar babu mummunan rauni a jikin sa, ya ce ya tafi kawai ba ya bukata, sai kuma yanzu da wayewar garin yau ya samu wayar Fulani Bilkisu.
Yareemah, kana lafiya?
Ta fada cikin tausayawa. Ji ya yi idanunsa sun cicciko da kwalla, bai zaci wannan rahmar daga gare ta ba. Abin da bai sani ba shi ne, ita halinta ya bambanta da na sauran mata. Mace ce mai hangen nesa da tsananin kawaici da maida dan kowa nata.
Im sorry Fulani, Im sorry. Ya furta in a subdued voice.
Ta yi murmushi, ta ce, Ba zancen Saade ya sa na kira ka ba. Na kira ka ne in jajanta abin da ya faru da Ya Gumsu. Da accident da aka samu, Allah ya tsayar haka, Ya sa kaffara, Allah ya ba ta lafiya.
Na so in bi su Yaa Kirjinoma Abujan, Askirama ya hana ni, sabida ita ma Saade kwance ta ke babu lafiya tun isowarta.
Tamkar zuciyarsa za ta fito ta bakinsa sabida zullumi, ya ce cikin wata marainiyar murya,
Me ke damunta?
Fulani ta yi dan jimm! Kafin ta ce,
Na dauka ka sani ai.
Gabansa ya yi mugun faduwa, kada dai Saade ta gaya musu maganar Dr. Ziyad ne? Yau da ya shiga uku in Askirama ya ji zancen nan ya san aurensa da Saade ya kare.
Hawaye suka fito daga idanun Yareema Sageer ba tare da ya shirya ba. Amma sai Fulani ta fadi abin da ya gigita shi, ya wanke zuciyarsa daga duk wani rudani da dimauta da ta ke ciki.
Ciki ne tare da ita na kusan watanni biyu.
Yareema sai da ya cire wayar daga kunnensa, don ya tabbatar da wanda yake magana, My inlaw ba gizo kunnuwansa ke masa ba. Ya wani irin lumshe idanunsa yana karbar wani irin excitement a cikin kirjinsa.
Don haka ka kwantar da hankalinka ka koma Abuja ka kula da lafiyar mahaifiyarka. Saade tana karkashin kulawarmu insha Allah. Kafin sannan zuciyar Askirama ta huce sai a ba shi hakuri.
Abin da nake so yanzu shi ne ka koma Abuja ka yi jinyar mahaifiyarka.
Insha Allah, I will. Ya fada cikin girmamawa.
Har sun yi sallama ya kasa jurewa. Cikin jin nauyi ya ce,
Fulanin Sarki zan iya magana da Saadatu?
Fulani ta ce, Ta samu barci, in ka koma Abuja ka samu nutsuwa ka kira ni, zan ba ta wayar insha Allahu.
Da wannan suka yi sallama.
A washegarin ranar ya tattara ya koma Abuja.
*****
Yau asibitin national hospital Abuja ya ga iyalin masarautar Askira, ko ina ka wulga motoci ne cike da dogarai masu rubutun Askira Emirate. Tabbacin mara lafiyar na da alaka da hamshakiyar masarautar Askira. Lokacin da Yareema ya iso an kai Ya Gumsu daki na musamman (V.I.P room) an ba ta kwanciya.
Sanda suka shiga shi da Awaisu Ya Gumsu barci ta ke yi. Amma jin muryar Yareema na magana da likita sai ta hau kokarin bude idonta.
Duk da barcin da ya ci karfinta kokarin magana ta ke yi da bakinta da ya karkace, amma ta kasa. Yareema ya matsa daidai kanta yana hawaye yana fadin,
Ki yafe ni ya Gumsu, na kasa cika alkawarin da na yi miki, amma na alakanta hakan da rabon gaggawar da ya rantse a tsakaninmu.
Ya Gumsu Saadatu ciki gare ta, na kasa cika alkawarin ki Ya Gumsu na kasa. Ya saka kuka tare da kifa kansa a kan cikinta.
Da hannunta mai lafiyar ta mika tana shafa sumar kansa, tana ci gaba da kokarin furta magana abu ya gagara, sai hawaye ke bi ta gefen idonta. Amma daga yadda ta kama shi da hannu daya ta kankame tana hawaye ya san alheri ta ke son fada.
“Is ok Ya Gumsu, ki yi barci. Ni dai fatana ki fahimci cewa Saadatu alkhairi ce a gare mu kamar yadda Alanguburo ya hango. Ya Gumsu ki kwantar da hankalinki a kan Fulani Bilkisu da ahalinta, wallahi ba ta nufinki da sharri. Idan Askirama ya fi sonta ba ya nufin ke uwar yayansa ba ya sonki. Yana son ta ne saboda kyautatawar ta gareshi tafi taku. Amma kowa da gurbinta, kuma kowa da matsayinta.
Sai ki duba ki tace ki ga shin me take yi wanda Askirama ke so? Kema sai ki kwaikwaya.
Shaidan ne ya ke kambama miki soyayyar Askirama ga Fulani Bilkisu, amma ita in ya sa ta tana yi, in ya hana ta tana hanuwa. Ke kuwa fa Ya Gumsu? Abin da ki ka ga dama shi ki ke masa, yana hakuri saboda mu, Ya Gumsu lokaci bai yi ba da girma zai bayyana a halayenki?
Hawayenta ya dadu, sai gyada masa kai ta ke akai-akai kamar kadangaruwa. Yarima ya ci gaba da cewa.
Ya Gumsu ki yafe mini ban cika alkawarin da na yi miki ba, musamman da na ji kin ce bayan watanni uku za ki raba mu. Na kasa Ya Gumsu, na kasa Saadatu ciki ne da ita, zan yi azumin kaffara ki yafe mini.
Tana so ta ce masa babu kaffara a kanka, tunda ba fadar Ubangiji ba ce, sannan baka sabi Allah ba, amma ta kasa. Yarima ya rungume ta yana ci gaba da rokonta rangwame da afuwa a kan aurensa da Saadatu wanda ya kara karya zuciyar Ya Gumsu, ta amince soyayyar danta ga yar Fulanin Askirama wani hadi ne daga Allah, domin ya dinke barakar da ke tsakaninsu. Ya kawo maslaha da fahimtar juna ga iyalan Maimartaba Sarkin Askira.