Sashe 20
Kida A Ruwa Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read
..........“Halan bakaji inda nace ka kaini bane zaka yo nan dani?”.
Zaka rantse mai taxi baiji abinda Sanda ya faɗa ba. Ran Sanda ya fara ɓaci, cikin fusata ya fara masifa, yayi da turanci yayi da hausa. Amma mai taxi yayi kunnen uwar shegu da shi yana ta garzaza gudu. Sanda ya fahimci dole ne yay wani abu a wannan gaɓar. Dan wannan mai taxi ɗin ɗayan biyu ne. Kodai ƴan one chance, ko liƙi ne ya buɗe abokan hamayya masu neman sa'a suka harbo shi. Ina hakan bazai faru ba, dolene ya ƙarasa abinda ya fara...
Da wannan tunanin ya mamayi drivern ya kai masa mahangurɓa a wuya. Sai dai ina shima ƙwararre ne, dan cike da salon ganewa ya duƙe kan steering. Yana kuma ɗagowa ya wanke fuskar Sanda da spry. Luuu Sanda yay baya ya zube a kujera.
Dariya Driver ya ƙyalƙyale da ita harda duka steering. Daga haka ya ƙarama motar wuta zuwa inda ya nufa...
•=•===•===•=•
Koda Nimrah ta dawo sashenta saboda korosu da Gwaggo Khadijah tayi bayan wucewar su Aunty Mommy wanka ta fara yi. Tasan har yanzu Dadah baya gida, dan in ya dawo bazai taɓa wutowa bai shiga gun su Mammah ba. Wanka tayi ta gyara jikinta. Duk da Magriba tayi tsaff ta shirya kanta cikin skirt da riga na lass. Dama indai kwalliya ce da iyayi a bar musu kayansu ita da Ruƙayya. Uban turaren data zuba a jikinta ga kabbasa har ji take yana hawa mata kai. Sashen nata ma ta sake saka turare kai kace yau ɗin itace da Dadahn. Wannan duk yana a cikin sabon karatun su Lailah. Sun tabbatar mata ba sai ranar girkinta zatace zatai abinda ya dace ga miji ba. Ita mace mai abokiyar zama tanayi abinda zai saka oga jin ƙaguwa dawowa wajenta a duk randa yake ba nata ba. Da wannan tunanin ta kammala saka kamshi ta koma bedroom tai sallar isha'i da aka kira, bayan ta idar karo na farko ta shiga kitchen ɗinta da nufin dafa wani abu, sai da ta gama ƙare masa kallo har store duk da ɗazu ko ina sun shiga da su Small Mom. Madara ta ɗakko da kayan tea ta kawo kitchen, komai ta zuba shi inda ya dace sannan ta ɗibo madara da yawa ta saka mata ruwa. Bata damu da yanda tai kauri ba dan yawunta har tsinkewa yake ta ɗakko biscuit ta fito. A kayan abinci da su Ja'afar suka kawo sashen nata daga ita har Ruky harda kayan kwalam aka haɗa musu saboda sanin halinsu....
.....★ A dai-dai wannan lokacin motar Daddy Imran daya maido Dadah gida ke tsayawa ƙofar sashen. Daga gidan Uncle Nasiru suke, bayan sun bar gidan Baffa can suka je. Sai da sukai sallar magriba da isha'i suka baro. Dadah dake kwance jikin sit idanunsa a lumshe ya buɗesu a hankali. Idanun sunyi ja kaɗan, sannan jijiyar kansa ya ɗan fito.
Cikin kasa haƙuri Imran ya ce, “Zak.. kamar baka da lafiya fa?”.
Ƙaramin tsaki Dadah yayi, ya ɗan furzar da huci yana mirza goshinsa kaɗan. “Kaina ke ciwo. Kwana biyu kenan na rasa mi yasa. Da ance maka yamma tayi sai naji yanayina na sauyawa kamar zanyi zazzaɓi, sai dai ƙarshe ciwon kai yake komawa”.
“Kaje asibiti?”.
“No. Ba wani serious bane bafa”.
“Babu ciwon daba serious ba. Musamman ma kai da har yanzu kake kan shan magani. Bari kawai mu juya asibiti”.
“Bari dai mu gani kwana biyu in bai daina ba. Ya kamata kaje gida kaima ka huta.”
“Shike nan, amma dan ALLAH kasha magani idan ka shiga. Maganar haɗuwa da Janar ma anjima kawai ka barta, zan masa bayani. Su Faro ma yau suke shirin kama Ojo”.
“Good. Bazai yiwu ba Imran, dole mu gansa muma yau. Kasan bamu da wani isashen lokaci kasancewar mun rikita duniyar mutanen nan, yanzu kowane irin lissafi yazo musu yi zasuyi. Babban fatanmu dai Faro su kama Ojo ɗin”.
“Haka ne, amma ai lafiya tafi komai.”
“Karka damu zan iya. Dan ina son shiga UNIT ZERO ma da gobe in sha ALLAHU. Ya kamata nayi magana ta farko da tsohon driver ɗin nan. Idan Madam ta barka ka fito mu haɗu”.
“Oh idan ma ta barni ne ko?”.
Murmurshi Dadah yayi batare da yace komai ba ya buɗe motar ya fice. “Ka isa gida cikin amincin UBANGIJI”. Ya faɗa yana rufe masa motar kawai. Murmurshi Imran yayi shima ya tada motar ya fice.
Sai da Dadah ya fara shiga sashen Mammah. Bai jima ba ya fito dan ya samu tana waya da Ummu matar Uncle Nasiru. Yasan kuma wayarsu bamai ƙarewa bace cikin sauƙi. Gara yaje idan yayi wanka ya dawo, dan shima baya son katse su ma...
Kamar ko yaushe babban falon a gyare, sannan Rayhana mayyayatu na zaune, sai Amimah tsaye da waya a hannu tana miƙa mata. Da alama Amima zuwa falon tayi kawo wayar. Kusan tare sukai masa sannu da zuwa. Sai dai Rayhana an wani kashe murya.
Amsa musu yayi yana wucewarsa kai tsaye sashen Nimrah. Ba Rayhana ba hatta Amimah sai da ɓata fuska. Dan ita fa kishin take taya Nabeeha da gaske. Aiko tana ganin Dadahn ya shige fuuu ta tafi sashen su kaima Nabeeha rahoto...
....Buɗe ƙofar da ƙamshin turarensa ya saka Nimrah da idonta ke kan television tana kallo da shan biscuit ɗinta da take sakawa cikin madara ta juyi da sauri. Ido suka haɗa da Dadah dake maida ƙofar ya rufe. Kyakkyawan murmushi ta sakar masa, tare da ajiye kofin ta taso inda yake. Harta iso idanunsa a kanta. Kanta tsaye jikinsa ta shige. Cikin ƙanƙamesa ta ce, “I miss you Mijin Naja'atu Nimrah”.
Murmurshin da bai shirya ba ya saki. Ya sauke nashi hannun ɗaya a bayanta yana ɗan bubbugawa na lallashi. Kafin cikin ƙaramin sauti ya furta, “Kin tabbatar?”.
Kai ta jinjina masa batare data ɗago ba.
“Uhmm to mi Mijin Naja'atu Nimrah zai samu?”.
Bai ma gama rufe baki ba ta ɗago tare da yin ɗiɗɗishe ta sumbaci gefen wuyansa. Lipstick ɗin data ƙawata bakinta da shi ya manne batare da Dadah ya sani ba. Sai kuma da sauri ta sake mayar da kanta ta ɓoye a jikinsa tare da sake rungume shi tana murmurshi.
Saitin kunnen ya duƙo ya raɗa mata. “Mijin Naja'atu Nimrah na godiya, sai dai wannan ya yi masa kaɗan”. Yay maganar da ɗago fuskarta ya nuna mata lips ɗinsa. Murmurshi tayi, sannan ta matsar da fuskartata gab da tashi har kowa na jin saukar numfashin ɗan uwansa. Yanda ta matso da lips ɗin ta gab da nashi yasa shi lumshe ido yana jiran saukar nata. Ganin ya sakankance kawai ta kwace jikinta ta bar wajen tana masa dariyar ƙeta.
Lips ɗin ya cije a hankali yana buɗe idanunsa ya bita da kallo. Sai kuma ya miƙe cike da basarwa ya koma kan ƙafafunsa ya tsaya da ƙyau. A lokacin Nimrah ke dawowa da ruwa mara sanyi da glass cup data ɗoro akan ƙaramin tray mai ƙyau. Har yanzu fuskarta da murmushi ta ce, “Dadah ga ruwa.”
“Sha abinki na ƙoshi”.
Ya faɗa kamar irin yayi fushin nan. Nimrah data yarda fushin yayi ta ajiye tray ɗin tana dawowa inda yake. Hannunsa ta kama cike da shagwaɓa tana diddira ƙafa ta ce, “Yi haƙuri na tuba. Naji zan maka idan kasha”.
“Ni zakima wayo?”.
“ALLAH Dadah da gaske.”
Idan ya biye mata yasan zata iya tada rikici. Dan hakan ya fara takawa kawai zuwa kujerar data ajiye ruwan. Zaune ya kai, ita kuma ta zuba a kofin ta miƙa masa.
“Thanks”.
Ya faɗa yana kai kofin bakinsa. Ita kuma ta ɗan zubama kansa idanunta. A bazata yaji saukar yatsarta a saman kansa.
“Dadah kanka na maka ciwo ko?”.
(Yarinyar nan wayonta yayi yawa) Ya faɗa a zuciyarsa yana kallonta. Kafin ma yace wani abu ta miƙe tana sake faɗin, “Dan ALLAH Dadah jirani ina zuwa”. Ta shige bedroom. Babu jimawa sai gata ta fito da ɗan ƙaramin towel a hannu. Ta bayansa taje yanzu ta tsaya. Kan nasa ta kama ta kwanto jikin kujerar sosai, hakan ya sashi ɗaga idanun sa ya kalleta. Dai-dai tana sauke towel ɗin hannunta dake a jiƙe saman goshinsa. Sanyin ya ratsa shi. Har sai da yaja ɓoyayyar ajiyar zuciya. A zahiri kuma ya yamutsa fuska kaɗan.
“Sorry Baby na kada kayi kuka”.
Ta faɗa cikin kunensa da raɗa. Tana gama faɗa kuma ta saka tafin hannunta ta rufe masa idanu tana ƴar dariya. Sai kuma a bazata yaji saukar ƙananun lips ɗinta kan nashi. Kaɗan tayi ta janye tana zamewa bayan kujerar.
Rasama abin yi Dadah yay. Dan gaba ɗaya ta gama tsinka masa jini. Dole ya miƙe a hankali yana cire towel ɗin data saka masa ya juya shi, yana dafe da shi a goshin nasa ya zagayo inda take a bayan kujerar. Kanta tai saurin cusawa a tsakanin ƙafafu.
“Dadah kada kayi magana dan ALLAH sai da safe”.
Ya tabbatar yarinyar nan sai ta saka shi sakin layuka a bainar nasi watarana. Baiyi maganar ba kamar yanda ta roƙa, ya cire towel ɗin kawai ya kama hannunta ɗaya ya sanya mata a ciki. Sai kuma ya kamo ɗaya ya sumbaci tsakiyarsa kawai ya juya ya fice a binsa yana murmurshi..........✍️
_Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._
*_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_*
*_+227 98 94 12 81_*
*_My NITA_*
*_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_*
_Shaidar biya👇_
*_Whatsapp number_*
*_+227 98 94 12 81_*
*_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_*
*9032345899*
*_Moniepoint MFB_*
*_BILKISU MUSA IBRAHIM_*
*_KATI MTN (1k)_*
*_09032345899_*
*_Shaidar biya: 👇_*
*_Telegram Number 09032345899_*
*_AREWABOOKS (Vvip)_*
*_Chapters & Audio_*
@BilynAbdull
*_WHATSAPP (500)_*
*1487616276*
*_Access Bank_*
*_Bilkisa Ibrahim Musa_*
*_Kati MTN:- (500)_*
*_09032345899_*
*_Shaidar biya:-_*
*_Whatsapp Number +234 805 568 7449_*
*_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_*
*_WhatsApp Number 👇_*
*+234 805 568 7449*
*_Telegram Number👇_*
*+234 903 234 5899*
*_Maza ku matso MASOYAN Bilyn Abdull da IDANU suka hana karatun novels...._*
*_Tofa Bilyn ku ta samo muku hanya mai sauƙi da kina aiki, ko kina kwance kina hutawa, ko kina inda baki son yawan surutu earpiece ɗinki kawai zaki maƙala a kunne ko Bluetooth kisha sauraren littafin KIƊA A RUWA.... Cikin sauƙi.... 💃_*
Zaka rantse mai taxi baiji abinda Sanda ya faɗa ba. Ran Sanda ya fara ɓaci, cikin fusata ya fara masifa, yayi da turanci yayi da hausa. Amma mai taxi yayi kunnen uwar shegu da shi yana ta garzaza gudu. Sanda ya fahimci dole ne yay wani abu a wannan gaɓar. Dan wannan mai taxi ɗin ɗayan biyu ne. Kodai ƴan one chance, ko liƙi ne ya buɗe abokan hamayya masu neman sa'a suka harbo shi. Ina hakan bazai faru ba, dolene ya ƙarasa abinda ya fara...
Da wannan tunanin ya mamayi drivern ya kai masa mahangurɓa a wuya. Sai dai ina shima ƙwararre ne, dan cike da salon ganewa ya duƙe kan steering. Yana kuma ɗagowa ya wanke fuskar Sanda da spry. Luuu Sanda yay baya ya zube a kujera.
Dariya Driver ya ƙyalƙyale da ita harda duka steering. Daga haka ya ƙarama motar wuta zuwa inda ya nufa...
•=•===•===•=•
Koda Nimrah ta dawo sashenta saboda korosu da Gwaggo Khadijah tayi bayan wucewar su Aunty Mommy wanka ta fara yi. Tasan har yanzu Dadah baya gida, dan in ya dawo bazai taɓa wutowa bai shiga gun su Mammah ba. Wanka tayi ta gyara jikinta. Duk da Magriba tayi tsaff ta shirya kanta cikin skirt da riga na lass. Dama indai kwalliya ce da iyayi a bar musu kayansu ita da Ruƙayya. Uban turaren data zuba a jikinta ga kabbasa har ji take yana hawa mata kai. Sashen nata ma ta sake saka turare kai kace yau ɗin itace da Dadahn. Wannan duk yana a cikin sabon karatun su Lailah. Sun tabbatar mata ba sai ranar girkinta zatace zatai abinda ya dace ga miji ba. Ita mace mai abokiyar zama tanayi abinda zai saka oga jin ƙaguwa dawowa wajenta a duk randa yake ba nata ba. Da wannan tunanin ta kammala saka kamshi ta koma bedroom tai sallar isha'i da aka kira, bayan ta idar karo na farko ta shiga kitchen ɗinta da nufin dafa wani abu, sai da ta gama ƙare masa kallo har store duk da ɗazu ko ina sun shiga da su Small Mom. Madara ta ɗakko da kayan tea ta kawo kitchen, komai ta zuba shi inda ya dace sannan ta ɗibo madara da yawa ta saka mata ruwa. Bata damu da yanda tai kauri ba dan yawunta har tsinkewa yake ta ɗakko biscuit ta fito. A kayan abinci da su Ja'afar suka kawo sashen nata daga ita har Ruky harda kayan kwalam aka haɗa musu saboda sanin halinsu....
.....★ A dai-dai wannan lokacin motar Daddy Imran daya maido Dadah gida ke tsayawa ƙofar sashen. Daga gidan Uncle Nasiru suke, bayan sun bar gidan Baffa can suka je. Sai da sukai sallar magriba da isha'i suka baro. Dadah dake kwance jikin sit idanunsa a lumshe ya buɗesu a hankali. Idanun sunyi ja kaɗan, sannan jijiyar kansa ya ɗan fito.
Cikin kasa haƙuri Imran ya ce, “Zak.. kamar baka da lafiya fa?”.
Ƙaramin tsaki Dadah yayi, ya ɗan furzar da huci yana mirza goshinsa kaɗan. “Kaina ke ciwo. Kwana biyu kenan na rasa mi yasa. Da ance maka yamma tayi sai naji yanayina na sauyawa kamar zanyi zazzaɓi, sai dai ƙarshe ciwon kai yake komawa”.
“Kaje asibiti?”.
“No. Ba wani serious bane bafa”.
“Babu ciwon daba serious ba. Musamman ma kai da har yanzu kake kan shan magani. Bari kawai mu juya asibiti”.
“Bari dai mu gani kwana biyu in bai daina ba. Ya kamata kaje gida kaima ka huta.”
“Shike nan, amma dan ALLAH kasha magani idan ka shiga. Maganar haɗuwa da Janar ma anjima kawai ka barta, zan masa bayani. Su Faro ma yau suke shirin kama Ojo”.
“Good. Bazai yiwu ba Imran, dole mu gansa muma yau. Kasan bamu da wani isashen lokaci kasancewar mun rikita duniyar mutanen nan, yanzu kowane irin lissafi yazo musu yi zasuyi. Babban fatanmu dai Faro su kama Ojo ɗin”.
“Haka ne, amma ai lafiya tafi komai.”
“Karka damu zan iya. Dan ina son shiga UNIT ZERO ma da gobe in sha ALLAHU. Ya kamata nayi magana ta farko da tsohon driver ɗin nan. Idan Madam ta barka ka fito mu haɗu”.
“Oh idan ma ta barni ne ko?”.
Murmurshi Dadah yayi batare da yace komai ba ya buɗe motar ya fice. “Ka isa gida cikin amincin UBANGIJI”. Ya faɗa yana rufe masa motar kawai. Murmurshi Imran yayi shima ya tada motar ya fice.
Sai da Dadah ya fara shiga sashen Mammah. Bai jima ba ya fito dan ya samu tana waya da Ummu matar Uncle Nasiru. Yasan kuma wayarsu bamai ƙarewa bace cikin sauƙi. Gara yaje idan yayi wanka ya dawo, dan shima baya son katse su ma...
Kamar ko yaushe babban falon a gyare, sannan Rayhana mayyayatu na zaune, sai Amimah tsaye da waya a hannu tana miƙa mata. Da alama Amima zuwa falon tayi kawo wayar. Kusan tare sukai masa sannu da zuwa. Sai dai Rayhana an wani kashe murya.
Amsa musu yayi yana wucewarsa kai tsaye sashen Nimrah. Ba Rayhana ba hatta Amimah sai da ɓata fuska. Dan ita fa kishin take taya Nabeeha da gaske. Aiko tana ganin Dadahn ya shige fuuu ta tafi sashen su kaima Nabeeha rahoto...
....Buɗe ƙofar da ƙamshin turarensa ya saka Nimrah da idonta ke kan television tana kallo da shan biscuit ɗinta da take sakawa cikin madara ta juyi da sauri. Ido suka haɗa da Dadah dake maida ƙofar ya rufe. Kyakkyawan murmushi ta sakar masa, tare da ajiye kofin ta taso inda yake. Harta iso idanunsa a kanta. Kanta tsaye jikinsa ta shige. Cikin ƙanƙamesa ta ce, “I miss you Mijin Naja'atu Nimrah”.
Murmurshin da bai shirya ba ya saki. Ya sauke nashi hannun ɗaya a bayanta yana ɗan bubbugawa na lallashi. Kafin cikin ƙaramin sauti ya furta, “Kin tabbatar?”.
Kai ta jinjina masa batare data ɗago ba.
“Uhmm to mi Mijin Naja'atu Nimrah zai samu?”.
Bai ma gama rufe baki ba ta ɗago tare da yin ɗiɗɗishe ta sumbaci gefen wuyansa. Lipstick ɗin data ƙawata bakinta da shi ya manne batare da Dadah ya sani ba. Sai kuma da sauri ta sake mayar da kanta ta ɓoye a jikinsa tare da sake rungume shi tana murmurshi.
Saitin kunnen ya duƙo ya raɗa mata. “Mijin Naja'atu Nimrah na godiya, sai dai wannan ya yi masa kaɗan”. Yay maganar da ɗago fuskarta ya nuna mata lips ɗinsa. Murmurshi tayi, sannan ta matsar da fuskartata gab da tashi har kowa na jin saukar numfashin ɗan uwansa. Yanda ta matso da lips ɗin ta gab da nashi yasa shi lumshe ido yana jiran saukar nata. Ganin ya sakankance kawai ta kwace jikinta ta bar wajen tana masa dariyar ƙeta.
Lips ɗin ya cije a hankali yana buɗe idanunsa ya bita da kallo. Sai kuma ya miƙe cike da basarwa ya koma kan ƙafafunsa ya tsaya da ƙyau. A lokacin Nimrah ke dawowa da ruwa mara sanyi da glass cup data ɗoro akan ƙaramin tray mai ƙyau. Har yanzu fuskarta da murmushi ta ce, “Dadah ga ruwa.”
“Sha abinki na ƙoshi”.
Ya faɗa kamar irin yayi fushin nan. Nimrah data yarda fushin yayi ta ajiye tray ɗin tana dawowa inda yake. Hannunsa ta kama cike da shagwaɓa tana diddira ƙafa ta ce, “Yi haƙuri na tuba. Naji zan maka idan kasha”.
“Ni zakima wayo?”.
“ALLAH Dadah da gaske.”
Idan ya biye mata yasan zata iya tada rikici. Dan hakan ya fara takawa kawai zuwa kujerar data ajiye ruwan. Zaune ya kai, ita kuma ta zuba a kofin ta miƙa masa.
“Thanks”.
Ya faɗa yana kai kofin bakinsa. Ita kuma ta ɗan zubama kansa idanunta. A bazata yaji saukar yatsarta a saman kansa.
“Dadah kanka na maka ciwo ko?”.
(Yarinyar nan wayonta yayi yawa) Ya faɗa a zuciyarsa yana kallonta. Kafin ma yace wani abu ta miƙe tana sake faɗin, “Dan ALLAH Dadah jirani ina zuwa”. Ta shige bedroom. Babu jimawa sai gata ta fito da ɗan ƙaramin towel a hannu. Ta bayansa taje yanzu ta tsaya. Kan nasa ta kama ta kwanto jikin kujerar sosai, hakan ya sashi ɗaga idanun sa ya kalleta. Dai-dai tana sauke towel ɗin hannunta dake a jiƙe saman goshinsa. Sanyin ya ratsa shi. Har sai da yaja ɓoyayyar ajiyar zuciya. A zahiri kuma ya yamutsa fuska kaɗan.
“Sorry Baby na kada kayi kuka”.
Ta faɗa cikin kunensa da raɗa. Tana gama faɗa kuma ta saka tafin hannunta ta rufe masa idanu tana ƴar dariya. Sai kuma a bazata yaji saukar ƙananun lips ɗinta kan nashi. Kaɗan tayi ta janye tana zamewa bayan kujerar.
Rasama abin yi Dadah yay. Dan gaba ɗaya ta gama tsinka masa jini. Dole ya miƙe a hankali yana cire towel ɗin data saka masa ya juya shi, yana dafe da shi a goshin nasa ya zagayo inda take a bayan kujerar. Kanta tai saurin cusawa a tsakanin ƙafafu.
“Dadah kada kayi magana dan ALLAH sai da safe”.
Ya tabbatar yarinyar nan sai ta saka shi sakin layuka a bainar nasi watarana. Baiyi maganar ba kamar yanda ta roƙa, ya cire towel ɗin kawai ya kama hannunta ɗaya ya sanya mata a ciki. Sai kuma ya kamo ɗaya ya sumbaci tsakiyarsa kawai ya juya ya fice a binsa yana murmurshi..........✍️
_Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._
*_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_*
*_+227 98 94 12 81_*
*_My NITA_*
*_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_*
_Shaidar biya👇_
*_Whatsapp number_*
*_+227 98 94 12 81_*
*_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_*
*9032345899*
*_Moniepoint MFB_*
*_BILKISU MUSA IBRAHIM_*
*_KATI MTN (1k)_*
*_09032345899_*
*_Shaidar biya: 👇_*
*_Telegram Number 09032345899_*
*_AREWABOOKS (Vvip)_*
*_Chapters & Audio_*
@BilynAbdull
*_WHATSAPP (500)_*
*1487616276*
*_Access Bank_*
*_Bilkisa Ibrahim Musa_*
*_Kati MTN:- (500)_*
*_09032345899_*
*_Shaidar biya:-_*
*_Whatsapp Number +234 805 568 7449_*
*_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_*
*_WhatsApp Number 👇_*
*+234 805 568 7449*
*_Telegram Number👇_*
*+234 903 234 5899*
*_Maza ku matso MASOYAN Bilyn Abdull da IDANU suka hana karatun novels...._*
*_Tofa Bilyn ku ta samo muku hanya mai sauƙi da kina aiki, ko kina kwance kina hutawa, ko kina inda baki son yawan surutu earpiece ɗinki kawai zaki maƙala a kunne ko Bluetooth kisha sauraren littafin KIƊA A RUWA.... Cikin sauƙi.... 💃_*