← Book details Kida A Ruwa Part 4 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 27

Sashe 10

Kida A Ruwa Part 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read

    Kowa sai da Nimrah ta gaisa da shi a gidan. Dan tsabar yanda suka daɗe suna waya hatta su Ja'afar sai da suka dawo suka iske. Hakama su Afrah da aka ɗakko a Islamiyya. Su Kulu ma sai da ta gaisa da su.
       Abu mafi burge Mammah da Nimrah tayi shine akaf labarin Dubai da take basu bata saka sunan Dadah ba balle wani abu daya faru tsakaninsu. Ita kawai taga kaza ne taga kaza. Amma tace wai ni da Dadah munje waje kaza. A'a bata ambata ba. Hakan na nuna tsantsar sirranta mutuncin mijinta a wajen ƙannensa da ita kanta mahaifiya. Bayyananniyar kunya da nuna girmamawa tsantsa data burge har su Ma'aruff. Hakama su Bilal da Ammar. Balle Gwaggo Khadijah da ke jin salon yarinyar ya gama kaita ƙololuwa.
         Sai da mazajen na Mammah suka wuce massalaci sallar magriba tunda Nimrah ta shagaltar da su ko sashen su basu karasa ba sun ɓige anan. To duka matan nasu ma anan suka same su. Ruƙayya na ganin Mammah da Gwaggo Khadijah sun shige bedroom yin salla ta silale tsohon ɗakinsu da wayar. Dariya su Lailah suka sanya mata dan sun san dai aminai ne za'ai gulma. Har Asma'u na faɗin, “Idan akai gulmata kuma ban yafe ba”.
     Hararta Ruky ta juyi tayi kawai, batare da tayi magana ba ta rufe ƙofar harda saka key. Nimrah dake jiyo su ta ce, “Aunty Ma'u ce ko?”.
        “Barta zan bata amsa ai. Ninah kin barni da damuwa tun ranar. Na rasa ya zan same ki. Kuma ina shakkar kiran layin nan na Dadah, kada a samu akasi ya ɗaga”.
      “Garama da baki kira ba ai. Kinga saƙona kuwa?”.
    “Na gani mana, ALLAH yaso dai ban gayama Uncle Ammar ba dan nayi niyyar hakan”.
       “Kambu sannu ƴar daɗi soyayya.”
   Cewar Nimrah da sauri. Ruƙayya ta sanya dariya.
     “Oh hakama zaki ce?”.
“Eh mana. To in ba daɗi soyayya ba miya kaiki. Yanzu dai Please sirri ne maganar nan. Kema kuma ki daina damuwa har na dawo sai mu tattauna sosai.”
          “Shike nan, amma kin san abin ya tsaya min a rai da yawa?”.
      “Dan ALLAH ki cire shi komai mai sauƙi ne. Kuma kamar yanda na gaya miki yana shan magani. Duk da bai taɓa sha a gabana ba. Kuma idan lissafin da suka sa yayi dai-dai da nawa ai kinga ya kusa daina sha tunda shekara naji doctor ɗin yace”.
         “Alhamdullahi ALLAH ya bashi lafiya. Ya kuma kiyaye gaba. ALLAH sarki Dadah bawan ALLAH. Ko mi yasa yake ɓoyewa to?”.
      “Saboda kar ya tada hankalin kowa mana. Amma zuciyata cike take da son sanin wanda sukai masa hakan. A dalilin miye? Mi yay musu? Tunda kinga mudai a sani mu ance yana ƙasar waje ne. Anan kuma naji an ambaci prison”.
         “Prison?”.
     “Humm ke dai yi shiru sai nazo. Amma aikin da nake son ki fara mana kiɗan fara bincika mana wajen Uncle Ammar. Irin ki nuna kin gani a media ne haka...”
        “Shawara mai ƙyau. Karki damu a yau ɗin nan ma kuwa”.
    “A'a ba yau ba. Kin san zai iya tsarguwa tunda munyi waya. Kamar dai nan da kwana biyu. Koma gab da zamu dawo dan Dadah yace nan da sati ɗaya”.
          “Okay ba damuwa. Amma yanzu ya zamu cigaba da waya?”.
      “Zan dinga kira idan ya bani aron wayar. Dan bansan miya sa tawa taƙi yi ba. Har hotspot ɗinsa na buɗe amma date na yaƙi motsawa balle WhatsApp ɗin yayi na kira tunda sai tanan. Na masa magana yace akwai matsala ne. Shiyyasa na ajiye ta kawai”.
          “Shike nan to. Bari naje naji maganar su Uncle's sun dawo massalaci gasu can.”
      “Maza jeki sai na kira”.
Daga haka sukai sallama. Nimrah ta sauke ajiyar zuciya. Sosai take jin nauyin ƙirjinta ya ragu tsakanin maganar farko da sukai da yau. Ko yaya ta ɗan fidda wani abunda ke'a ranta wata da watanni. Hakan kuma sai ya buɗe mata tunaninta. Musamman akan mutanen can da alamarin su ya kasa shuɗe mata. Ta tabbatar suna bibiyarta kamar yanda suka faɗa, kuma suna jiran ranar da zasu amshi amsar aikin da suka bata. Shiyyasa take ganin dole ta shirya. Kodai lokaci yayi da zata gane da gaske Dadan ne mai gaskiya, ko kuma su ɗinne masu gaskiyar. Dan jira take kawai su koma gida, daga lokacin ne kuma SABON WASAN ZAI FARA a duka ɓangarorin biyu. Ita da NABEEHA, sannan ITA da DADAH a bayan fage.....

      Hhhhh to bari muga wazai lashe kofin🤣🤣🏃🏼‍♀️🏃🏼‍♀️.

∆×∆×∆×∆×∆

       A gaba Oga Jush da tantiriyarsa suka saka Dadah zuwa wani ɗaki. Bai yi musu musu ba ya fara tafiya. Su ko suna biye da shi suna ƙare masa kallo cike da shaiɗancin da kowanne yafi ƙwarewa..
      Bedroom ɗin ma dai ɓata lokaci ne lissafin alatunsa. Dan ko gadon ciki aka barka da shi an haɗaka da lissafin aiki. Jush ya tsaya a bayan Dadah. Hannu ya kai zai taɓa masa ƙugu Dadah ya cafke hannun a cikin nashi. Juyowa yay fuskarsa da murmushin da Jush ɗin baya gani na tsantsar ta kaici. Shi ko wawan dariya ya saki da zuƙar sigari ya matsa kusa da Dadan gab. Dadah yaja jikinsa baya. Oga Jush ya sake matsawa. Ya sake ja baya, shima ya sake binshi tamkar wasu saurayi da budurwa ko mata da miji. Sai da Dadah ya dangane da gadon sannan ya tsaya cak. Muguwar dariya Jush ɗin ya saki tare da kai hannu saman ɗan kamfansa ya katse shi.
     Tsinanne sai gashi zirr. Dadah fuskarsa kawai yake kallo. Duk da ya fahimci abinda yayi. Dan wani irin kamo hannunsa Jush yayi kawai yayi, ɗayan hannun kuma ya zare gilashinsa. Kallon ido cikin ido sukama juna. Kallon daya saka Jush kamar ƴar kaɗuwa dan har sai da yaja jikinsa baya ma. Da wannan damar kuma Dadah yay amfani ya ɗaga ƙafarsa ya buga masa gwiwar a gabansa.
     Ba arziƙi Jush ya wage baki zai fasa ƙara Dadah ya rufe shi rufff da hannunsa yana mai fisgarsa ya wuraga a gadon. Sai kuma ya saka hannu ya sake fisgar blanket ya jefa masa a jiki dan baya fatan kallon mummunan tsiraicin tsohon banza.
        Wani irin rawa jikin budurwarsa yaso farawa ganin yanda Dadah ya cika bakin Jush ɗin da wani abu daya hana shi magana. Koma miye ya zuba masa shi lokacin daya toshe masa baki. Da sauri ta zaburo ta matso. Dan ita dai ba haka sukai da Dadan ba ai. Cikin ƙaraji da tsawa ta ce, “Ka haukace ne? Ai ba haka mukai da kai ba?”...........✍️

_Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._

*_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_*
*_+227 98 94 12 81_*
*_My NITA_*

*_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_*

_Shaidar biya👇_

*_Whatsapp number_*
*_+227 98 94 12 81_*

*_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_*

*9032345899*
*_Moniepoint MFB_*
*_BILKISU MUSA IBRAHIM_*

*_KATI MTN (1k)_*
*_09032345899_*

*_Shaidar biya: 👇_*
*_Telegram Number 09032345899_*

*_AREWABOOKS (Vvip)_*
*_Chapters & Audio_*
@BilynAbdull

*_WHATSAPP (500)_*

*1487616276*
*_Access Bank_*
*_Bilkisa Ibrahim Musa_*

*_Kati MTN:- (500)_*
*_09032345899_*

*_Shaidar biya:-_*
*_Whatsapp Number +234 805 568 7449_*

*_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_*

*_WhatsApp Number 👇_*
*+234 805 568 7449*
*_Telegram Number👇_*
*+234 903 234 5899*

*_Maza ku matso MASOYAN Bilyn Abdull da IDANU suka hana karatun novels...._*

*_Tofa Bilyn ku ta samo muku hanya mai sauƙi da kina aiki, ko kina kwance kina hutawa, ko kina inda baki son yawan surutu earpiece ɗinki kawai zaki maƙala a kunne ko Bluetooth kisha sauraren littafin KIƊA A RUWA.... Cikin sauƙi.... 💃_*

*_Kar dai na cika ku da zance. Zamu fara saida littafin KIƊA A RUWA.... Na saurare (Audio) kenan akan farashi mai sauƙi da rahusa._*

*_Akwai VVIP AREWAPEN kenan 💃_*

*_Akwai VIP Telegram 💃_*

*_(Ƴan WhatsApp ku haƙura kawai ƴan ta'addar bati sunfi yawa a cikinku gaskiya tsoron rashin m ɗinku nake 😂🤣)_*

*_Telegram Audio 2k ne kacal ba tsada 💃. Sai kusaka ta wannan account ɗin👇_*

_(2k)_

*9032345899*
*_Moniepoint MFB_*
*_BILKISU MUSA IBRAHIM_*

*_KATI MTN (2k)_*
*_09032345899_*

*_Shaidar biya: 👇_*
*_Telegram Number 09032345899_*

*_Ƴan NIGER🇳🇪 kuma bazamu barku a baya ba in sha ALLAHU zaku biya (Telegram vip 1,500 CFA) domin littafin KIƊA A RUWA..... na ji Audio-vocal. Sai ki biya tanan👇_*.

_(1,500 CFA)_
*_+227 98 94 12 81_*
*_My NITA_*

*Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 1,500 CFA vip telegram*

_Shaidar biya👇_

*_Whatsapp number_*
*_+227 98 94 12 81_*

*_AREWAPEN (Vvip)_*
*_Chapters & Audio_*
@BilynAbdull

*_Ƴan WhatsApp kuzo muyi shawara idan zaku iya amana ayi harkar nan daku 😂, dan bana son a barku a baya duk da dai bakwa ji, ba raga min zakuyi ba na sani duk da ƙaunar da nake muku 🤣😂._*

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
[22/05, 8:12 pm] Halima KW BZ: *_Typing📲_*

*_💦KIƊA A RUWA...!!💦_*

*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*

*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._

*_Masu fama da matsalar idanu kuma naku ya fara sauka a AREWAPEN faka-faka AUDIO da zafinsa. Book 1 zaku sameshi a cikin book 1. Book 2 na tare da book 2 shima. 💃💃😘😘😀_*

*_GENERAL FICTION_*

_Wannan labari ƙirƙirarre ne. Sunaye, wurare, da abubuwan da suka faru duk ƙirƙira ne, ba su da alaƙa da gaskiya ko wani, koda Bilyn Abdull ce 😂._

*_BOOK 4_*
_Chapter 8_

__________________
__________________

*_TELEGRAM GROUP_*

https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk

*_WHATSAPP CHANNEL_*

https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F

*_TIKTOK_*

https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/

*_INSTAGRAM_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

______________________
Chapter 10 · 0% Book details