Sashe 14
Kauyen Yar Kadde Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Nace ki d'auka ko?" cikin tsawa, niko taurin kai sai nai kamar banji sa ba nasa kai.
Banyi taku uku ba naji an ri'ko hannu na, waigo wa nayi ya wurgamin wata matsiyaciyan harara tare da sakin min hannu nawa, yayi min nuni da zo'bon da na aje.
Tura baki nayi ina cewa "mama tace na kawo ni, amma kafin ki sayo mai na sanar miki?".
Ya tsina fuska nayi sa'an nan nace kamar mai ciwon baki " gani nayi ai bakai ka aiken ba" tare da zum'bura baki.
"To sai ki d'auka kisha, don ni banshan 'kazan ta" kallon sa nayi shima ya d'ago daradaran idanuna sa.
"Eh, yadda kikajin nan" "ummm, hakan yayi" nace tare da matsawa na d'au zo'bon zan wuce.
"Shanye shi anan " yace fuska a d'aure kamar wanda bai ta'ba dariya ba.
Tsoro ne ya kamani na kafa kai bayan na bud'e goran .
Bige goran yayi ya zube min a jiki, sanyin zo'bon har cikin kaina.
Kallon sa nayi shima ni yake kallo, fuska babu walwala yake "duk ranan da na sake ganin ki da irin wad'an nan tsuma ko makaman tansu, tabbas rai zai mummunan 'baci".
" Fita min a gida" yace cikin tsawa daya firgitani, da gudu na fita.
"Sai yanzu naji sa'ki a zuciya ta, na fanshe haushi na" yace tare da shige wa d'aki, alwallah ya gaba tar don anfara kiran sallan magariba, ya fito don tafiya massalaci.
•••••••••••••
"Mugu kawai" nace lokacin da na shigo gida, "kada wa Joy?" cewar mama daga kitchen.
"Ba kowa" nace tare da nufan d'aki ina jin ta tana cewa "kin zama mahaukaciya ba ai dole" bance komai ba na bud'e gana mazgo na don canza kayan jikina.
Kallon kayan nayi ina tunanin maganan sa, don gaskiya na tsora ta sosai.
Ganin haka bai min ba na zazzage kayan ciki kaf a tsakar d'akin.
Da 'kar na samu wani dogon riga mai gajeran hannu ya wuce guwa nasa ina mai cewa "ka nunan kayan da zam saka tunda kasayo min" ina mai murgud'a baki kamar yana gaba na.
°°°°°°°°°°°°
Shiru- shiru har 9:30pm mama bata gansa ba, don haka tace "tashi ki kaima doctor abincin nan".
Zabura nayi tare da cewa " Allah mama bazani ba, doctor d'in nan fiti nan nene" zata sake magana sai ga Aisha ta shigo.
"Yauwa tunda ban isa da d'ayan ba nasan wannan baza ta'ki ba" ya tsina hanci nayi tare da ta'be baki.
Dariya Aisha tayi tare da cewa "waya ta'ba min besty? eyeh? mai mukayi ne mama" duk cikin tsokaana tayi.
Hararan ta nayi tare da gyara kwanciya ta.
"Uhum mama bani sa'kon mai zan miki kiga cika aiki yanzu tunda wata bata son albarka".
Tsaki nayi mama tace " ma'kocin ku likitan nan zaki mi'kawa abinci".
"Aiko yanzu na barsa waje yana shan iska, yauwa kai mai" mama tace tana mi'ka mata.
'Kar'ba tayi ta fita, bata jima ba ta dawo ko nace suka shigo tare hannu ta d'auke da kwanon abinci.
Waiga dukan mu mukayi kallon d'aya na masa na d'auke kai da sauri saboda hararan da yayi min.
Duk da dare ne akwai farin wata kamar rana.
Turo baki nayi, "Auwal ya haka?" lokacin da Aisha ta aje abincin.
Murmushi yayi tare da cewa "nagode mama naci abinci ko?" yace yana zama kusa dani kad'an.
Cikin 'kasa da murya yadda babu wanda zaiji yace "bakijin magana ko?" kallon su mama nayi naga hakalin ta naga abincin da aka aje Aisha cema naga tana kallo na.
"Bani da wasu sai irin su" nace a hankali, zaiyi magana mama tace "yanzu ka kyauta?, haka mukayi da kai?".
" Ayi ha'kuri gobe zanci" yace yana murmushi kad'an, "to nayi".
Fira suka d'an ta'ba da mama ya tashi yayi mata sai da safe ya fita, ba tare da ya kalleni ko ya sake kulani ba.
Kamar ma baiji mai nace ba..
Washe gari ina cikin barci safen da na saba, naji muryan sa yana ce da mama " mama yanzu naga waccen yarinyan da suke tafiya makaranta da Joy ta tafi, nace lafia bata tafi ba, ko ta riga ta gaba ne?".
"Wai Joy ai tayi kwana biyu bata zuwa, nayi nayi ta'ki, kuma ko jiya bayan kafita maganan makaranta yarinyan tazo mata, amma fir tace baza taba, ko naji tana ce da ita next week zata".
" To mai yasa?, oho gata can bata da sana'a kullum sai barci, don ko church yanzu taba tafiya, nai magana har bakina yayi tsini amma ta'ki haka ma zuba mata ido".
Inajin su sukai ta magana, har takai ga yace mama ta tasoni, zuwa ko tayi tashi na d'in nayi kamar ina barci.
Kiran suna na ta fara, da yake ban cika nauyin barci ba da safe, nafi barci harda minshari da dare, don saboda tsaban barci kana iya saceni ka gudu.
Tayi kira yakai uku na'ki ko motsi, sai ta fara jijjigani amma ko didim.
Auwal na tsaye yanaji gashi ya tsaida Aisha a waje .
Don haka sai ya shigo d'akin kawai yana cewa "mama bani ruwan sanyi kawai" bata musa ba kuwa tace "to tare da shiga bangi da don d'ako masa.
Bata jima ba ta kawo, jin tace " gashi" yasa na mi'ke a zabure, ina zare ido fuska ta a had'e.
Dariya mama tayi tare da cewa "dama ai nasan kinaji na, dakin cigaba da 'kaliya ai dakin ga aiki".
Turo baki nayi tare da zuro 'kafafuna a 'kasa, shiko kamar wani ubana yana wani kauda kai ya had'e rai yace " tashi kisa uniform mu tafi" kallon sa nayi tare da hararan sa.
Zuwa can nace "ai nayi latti , sai kuma gobe".
" Baki isaba tashi kisaka uniform nace" "uhum banyi wanka bani, ba'a bu'kata wuce ni kina 'batan lokaci" yace tare da barin d'akin.
Yana daga waje yace "ina jira minti biyar na baki, kika wuce rai ya 'baci".
" Kiji fa mam, sai kace wani ubana, to wai meye ruwan shi dani".
Bugen baki mama tayi tare da cewa "karki shirya ki tsaya yau naga duka" daga haka ta fita itama.........
Comment & share pls
[11/5, 9:50 PM] Safeeya Aliyu: 🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳
*'KAUYEN 'YAR KADDE*
🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳
*Story & written by: Safiyya Aliyu Wakili*
💫DA BAZAR MU WRITER'S ASS💫
*We are here to make you happy, smile, educate and realized that we are best among all........ DA BAZAR MU MUKE TUN'KAHO*
*Dedicated to Safiyya A W fan's club, kuna bani nishad'i godiya mai tarin yawa*
*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*
🅿2⃣9⃣to3⃣0⃣
Bayi na shiga, wanka ta nayi sannan na fito, koda na fito ganin kayan makaranta na da school bag d'ina a gefen katifa da kayan shafa, nasan duk aikin mama ne.
Janyo kayan shafan nayi ina hararan uniform d'in kamar shine ya min laifi, shafa mai nayi kawai na d'au kayan na saka, fuka babu komai na fito, tunda na fito ya kafeni da ido.
Kauda kaina nayi daga gare sa tare da tsaki a zuciya ta, nufan hanya fita nayi ba tare da na kula mama koshi ba.
"Baki sallame taba", kamar ba dani yake ba na 'kara gaba.
Girgiza kai kawai yayi mama tayi murmushi tare da cewa " nagode yaro na, ubangiji ya taimake ka" "ameen" yace tare da bin bayan na.
Ina fito wa naga Aisha tsaye, muna had'a ido na d'auke kai na.
Cikin masifa ta nufo ni, tana cewa "ai da baki fito ba, da ya barki, kinje kin shanya mutane, kuma muje yau sai kinsha duka biyu, gana rashin zuwa gana latti".
Kamar ba dani take ba na nufi hanya, lokacin ne ya fito motar sa ya bud'e, yana mai cewa Aisha " shiga muje na kai ku" da farin ciki ta nufi motan.
Ina jin su ban ko waigo ba, tana shiga ya tada motan.
Ya fara tafiya a hankali, don garin namu hawa da sauka ne, ga wasu shegun duwatsu, har da uban ramu ka, gomnati ta'ki kawo tallafi. Koda yazo dai-dai inda nake sai ya tsaya ba tare da yayi magana ba.
Ganin haka na bud'e bayan motan na shiga tunda Aisha na gaba.
Ajiyan zuciya ya saki tare da lumshe idanun sa na wani lokaci, kafin ya nisa ya bud'e a hankali ya sauke su akan fuska ta.
Ta madubin motan, wani irin nishad'i naji yana tsarga 'kashi da 'bargo na, shima ta 'barayin sa hakan ne.
Aisha ko washe baki take ta shiga motan da bata ta'ba shiga ba.
Fara tafiya yayi, a hankali yake tu'kin mota shiru kamar kurmaye, sai aukin kallo kamar zai cinyeni.
A haka har muka fito bakin titin shiga cikin gari, yana ganin sa a kwanlta yace yana mai kallon gefen da Aisha take "inane hanyan makaranta?" .
"Nan hanyan zaka bi" ta nuna masa gefen dama, daga nan ne ya fara tu'ki cikin kwarewa, da taimakon Aisha ya kawo mu makaranta .
Yana parking muka fita, kiran Aisha yayi don yaga sai faman had'e rai nake tunda muka fito.
Dawo wa tayi tare da le'ka kanta ta gilas d'in motan, kud'i ya mi'ka mata yace "kuyi break" godiya tayi masa sa'anan ta biyo bayan na da nake ta tafiya ta ba tare da na jira ta kona waigo ba.
Yana kallon na har na shiga class sa'anan ya bar wurin cike da tsanani 'kauna ta.
"Wai besty yau Allah ya d'aga mu, kuma Allah ya cece mu, da yanzu muna can hanya muna cin kwakwa, amma gaskiya yana da kirki, kalli kud'in da ya bamu, da har inajin haushin tsaida ni da yayi", kallo d'aya nayi na d'auke kai na, " ga naki, banso" nace.
" Kai amma guy d'in nan ya had'u, idanun sa farare 'kar dasu, gashin giran sa masu tsanani kyau da tsari, inama inama besty ohhhhhh Allah na" tace tana rugune hannun ta a 'kirjin ta
Esha ke cewa bayan mun zauna, zancen ta na sufan tamin habibi yayi ba'in 'bata min rai amma ban nuna ba nabar abin a raina yana cin raina, bamu dad'e da zuwa ba aka fara tsaron latt, malami ya shigo muka fara karatu.
****************
Muna fito wa daga cikin makaranta muna tafe Aisha sai zuba take ita d'aya kamar kad'anya .
Banyi taku uku ba naji an ri'ko hannu na, waigo wa nayi ya wurgamin wata matsiyaciyan harara tare da sakin min hannu nawa, yayi min nuni da zo'bon da na aje.
Tura baki nayi ina cewa "mama tace na kawo ni, amma kafin ki sayo mai na sanar miki?".
Ya tsina fuska nayi sa'an nan nace kamar mai ciwon baki " gani nayi ai bakai ka aiken ba" tare da zum'bura baki.
"To sai ki d'auka kisha, don ni banshan 'kazan ta" kallon sa nayi shima ya d'ago daradaran idanuna sa.
"Eh, yadda kikajin nan" "ummm, hakan yayi" nace tare da matsawa na d'au zo'bon zan wuce.
"Shanye shi anan " yace fuska a d'aure kamar wanda bai ta'ba dariya ba.
Tsoro ne ya kamani na kafa kai bayan na bud'e goran .
Bige goran yayi ya zube min a jiki, sanyin zo'bon har cikin kaina.
Kallon sa nayi shima ni yake kallo, fuska babu walwala yake "duk ranan da na sake ganin ki da irin wad'an nan tsuma ko makaman tansu, tabbas rai zai mummunan 'baci".
" Fita min a gida" yace cikin tsawa daya firgitani, da gudu na fita.
"Sai yanzu naji sa'ki a zuciya ta, na fanshe haushi na" yace tare da shige wa d'aki, alwallah ya gaba tar don anfara kiran sallan magariba, ya fito don tafiya massalaci.
•••••••••••••
"Mugu kawai" nace lokacin da na shigo gida, "kada wa Joy?" cewar mama daga kitchen.
"Ba kowa" nace tare da nufan d'aki ina jin ta tana cewa "kin zama mahaukaciya ba ai dole" bance komai ba na bud'e gana mazgo na don canza kayan jikina.
Kallon kayan nayi ina tunanin maganan sa, don gaskiya na tsora ta sosai.
Ganin haka bai min ba na zazzage kayan ciki kaf a tsakar d'akin.
Da 'kar na samu wani dogon riga mai gajeran hannu ya wuce guwa nasa ina mai cewa "ka nunan kayan da zam saka tunda kasayo min" ina mai murgud'a baki kamar yana gaba na.
°°°°°°°°°°°°
Shiru- shiru har 9:30pm mama bata gansa ba, don haka tace "tashi ki kaima doctor abincin nan".
Zabura nayi tare da cewa " Allah mama bazani ba, doctor d'in nan fiti nan nene" zata sake magana sai ga Aisha ta shigo.
"Yauwa tunda ban isa da d'ayan ba nasan wannan baza ta'ki ba" ya tsina hanci nayi tare da ta'be baki.
Dariya Aisha tayi tare da cewa "waya ta'ba min besty? eyeh? mai mukayi ne mama" duk cikin tsokaana tayi.
Hararan ta nayi tare da gyara kwanciya ta.
"Uhum mama bani sa'kon mai zan miki kiga cika aiki yanzu tunda wata bata son albarka".
Tsaki nayi mama tace " ma'kocin ku likitan nan zaki mi'kawa abinci".
"Aiko yanzu na barsa waje yana shan iska, yauwa kai mai" mama tace tana mi'ka mata.
'Kar'ba tayi ta fita, bata jima ba ta dawo ko nace suka shigo tare hannu ta d'auke da kwanon abinci.
Waiga dukan mu mukayi kallon d'aya na masa na d'auke kai da sauri saboda hararan da yayi min.
Duk da dare ne akwai farin wata kamar rana.
Turo baki nayi, "Auwal ya haka?" lokacin da Aisha ta aje abincin.
Murmushi yayi tare da cewa "nagode mama naci abinci ko?" yace yana zama kusa dani kad'an.
Cikin 'kasa da murya yadda babu wanda zaiji yace "bakijin magana ko?" kallon su mama nayi naga hakalin ta naga abincin da aka aje Aisha cema naga tana kallo na.
"Bani da wasu sai irin su" nace a hankali, zaiyi magana mama tace "yanzu ka kyauta?, haka mukayi da kai?".
" Ayi ha'kuri gobe zanci" yace yana murmushi kad'an, "to nayi".
Fira suka d'an ta'ba da mama ya tashi yayi mata sai da safe ya fita, ba tare da ya kalleni ko ya sake kulani ba.
Kamar ma baiji mai nace ba..
Washe gari ina cikin barci safen da na saba, naji muryan sa yana ce da mama " mama yanzu naga waccen yarinyan da suke tafiya makaranta da Joy ta tafi, nace lafia bata tafi ba, ko ta riga ta gaba ne?".
"Wai Joy ai tayi kwana biyu bata zuwa, nayi nayi ta'ki, kuma ko jiya bayan kafita maganan makaranta yarinyan tazo mata, amma fir tace baza taba, ko naji tana ce da ita next week zata".
" To mai yasa?, oho gata can bata da sana'a kullum sai barci, don ko church yanzu taba tafiya, nai magana har bakina yayi tsini amma ta'ki haka ma zuba mata ido".
Inajin su sukai ta magana, har takai ga yace mama ta tasoni, zuwa ko tayi tashi na d'in nayi kamar ina barci.
Kiran suna na ta fara, da yake ban cika nauyin barci ba da safe, nafi barci harda minshari da dare, don saboda tsaban barci kana iya saceni ka gudu.
Tayi kira yakai uku na'ki ko motsi, sai ta fara jijjigani amma ko didim.
Auwal na tsaye yanaji gashi ya tsaida Aisha a waje .
Don haka sai ya shigo d'akin kawai yana cewa "mama bani ruwan sanyi kawai" bata musa ba kuwa tace "to tare da shiga bangi da don d'ako masa.
Bata jima ba ta kawo, jin tace " gashi" yasa na mi'ke a zabure, ina zare ido fuska ta a had'e.
Dariya mama tayi tare da cewa "dama ai nasan kinaji na, dakin cigaba da 'kaliya ai dakin ga aiki".
Turo baki nayi tare da zuro 'kafafuna a 'kasa, shiko kamar wani ubana yana wani kauda kai ya had'e rai yace " tashi kisa uniform mu tafi" kallon sa nayi tare da hararan sa.
Zuwa can nace "ai nayi latti , sai kuma gobe".
" Baki isaba tashi kisaka uniform nace" "uhum banyi wanka bani, ba'a bu'kata wuce ni kina 'batan lokaci" yace tare da barin d'akin.
Yana daga waje yace "ina jira minti biyar na baki, kika wuce rai ya 'baci".
" Kiji fa mam, sai kace wani ubana, to wai meye ruwan shi dani".
Bugen baki mama tayi tare da cewa "karki shirya ki tsaya yau naga duka" daga haka ta fita itama.........
Comment & share pls
[11/5, 9:50 PM] Safeeya Aliyu: 🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳
*'KAUYEN 'YAR KADDE*
🌳🌳🌳🌳🌳🌳🌳
*Story & written by: Safiyya Aliyu Wakili*
💫DA BAZAR MU WRITER'S ASS💫
*We are here to make you happy, smile, educate and realized that we are best among all........ DA BAZAR MU MUKE TUN'KAHO*
*Dedicated to Safiyya A W fan's club, kuna bani nishad'i godiya mai tarin yawa*
*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*
🅿2⃣9⃣to3⃣0⃣
Bayi na shiga, wanka ta nayi sannan na fito, koda na fito ganin kayan makaranta na da school bag d'ina a gefen katifa da kayan shafa, nasan duk aikin mama ne.
Janyo kayan shafan nayi ina hararan uniform d'in kamar shine ya min laifi, shafa mai nayi kawai na d'au kayan na saka, fuka babu komai na fito, tunda na fito ya kafeni da ido.
Kauda kaina nayi daga gare sa tare da tsaki a zuciya ta, nufan hanya fita nayi ba tare da na kula mama koshi ba.
"Baki sallame taba", kamar ba dani yake ba na 'kara gaba.
Girgiza kai kawai yayi mama tayi murmushi tare da cewa " nagode yaro na, ubangiji ya taimake ka" "ameen" yace tare da bin bayan na.
Ina fito wa naga Aisha tsaye, muna had'a ido na d'auke kai na.
Cikin masifa ta nufo ni, tana cewa "ai da baki fito ba, da ya barki, kinje kin shanya mutane, kuma muje yau sai kinsha duka biyu, gana rashin zuwa gana latti".
Kamar ba dani take ba na nufi hanya, lokacin ne ya fito motar sa ya bud'e, yana mai cewa Aisha " shiga muje na kai ku" da farin ciki ta nufi motan.
Ina jin su ban ko waigo ba, tana shiga ya tada motan.
Ya fara tafiya a hankali, don garin namu hawa da sauka ne, ga wasu shegun duwatsu, har da uban ramu ka, gomnati ta'ki kawo tallafi. Koda yazo dai-dai inda nake sai ya tsaya ba tare da yayi magana ba.
Ganin haka na bud'e bayan motan na shiga tunda Aisha na gaba.
Ajiyan zuciya ya saki tare da lumshe idanun sa na wani lokaci, kafin ya nisa ya bud'e a hankali ya sauke su akan fuska ta.
Ta madubin motan, wani irin nishad'i naji yana tsarga 'kashi da 'bargo na, shima ta 'barayin sa hakan ne.
Aisha ko washe baki take ta shiga motan da bata ta'ba shiga ba.
Fara tafiya yayi, a hankali yake tu'kin mota shiru kamar kurmaye, sai aukin kallo kamar zai cinyeni.
A haka har muka fito bakin titin shiga cikin gari, yana ganin sa a kwanlta yace yana mai kallon gefen da Aisha take "inane hanyan makaranta?" .
"Nan hanyan zaka bi" ta nuna masa gefen dama, daga nan ne ya fara tu'ki cikin kwarewa, da taimakon Aisha ya kawo mu makaranta .
Yana parking muka fita, kiran Aisha yayi don yaga sai faman had'e rai nake tunda muka fito.
Dawo wa tayi tare da le'ka kanta ta gilas d'in motan, kud'i ya mi'ka mata yace "kuyi break" godiya tayi masa sa'anan ta biyo bayan na da nake ta tafiya ta ba tare da na jira ta kona waigo ba.
Yana kallon na har na shiga class sa'anan ya bar wurin cike da tsanani 'kauna ta.
"Wai besty yau Allah ya d'aga mu, kuma Allah ya cece mu, da yanzu muna can hanya muna cin kwakwa, amma gaskiya yana da kirki, kalli kud'in da ya bamu, da har inajin haushin tsaida ni da yayi", kallo d'aya nayi na d'auke kai na, " ga naki, banso" nace.
" Kai amma guy d'in nan ya had'u, idanun sa farare 'kar dasu, gashin giran sa masu tsanani kyau da tsari, inama inama besty ohhhhhh Allah na" tace tana rugune hannun ta a 'kirjin ta
Esha ke cewa bayan mun zauna, zancen ta na sufan tamin habibi yayi ba'in 'bata min rai amma ban nuna ba nabar abin a raina yana cin raina, bamu dad'e da zuwa ba aka fara tsaron latt, malami ya shigo muka fara karatu.
****************
Muna fito wa daga cikin makaranta muna tafe Aisha sai zuba take ita d'aya kamar kad'anya .