Sashe 16
Kasaita Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Maganarsa a hankali take fita, "Dama kirawo ki na yi saboda ina jin yunwa, don Allah ki sama mini wani abu in ci, ko da shayi ne."
"Ina kicin É—in?"
"Yana ƙasa."
Na miƙe na nufi ƙasa, lokacin da na ji jikina ya yi mini sanyi. Firji na gani, ina buɗashi na ga cike yake da kayan kicin,alayyahu ne,nama,salat,tumatirin gwangwani,kai tarkace na kicin dai gasu nan birjik.
A nan take na yi tunanin haɗa masa salat, na kuwa cire mayafin da na yafa a kaina na ajiye gefe ɗaya, haka alkyabbar saman kayan baccina, cikin ƙanƙanin lokaci na gama yanka salat ɗin,ƙwai kawai nake jira ya dafu, madadin in tsaya haka nan sai na yi tunanin haɗa masa matsatstsan lemo da abarba.
Miser ta matse lemo nasa na matse shi, abin ka ga na'urar bature, haka kuma injin ɗin markaɗe na bature ya markaɗe mini abarba (Blander), rashin sabo da dogayen kaya yasa na ji rigar saman na damuna, amma dole haka na haƙura da ita.
Bayan na tace su ne, na samo ƙanƙara na jefa a cikin ɗan siririn dogon kofin da na gani mai murfi yalo (jug), shuga ɗan kaɗan na saka masa na ga ƙatuwar ƙwalbar fulebo, ta sitirober (Strawberry).
"Sannu da aiki." Na ji an ce daga bayana.
*ƘASAITA BOOK 1*
*NA*
*MARYAM KABIR MASHI*
Page 13
Na yi saurin firgita na nufi inda alkyabbata take na É—auka na saka ta.
Farar singilet ce a jikinsa da dogon wando, wannan yasa ban ƙara juyawa na kalle shi ba, duk da dama jingine yake a jikin ƙofar shigowa ya harɗe hannayensa saman ƙirjinsa.
"In kin gama ina sama."
Ban amsa ba ni dai na ƙagu in gama in koma in ƙwanta.
Ƙarfe sha biyu da mintuna goma na kammala komai, cikin tangarayen nan nasu na sarauta a ciki na haɗa masa haɗin salat ɗin, na jera a wani ƙyakƙyawan faranti.
Ina shiga ɗakin nasa yana ƙwance a ƙasa kamar yanda na same shi da rana, na iso kusa da shi na ajiye kayan, ya tashi zaune.
"Za ki ci?" Na girgiza kaina.
"To na gode, shi kenan dama,mu je in rakaki."
Na miƙe na fara yin gaba, zuciyata ta cika dam da daɗi. Ina tafe yana biye da ni har ƙofar gida ta ƙasa, na juya na kalle shi.
"Mu je in kai ki gida ko,ko baƙya jin tsoro?"
Ban dai samu yin magana ba.
Yana bakin ƙofata ya dafa ta,ni kuwa ina daga cikin gida na riƙe ƙofar alamar zan rufe, ganin yana murmushi yasa na tsaya ina kallonsa.
"Na gode Yasmin,sai da safe kin kawo mini karin kumallo (Break fast)."
"Nima ba ni nake yin karin kumallo ba, yi mini ake yi."
"Ina son ci haka nan." Sai naga yana leƙen bayana, na ga ya ƙara zare idanuwansa.
"Me ye?" Na tambaye shi da sauri.
"Kamar wani abu ne tafe a bayanki."
Sai na yi saurin sakin ƙofa na fito da niyyar in waiga in ga ko meye, sai na ga ya yi ƴar dariya.
"Ba komai zolayarki nake yi, saboda kin ƙi yin fara'a."
Na ɗan yi murmushin dole, na koma cikin gida, sannan ya juya ya tafi,ni kuwa na kasa rufe ƙofar da take riƙe a hannuna, ina ta bin shi da kallon mamaki.
Har sai da ya juyo ya ɗago mini hannu, sannan na mayar da ƙofa na kulle da gudu na haye sama saboda tsoro. Ina isa madadin in ƙwanta sai na cire kayan saman rigar baccina, na buɗe ƙofar gaban gidan na fita baranda na runtse idanuwana na ware hannayena duk biyun iska na ɗaukan gashina a hankali.
Babu wanda ke zuciyata sai Anwar,son shi da ƙaunarshi suka dawo mini sabo a wannan daren,shin ko dai dama yaudara ce Yarima ya yi mini yanzu gashi nan ya tunasar da ni masoyina. Na tuna wata rana da Anwar ya zo gidanmu zai tafi, na yi masa rakiya, har ya zauna kujerar motarsa sai na ga ya miƙe tsaye, mamadin ya yi magana, sai na ga ya matso kusa da ni sosai.
A hankali ya ce, "Kalli ki ga yanda bishiyoyin nan ke rausayar jin daɗi, saboda sun samu ni'imtaccen wajen ƙwanciya."
Ya kawo hancinsa gab da nawa, sai na ji ya ce, "Haka muma wani daren za mu samu ni'imtaccen maƙwanci."
Idanuwana a lumshe ina ji ya sumbaci wuyana, yanda tsigar jikina ta tashi a wancan lokacin, haka na ji ni a yanzu.
Mamadin inji farin ciki, sai na ji lemar hawaye na gangaro mini,saboda tunaninmu ya zama mafarki,ko a wane hali yake ciki yanzu? Tunanin da nake so in kawar a zuciyata,amma sai nema yake ya haye mini,wai tunanin Yariman da yake babban maƙiyina na yi tsaki a daidai lokacin da na tuno ni bayana ƙwance a ƙirjinsa.
"Allah ya saka mini." Na faɗa tare da buɗe idanuwana, na shige cikin gida, har na kama ƙofar gidan zan rufe, sai na hango Yarima a barandarsa yasa hannuwa a aljihu yana kallon sama, na yi saurin mayar da ƙofata na kulle. Abin ka ga ƙofa mai gilashi ce, sai na ɗaga labulan na leƙo yanda na barshi haka yake, na yi tsaki na wuce na yi ƙwanciyata.
Bacci zo mana, amma kamar an busar mini da idanuwana,ko me ye dalili? Oho, na mutstsuke idanuwana tare da runtse su na yi lamo, amma babu alamar bacci a idanuwana. Ni kuma na kasa sanin me ya hana ni yin sa,a zuciyata na ji ina so na ƙara leƙawa in ga yarima ya shiga ɗakinsa ko kuwa yana nan a tsaye.
Shin dama haka yake yi ko kuwa yau ne kawai? Na miƙe na je na ɗaga labulan ƙofata,yana nan a tsaye, amma yanzu ya ɗan sunkuya ya dafa ɗan abin barandar wato gilashi mai zagayen nan. Taɓe baki na yi na koma, meye dalilinsa na ƙurawa dakina idanuwa,ko yana nufin nima irin sa ce mai tsayuwar dare, haka na faɗa gadona na tura kaina a ƙarƙashin filo, sannan na ɗan samu nutsuwa.
Ƙarfe goma na safiya na samu na farka daga saman gadona. Baccin bayan sallar Asubahi da na samu na yi ta da ƙyar, shi ma na san saboda kiran sallar masallacin cikin gidan shi yasa, wanda ake yin shi tamkar a ƙofar taga ta.
Na samu tsayin awa ɗaya, sannan na fito falon ƙasa,wayata da ke rataye a hannuna ita ce ta ɗauki ƙara, ina karawa a kunnena, sai na ji an ce.
"Ina jiran Gimbiya in ta tashi,abincina nake son ci." Sai a lokacin na tuna da ya ce yana cin abincin gidan na safe, na taɓe baki a lokacin da na isa ɓangaren da nake yin karin kumallo.
Su Musulma na zazzaune suna jirana, da sauri suka miƙe suka miƙa gaisuwarsu,a inda na zauna na bubbuɗe abin da su Asiya suka girka mini,kunun gyaɗa ne mai ɗauke da lafiyayyar madara, tare da farfesun dagwargwajajjan naman kaza, wanda babu ƙashi ko ɗaya a jikinsa, gefe ɗaya kuma biredi ne wanda aka yi shi da faɗi, tamkar an yayyankashi.
Ban da kunun aya wanda mutumina ne,ni na ce kullum ina buƙatar a dinga yi mini shi, amma mai kaurin gaske, cikin wata tangaran doguwa kuma tsire ne ya sha kayan haɗinsa sai ɗaukan ido da hanci yake, gefe ɗaya kuwa sinasir ne shishshimfiɗe a ƙwanan tangaran.
Na umarci su Mansura da su samo farantai su shirya su,su kai gidan Yarima su ce ga ni nan zuwa, haka aka yi. Ina shiga na same shi a sashen cin abinci ya kishingiɗa,siket da riga ne na atamfa ƴar Holand a jikina, ɗinkin mai shaf ne (fitted), amma buɗaɗɗan wuya da dogon hannu ne, sai mayafi ƙarami da na lulluɓe kaina da shi.
Atamfar Koriya ce da ɗishi-ɗishin zane baki a jikinta, wanda takalma masu tsini ne a ƙafata,su kuma baƙaƙe, haka mayafin saman kaina. Daga kishingiɗan nan da yake bai tashi ba, har sai da na zauna tukunna ya tashi ya zauna.
"Barka da Asuba." Na ce masa.
"Kin tashi lafiya?"
Na yi murmushi, "ga ni kuwa kaga alama."
"Ya jikin naki?"
"Ya warware."
Na ɗan yi shiru, "Ka yi haƙuri don Allah na manta ne da tuni an kawo maka,ni kuma ban tashi da wuri ba."
"Ba damuwa,ni ma ban daɗe da tashi ba,yau da ƙyar na je masallaci sallah saboda bacci, throughout jiya ban samu bacci ba na rasa abin da ya hana ni bacci.
"Jin daÉ—i." Na bashi amsa. Ya yi É—an murmushi, "ina fa jin daÉ—i ga wanda ba shi da mata." Ya faÉ—a a daidai lokacin da ya rage sautin muryarsa, na É—ago kai muka haÉ—a ido da shi, sai na ga ya yi murmushi tare da lumshe idanuwansa tare da buÉ—e su.
"Ko zaki amince ki zama matata,ki kawo mini jin daÉ—in?"
Na girgiza kaina tare da miƙewa tsaye. "Zan tafi ni." Na faɗa, amma sai na tsinci kaina da canjawar murya.
"Kayan abincin jiya na É—aki,ko za ki fito da su,dama ni mai gata ne, da an gyara mini É—akin nawa yau É—aya dai."
Ban ce masa komai ba na wuce abina.
"Ɗinkin ya yi miki ƙyau." Na ji ya faɗa a lokacin da na juya na tafi,a zuciyata na ce ka ƙari kinibibinka ni dai ba zan taɓa zama tare da kai ba,mayaudari,in ji da kunnena ka ce ba ka sona, sai yanzun don an hana ka zuwa wajen ƴaƴan turawa, shi ne za ka dinga kashe mini muryar kinibibi. Na gangaro na ajiye kayan kicin na yi gaba, zuwa gidana.
An samu ƙwanaki shida kenan yanayi mini ire-iren waɗannan tsirfar, ban da kallo da yake bina da shi, idan ina zaune a saman dutsen da nake hutawa, amma ko da wasa ban damu da abubuwan da yake yi ba, wani lokacin ma haushinsa nake ji, sai dai kuma abu ɗaya da ban gane shi ba, shi ne idan ina tare da shi duk jikina sai ya yi sanyi,ko magana ba na son yi.
Kuma idan na san yana waje a zaune, zan ga ina yawaitar kallon wajen,ko me ye haka kuma? Ni dai na san ina yawan tunanin Anwar wanda nake ta mafarkin ya zama angona,shekaru huÉ—u kenan, amma yau rana É—aya mafarkina ya zama dirama.
"Ina kicin É—in?"
"Yana ƙasa."
Na miƙe na nufi ƙasa, lokacin da na ji jikina ya yi mini sanyi. Firji na gani, ina buɗashi na ga cike yake da kayan kicin,alayyahu ne,nama,salat,tumatirin gwangwani,kai tarkace na kicin dai gasu nan birjik.
A nan take na yi tunanin haɗa masa salat, na kuwa cire mayafin da na yafa a kaina na ajiye gefe ɗaya, haka alkyabbar saman kayan baccina, cikin ƙanƙanin lokaci na gama yanka salat ɗin,ƙwai kawai nake jira ya dafu, madadin in tsaya haka nan sai na yi tunanin haɗa masa matsatstsan lemo da abarba.
Miser ta matse lemo nasa na matse shi, abin ka ga na'urar bature, haka kuma injin ɗin markaɗe na bature ya markaɗe mini abarba (Blander), rashin sabo da dogayen kaya yasa na ji rigar saman na damuna, amma dole haka na haƙura da ita.
Bayan na tace su ne, na samo ƙanƙara na jefa a cikin ɗan siririn dogon kofin da na gani mai murfi yalo (jug), shuga ɗan kaɗan na saka masa na ga ƙatuwar ƙwalbar fulebo, ta sitirober (Strawberry).
"Sannu da aiki." Na ji an ce daga bayana.
*ƘASAITA BOOK 1*
*NA*
*MARYAM KABIR MASHI*
Page 13
Na yi saurin firgita na nufi inda alkyabbata take na É—auka na saka ta.
Farar singilet ce a jikinsa da dogon wando, wannan yasa ban ƙara juyawa na kalle shi ba, duk da dama jingine yake a jikin ƙofar shigowa ya harɗe hannayensa saman ƙirjinsa.
"In kin gama ina sama."
Ban amsa ba ni dai na ƙagu in gama in koma in ƙwanta.
Ƙarfe sha biyu da mintuna goma na kammala komai, cikin tangarayen nan nasu na sarauta a ciki na haɗa masa haɗin salat ɗin, na jera a wani ƙyakƙyawan faranti.
Ina shiga ɗakin nasa yana ƙwance a ƙasa kamar yanda na same shi da rana, na iso kusa da shi na ajiye kayan, ya tashi zaune.
"Za ki ci?" Na girgiza kaina.
"To na gode, shi kenan dama,mu je in rakaki."
Na miƙe na fara yin gaba, zuciyata ta cika dam da daɗi. Ina tafe yana biye da ni har ƙofar gida ta ƙasa, na juya na kalle shi.
"Mu je in kai ki gida ko,ko baƙya jin tsoro?"
Ban dai samu yin magana ba.
Yana bakin ƙofata ya dafa ta,ni kuwa ina daga cikin gida na riƙe ƙofar alamar zan rufe, ganin yana murmushi yasa na tsaya ina kallonsa.
"Na gode Yasmin,sai da safe kin kawo mini karin kumallo (Break fast)."
"Nima ba ni nake yin karin kumallo ba, yi mini ake yi."
"Ina son ci haka nan." Sai naga yana leƙen bayana, na ga ya ƙara zare idanuwansa.
"Me ye?" Na tambaye shi da sauri.
"Kamar wani abu ne tafe a bayanki."
Sai na yi saurin sakin ƙofa na fito da niyyar in waiga in ga ko meye, sai na ga ya yi ƴar dariya.
"Ba komai zolayarki nake yi, saboda kin ƙi yin fara'a."
Na ɗan yi murmushin dole, na koma cikin gida, sannan ya juya ya tafi,ni kuwa na kasa rufe ƙofar da take riƙe a hannuna, ina ta bin shi da kallon mamaki.
Har sai da ya juyo ya ɗago mini hannu, sannan na mayar da ƙofa na kulle da gudu na haye sama saboda tsoro. Ina isa madadin in ƙwanta sai na cire kayan saman rigar baccina, na buɗe ƙofar gaban gidan na fita baranda na runtse idanuwana na ware hannayena duk biyun iska na ɗaukan gashina a hankali.
Babu wanda ke zuciyata sai Anwar,son shi da ƙaunarshi suka dawo mini sabo a wannan daren,shin ko dai dama yaudara ce Yarima ya yi mini yanzu gashi nan ya tunasar da ni masoyina. Na tuna wata rana da Anwar ya zo gidanmu zai tafi, na yi masa rakiya, har ya zauna kujerar motarsa sai na ga ya miƙe tsaye, mamadin ya yi magana, sai na ga ya matso kusa da ni sosai.
A hankali ya ce, "Kalli ki ga yanda bishiyoyin nan ke rausayar jin daɗi, saboda sun samu ni'imtaccen wajen ƙwanciya."
Ya kawo hancinsa gab da nawa, sai na ji ya ce, "Haka muma wani daren za mu samu ni'imtaccen maƙwanci."
Idanuwana a lumshe ina ji ya sumbaci wuyana, yanda tsigar jikina ta tashi a wancan lokacin, haka na ji ni a yanzu.
Mamadin inji farin ciki, sai na ji lemar hawaye na gangaro mini,saboda tunaninmu ya zama mafarki,ko a wane hali yake ciki yanzu? Tunanin da nake so in kawar a zuciyata,amma sai nema yake ya haye mini,wai tunanin Yariman da yake babban maƙiyina na yi tsaki a daidai lokacin da na tuno ni bayana ƙwance a ƙirjinsa.
"Allah ya saka mini." Na faɗa tare da buɗe idanuwana, na shige cikin gida, har na kama ƙofar gidan zan rufe, sai na hango Yarima a barandarsa yasa hannuwa a aljihu yana kallon sama, na yi saurin mayar da ƙofata na kulle. Abin ka ga ƙofa mai gilashi ce, sai na ɗaga labulan na leƙo yanda na barshi haka yake, na yi tsaki na wuce na yi ƙwanciyata.
Bacci zo mana, amma kamar an busar mini da idanuwana,ko me ye dalili? Oho, na mutstsuke idanuwana tare da runtse su na yi lamo, amma babu alamar bacci a idanuwana. Ni kuma na kasa sanin me ya hana ni yin sa,a zuciyata na ji ina so na ƙara leƙawa in ga yarima ya shiga ɗakinsa ko kuwa yana nan a tsaye.
Shin dama haka yake yi ko kuwa yau ne kawai? Na miƙe na je na ɗaga labulan ƙofata,yana nan a tsaye, amma yanzu ya ɗan sunkuya ya dafa ɗan abin barandar wato gilashi mai zagayen nan. Taɓe baki na yi na koma, meye dalilinsa na ƙurawa dakina idanuwa,ko yana nufin nima irin sa ce mai tsayuwar dare, haka na faɗa gadona na tura kaina a ƙarƙashin filo, sannan na ɗan samu nutsuwa.
Ƙarfe goma na safiya na samu na farka daga saman gadona. Baccin bayan sallar Asubahi da na samu na yi ta da ƙyar, shi ma na san saboda kiran sallar masallacin cikin gidan shi yasa, wanda ake yin shi tamkar a ƙofar taga ta.
Na samu tsayin awa ɗaya, sannan na fito falon ƙasa,wayata da ke rataye a hannuna ita ce ta ɗauki ƙara, ina karawa a kunnena, sai na ji an ce.
"Ina jiran Gimbiya in ta tashi,abincina nake son ci." Sai a lokacin na tuna da ya ce yana cin abincin gidan na safe, na taɓe baki a lokacin da na isa ɓangaren da nake yin karin kumallo.
Su Musulma na zazzaune suna jirana, da sauri suka miƙe suka miƙa gaisuwarsu,a inda na zauna na bubbuɗe abin da su Asiya suka girka mini,kunun gyaɗa ne mai ɗauke da lafiyayyar madara, tare da farfesun dagwargwajajjan naman kaza, wanda babu ƙashi ko ɗaya a jikinsa, gefe ɗaya kuma biredi ne wanda aka yi shi da faɗi, tamkar an yayyankashi.
Ban da kunun aya wanda mutumina ne,ni na ce kullum ina buƙatar a dinga yi mini shi, amma mai kaurin gaske, cikin wata tangaran doguwa kuma tsire ne ya sha kayan haɗinsa sai ɗaukan ido da hanci yake, gefe ɗaya kuwa sinasir ne shishshimfiɗe a ƙwanan tangaran.
Na umarci su Mansura da su samo farantai su shirya su,su kai gidan Yarima su ce ga ni nan zuwa, haka aka yi. Ina shiga na same shi a sashen cin abinci ya kishingiɗa,siket da riga ne na atamfa ƴar Holand a jikina, ɗinkin mai shaf ne (fitted), amma buɗaɗɗan wuya da dogon hannu ne, sai mayafi ƙarami da na lulluɓe kaina da shi.
Atamfar Koriya ce da ɗishi-ɗishin zane baki a jikinta, wanda takalma masu tsini ne a ƙafata,su kuma baƙaƙe, haka mayafin saman kaina. Daga kishingiɗan nan da yake bai tashi ba, har sai da na zauna tukunna ya tashi ya zauna.
"Barka da Asuba." Na ce masa.
"Kin tashi lafiya?"
Na yi murmushi, "ga ni kuwa kaga alama."
"Ya jikin naki?"
"Ya warware."
Na ɗan yi shiru, "Ka yi haƙuri don Allah na manta ne da tuni an kawo maka,ni kuma ban tashi da wuri ba."
"Ba damuwa,ni ma ban daɗe da tashi ba,yau da ƙyar na je masallaci sallah saboda bacci, throughout jiya ban samu bacci ba na rasa abin da ya hana ni bacci.
"Jin daÉ—i." Na bashi amsa. Ya yi É—an murmushi, "ina fa jin daÉ—i ga wanda ba shi da mata." Ya faÉ—a a daidai lokacin da ya rage sautin muryarsa, na É—ago kai muka haÉ—a ido da shi, sai na ga ya yi murmushi tare da lumshe idanuwansa tare da buÉ—e su.
"Ko zaki amince ki zama matata,ki kawo mini jin daÉ—in?"
Na girgiza kaina tare da miƙewa tsaye. "Zan tafi ni." Na faɗa, amma sai na tsinci kaina da canjawar murya.
"Kayan abincin jiya na É—aki,ko za ki fito da su,dama ni mai gata ne, da an gyara mini É—akin nawa yau É—aya dai."
Ban ce masa komai ba na wuce abina.
"Ɗinkin ya yi miki ƙyau." Na ji ya faɗa a lokacin da na juya na tafi,a zuciyata na ce ka ƙari kinibibinka ni dai ba zan taɓa zama tare da kai ba,mayaudari,in ji da kunnena ka ce ba ka sona, sai yanzun don an hana ka zuwa wajen ƴaƴan turawa, shi ne za ka dinga kashe mini muryar kinibibi. Na gangaro na ajiye kayan kicin na yi gaba, zuwa gidana.
An samu ƙwanaki shida kenan yanayi mini ire-iren waɗannan tsirfar, ban da kallo da yake bina da shi, idan ina zaune a saman dutsen da nake hutawa, amma ko da wasa ban damu da abubuwan da yake yi ba, wani lokacin ma haushinsa nake ji, sai dai kuma abu ɗaya da ban gane shi ba, shi ne idan ina tare da shi duk jikina sai ya yi sanyi,ko magana ba na son yi.
Kuma idan na san yana waje a zaune, zan ga ina yawaitar kallon wajen,ko me ye haka kuma? Ni dai na san ina yawan tunanin Anwar wanda nake ta mafarkin ya zama angona,shekaru huÉ—u kenan, amma yau rana É—aya mafarkina ya zama dirama.