Sashe 7
Heart Part 2 Complete Hausa Novel · about 2 min read
A hankali ta runtse idanunta. Nutsuwarta da tsoron Allahnta suka dawo jikinta. Taji ta tsani haihuwar ma bakidaya in dai son ta ne yau ya kawo ta ga wannan halakar.
Ta tuno tarbiyyar da dattijan iyayenta suka kare rayuwarsu a dorata a kai. Sun kuma sha gaya mata akan damuwarta na rashin haihuwa cewa babu mai baka abinda Allah bai ga damar baka ba.
A yau a bayan idon Ammi, Malam da Zayyan gashi rashin hakurinta ya kawo ta ga halaka har guda biyu; shirka da zina, zinar ma da aurenta….. yau ga inda rashin tawakkalinta, da rashin jin lallashin mijinta ya kawo ta, wai za’a yi zina da ita da aurenta…. kuma da wannan kazamin mushrikin.
Kafin Ammara ta ankara Safiyyah tayi wuf! Ta mike ta kama hanyar fita bukkar. Tana fitowa kuma sai ta taka da mugun gudu. Gudu take da gaske tun karfinta kamar mai gudu akan iska, ita kanta bata san ta iya gudu ba sai yau, domin gani take kamar Bokan zai biyota ko yasa rauhanansa sau daukota su maida masa ita kota wane hali.
Gudu take babu waiwaye har ta samu ta fita daga gonar, ta shiga ainahin cikin kauyen Daka-tsalle.
Jama’ar kauyen na kallonta sai gudu take kamar wani ya biyota, ba tareda ta san inda take jefa kafarta ba, ba kuma ta waiwaye, tana rokon Allah in mafarki ne take yi saboda damuwar rashin haihuwa yayi gaggawar farkar da ita haka daga wannan mummunan mafarkin.
Gudun neman tsira, nadama da ceton Imani Safiyyah ke yi, wanda yafi kama da gudun famfalaki, har ta hau kan babban titin kauyen, ba tare data sani ba. Bata lura ba wata mota kirar Honda ta taho da gudun gaske duk kokarinta na kaucema Safiyyah hakan bai samu ba. Direban kawai ganin Sophie yayi ta fado gabansa, yayi kokarin cin birki ya hango trailer a bayan sa, dole ya zabi bige Safiyyah don ceton kansa da motocin dake bayansa, wadanda cin birkinsa a lokacin zaisa trailer din ta danne su gabadaya.
Haka ya kwashe Safiyyah ya jefar a gefen titi, sannan shima ya gangara gefen titin ya tsaya yana ambaton “innalillahi wainna ilaihi rajioun”.
***** ***** *****
Ta tuno tarbiyyar da dattijan iyayenta suka kare rayuwarsu a dorata a kai. Sun kuma sha gaya mata akan damuwarta na rashin haihuwa cewa babu mai baka abinda Allah bai ga damar baka ba.
A yau a bayan idon Ammi, Malam da Zayyan gashi rashin hakurinta ya kawo ta ga halaka har guda biyu; shirka da zina, zinar ma da aurenta….. yau ga inda rashin tawakkalinta, da rashin jin lallashin mijinta ya kawo ta, wai za’a yi zina da ita da aurenta…. kuma da wannan kazamin mushrikin.
Kafin Ammara ta ankara Safiyyah tayi wuf! Ta mike ta kama hanyar fita bukkar. Tana fitowa kuma sai ta taka da mugun gudu. Gudu take da gaske tun karfinta kamar mai gudu akan iska, ita kanta bata san ta iya gudu ba sai yau, domin gani take kamar Bokan zai biyota ko yasa rauhanansa sau daukota su maida masa ita kota wane hali.
Gudu take babu waiwaye har ta samu ta fita daga gonar, ta shiga ainahin cikin kauyen Daka-tsalle.
Jama’ar kauyen na kallonta sai gudu take kamar wani ya biyota, ba tareda ta san inda take jefa kafarta ba, ba kuma ta waiwaye, tana rokon Allah in mafarki ne take yi saboda damuwar rashin haihuwa yayi gaggawar farkar da ita haka daga wannan mummunan mafarkin.
Gudun neman tsira, nadama da ceton Imani Safiyyah ke yi, wanda yafi kama da gudun famfalaki, har ta hau kan babban titin kauyen, ba tare data sani ba. Bata lura ba wata mota kirar Honda ta taho da gudun gaske duk kokarinta na kaucema Safiyyah hakan bai samu ba. Direban kawai ganin Sophie yayi ta fado gabansa, yayi kokarin cin birki ya hango trailer a bayan sa, dole ya zabi bige Safiyyah don ceton kansa da motocin dake bayansa, wadanda cin birkinsa a lokacin zaisa trailer din ta danne su gabadaya.
Haka ya kwashe Safiyyah ya jefar a gefen titi, sannan shima ya gangara gefen titin ya tsaya yana ambaton “innalillahi wainna ilaihi rajioun”.
***** ***** *****