Sashe 13
Heart Part 2 Complete Hausa Novel · about 9 min read
RANAR DASHEN
S
afiyyah ta sha ‘yar wuya wajen yi mata dashen IVF, amma ta dade tana gayawa kanta babu wani dadi a duniya da ya wuce (samun Dan kanka).
Shikuma uban gayyar ba kananan kudi ya kashe akai ba, amma ya gayawa kansa shima gara su haihun, wato su samu Dan ko daya ne a rayuwarsu, in ba haka ba bazai taba samun kan Safiyyah ba. Haka Mama bazata barsu su huta ba.
Na farko idan har ba haihuwa tasamu ba bazata taba dawowa ‘Hijabhie’ dinsa ta baya ba, bazata dawo musu da farin cikin su irinna baya ba, da kulawar soyayyarta da yake ta kewa yazu dare da rana. Shima kuma ba zai huta da kwarzabar Mama data su Yaya Zubaida ba, duk dai akan rashin haihuwar matar tasa, itama Sophie bazata taba hutawa da gorinsu da wulakancinsu da habaicinsu ba wanda basa ko gajiya, kuma shi yafi komai saka mata inferiority complex. Kai sai ka rantse haihuwar nan kudi ake sakawa a sayota da arha a bakin titi, ko iyawar mutum ke bashi ita.
Abin farin ciki a garesu kuma shine kamar almara, daga attempt na farko, cikin ikon Allah watanni uku da yin dashennan aka tabbatar da zaunawar ciki na wata uku a jikin Safiyyah Usman (Mrs Zayyan Rafindadi).
Duk da cewa a mafi yawan lokuta kashi 25-30 cikin 100 na masu yin IVF a karon farko ne kawai ake yin nasara. Amma yiwuwar nasarar na karuwa bayan an sake gwadawa sau da dama.
Dole Likitocin suka rike Safiyyah a asibitin har tsayin watanni hudu don a samu cikin ya zauna da kyau, hutu zallah Safiyyah keyi a gadon asibiti, ta wanke goma ta tsoma biyar. Zayyan ya dauki nauyin komai na kulawarta da hutunta wato ya tsaya ma Safiyyah.
Samun miji tsayyaye akan damuwarka da bukatunka ma kadai irin Arch. Zayyan Bello Rafindadi, ba karamar sa’a bace ga diya mace. Ta wannan fannin kam Safiyyah tayi sa’a, ta kuma ta yi sa’a, ta yi wa mata ‘yan uwanta da yawa kwalele, na sa’ar samun mijin da ya tara wadannan qualities din. Shi Zayyan a halayyarsa da babi’unsa akwai kyautatawa iyali, he’s a caring husband, baida son kansa, baida mugunta, abin hannunsa kakaf! Na iyalinsa da ‘yan uwansa ne, mutum ne mai kulawa, mai tattalin farin cikin iyali, sannan mai sonta da tausayinta da son kwanciyar hankalinta, in ka dauke matsalar mahaifiyarsa Mama mace marar kawaici da rashin maida surukin da baiyi mata ba nata, da ‘yan uwansa mararsa kara da zumunci ga Safiyyarsa, da kiyayya da raini gareta maras dalili, to da sai ace Safiyyah tafi matar gwamna sa’ar rayuwar gidan miji kam, saidai kawai matar gwamna ta nuna mata firda-firdan motoci da kantamemen gida da rashin hutu da rashin kwanciyar hankali.
Yo kiyayyarsu maras dalili mana? Don ta ko’ina ta duba ta hanga dalilin kiyayyar Mama da ‘yan uwan Zayyan a gareta, bata iya ta hango ta ina ta kuskuro su kota ragesu ba, bata ga hujjarsu mai ma’ana na kinta ba, iyaka kokarinta kullum tana yi wajen kyautata musu, duk wani abu da ya zama hakkinsu ne a wuyanta Safiyyah babu jinkiri tana kokarin saukeshi ba sai Zayyan ya fada ko ya sani ba, ba kuma sai ya saka ta ba, hannunta a mike yake kullum ga kowa nasa, wajen kyauta da yawan alkhairi, balle ga su dangin mijinta da haihuwarsu barkar haihuwarsu ko bikinsu baya wuce alkhairinta, kuma sai tayi babbar bajinta take jin dadi, kai har da wanda ba hakkinta ba, Safiyyah yi musu take, saboda kaunar data ke yi ma Zayyan. Amma Mama Fatu da ‘ya’yanta babu ragayya ko kankani a tsakaninsu, babu godi bare an gode kawai don bata haihu ba, ko tace Allah bai bata haihuwa dasu ba, babu mai yaba kokarinta, bata da wani farin jini a idonsu saboda ubanta ba mai kudi bane, ba mai Mulki ba, kuma ba mai irin tsarin rayuwarsu ta ‘yan boko ba, babban dalilinsu kuma na yanzu an doshi decade bata haihu da dansu ba (shekara goma).
Sosai cikin jikin Safiyyah ya bayyana kansa a watanni na biyar da yin dashensa, Safiyyah abin nema ya samu wai matar Dansanda ta haifi barawo, tafi Zayyan So da dokin isowar IVF Baby dinsu.
Zancen nasarar IVF da suka samu ya kai kunnen Mama Fatu daga bakin Yaya Zubaina, kasancewar komai Zayyan zaiyi sai yayi shawara da Zubaina. Yanzunma ya damka mata alhakin fara hada musu kayan haihuwar Baby ne inda yace, ta hada komai (unisex) don yaki yarda ma ayi scan a gano musu jinsin jaririn, yace shi kome Allah ya basu abin so ne da kauna da tattali a gareshi, walau mace walau namiji.
Safiyyah tun samun cikin ta bata je Katsina ba, kuma basu hadu da Mama ba, don Zayyan ya hanata tafiye-tafiye tun fitowarsu asibiti, wato tun zaunawar cikin. Ta kan dai kirata a waya tayi gaisuwar da bata wani tasiri wajen canza matsayinta a gun Mama Fatu.
Don haka Mama bata san cikin IVF ya kankama ba.
Har saida Zubaina tazo ta sameta kan wane shiri ya kamata suyi na haihuwar matar Baffa, kuma ince ko ta bada dakan yajin haihuwa da sauransu, don dole suyi gagarumin shiri, su yi duk abinda ya kamata a haihuwar Baffan Mama ta farko, bayan kwashe shekaru goma ba’a samu cikin ba.
Ta cigaba da gayawa Mama cikin farin ciki da taya dan uwanta murna,
“yanzu kinga Mama cikin taimakon Allah IVF din da sukayi (dashen haihuwa) kamar da wasa ya zauna”.
Ina wuta Mama Fatu ta jefasu shi da Safiyyah? Don babban ashar Mama ta saki, tana cewa “Safiyyah ta ja mata Da ga halaka, saboda bakin cikin ta kasa haihuwa ta hanyar da Allah ya tsara, saboda tana bakin cikin kada ya auro wata ita ta haifa masa naturally.
Mama bata taba zaton maganar da Zayyan yayi mata watannin baya cewa wai ta tunzura Safiyyah ga son yin IVF zasu aikata din ba, ta dauka magana ce kawai ta fatar bakinsu. Shiyasa bata wani hana su sosai tun a lokacin ba.
Mama tace ita ko a zamanin jahiliyyah bata taba jin inda aka haihu haihuwar dan halak ta hanyar Dashe ba.
Tace dan Dashe ba cikin zuri’arta ba, duk da Zayyan ya gaya mata tun kafin ayi bata taba daukar zancen wani serious ba, sai bayan data ji sun aikata din kuma ya zauna. Ta fitini kanta da zage-zage. Zubaina ta rasa yadda zata yi ta ganar da Mama IVF ba haramun bane a addinance.
Tace a ranta Mama kamar wadda bata yi ilmin zamani ba? Koko ace ta take sanin, saboda son ranta.
Mama ta kafe akan ra’ayin ta na cewa ba dai cikin zuri’arta za’a ajiye dan Dashe ba. Har ita Zubainar Mama ta hadasu ta zage tas, tace itace babbar munafuka da ita kadai ake kulle-kulle a gidan Baffa, ita dashi duk an saka sunansu a minjaye su duka an shanye, to su kam wato itada sauran ‘yan uwansa sunfi karfin gidan Alaramma.
Nan da nan kuma Mama ta figi wayarta ta kira Safiyyah. Don ta kasa hakura da zancen IVF.
Safiyyah na zaune a falonta, ta saka tirtsetsen cikinta a gaba, wanda kullum taji motsi a cikinsa sai tayi tazbihi ta tsarkake kudura da iradar Ubangiji. Kunun gargajiya na “Tamba” take sha a kofin Mug, wayarta tayi ruri.
Koda ganin yau Mama da kanta ta kirata, Safiyyah farin ciki taji mai yawa, ta dauka a dokance cikin matukar girmamawa har da russunawarta, ta dauka sannu da jiki Mama zata yi mata, don tun fitowarta daga asibiti basu yi waya da Mama ba. Don ko kiran Mama tayi don ta gaidata Mama bata amsa kiranta sai taga dama. Kuma gashi yau ta kira ta da kanta ba sako ba. Don haka yau Safiyyah da taga kiran Mama cikin wayarta ba karamin farin ciki taji a ranta ba.
Amma tana dagawa da sallama jin gurnanin Mama kadai ta cikin wayar yasa taji gabanta ya fadi, mummunar faduwa.
Ta hadiyi miyau da kyar tana amsa wayar Mama cikin ladabi mai girma, Mama ta basar da gaisuwarta da ladabinta tace,
“Sannu Hakimar Baffa! Babbar mace Hakima a gidan Baffa! Ko ince sannu Hakimar Dandume ‘yar Mallam jikar Alaramma. Ni ba kira nayi don mu gaisa ba, kira nayi inji dalilin kawomin Dan dashe cikin zuri’ata mai tsafta.
Ashe karyar Malanta kuke babu sanin Allah cikin lamarinku, ki gayamin Ayar da ta ce in ka kasa haihuwa kayi dashen ciki, ko wadda tace dashen ciki ya halatta, zan so kwarai sanin dalilinki na baiwa kanki abinda Allah bai ga damar baki ba, saboda tsoron kada Baffa ya sake ki ne ko don kada ya kara aure da wadda zata haihu?
Da zai yi dayan biyun wadannan din da tuni bai yi ba? Yau kuke tare dashi? Ko yau aka fara jiran haihuwar taki?
Shin ana aure dole ne Safiyyah, ko Baffana shine autan maza da kika bi kika laqe masa haka? Alhalin bazaki amfanar dashi komai ba?
In kina nufin ‘ya’yan dashe zaki ke kawomin cikin jikokina kuma in amsa kin yi kuskure, don bazan amsa ba, ba dai ni Fatuma ce zan goya dan Dashe a bayana da sunan jika ba.
Don haka tun wuri ki nemi Kakar diyanki in kin haifa a can Dandume, bani Fatun Bello Rafindadi ba, don ban yarda da halaccin haihuwarsu a addinin musulunci ba…...”.
Safiyyah kasa karasa sauraron Mama tayi, ta saki wayar a kan kujera tana fidda hawaye masu zafi.
Ba cin mutuncin Mama gareta ne ya sata kuka ba. Face jin a fakaice Mama na son tabo mutuncin iyayenta, cewa basu san Allah ba. Alhalin su ko sanin anyi dashen ma basu yi ba.
Zayyan bai san da wannan wayar da Mama ta bugowa Sophie ba, itama kuma bata gaya masa ba, ita kadai ta bar abun a ranta yayi ta cinta wanda ya sabbaba mata sabuwar damuwa kuma.
A rashin saninta shima Mama ta kira shi har gabanta, tayi masa nasa wankin babban bargon akan Dashe da suka yi kwatankwacin nata, tace “ya bata kunya ya rasa mazantaka, ya bari Safiyyah ta mayar da shi waina a tanda, sai yadda taga dama take juyashi, tunda har ta ja shi suyi dashen Da da ilminsa da komai babu iznin ita data haife shi.
A karshe ta gaya masa cewa “wannan dan ko an haife shi ba jikanta bane, na Alaramma ne shikadai”.
Maganar nan tayi masa zafi kwarai, Mama na son sheganta masa Da ne tun ba’a haifeshi ba ko yaya? Wannan cikin da yadda yake son sa tun bai zo duniya ba? Ya kidima ya shiga rudu, ya shiga tashin hankali mai yawa akan kalaman Mama.
A iya saninsa ya gayawa Mama zancen zasu yi IVF, kuma bata yi wani mummunan umarni a kai ba. Cewa tayi kawai in sun ga shi zai fishshesu to suje su yi.
Don haka tunda ya dawo gida a ranar Safiyyah ta kasa gane kansa, amma koda wasa bai gaya mata komai ba akan zuwansa Katsina, itama kuma ta ja bakinta tayi shiru bata gaya masa wayar da suka yi da Mama akan cikin ta ba.
Haka kowannesu ya bar abun a ransa yana damunsa, har zuwa sanda suka manta da shi suka cigaba da shirin taryar Baby dinsu, cike da wata irin soyayya ta daban ga yaron, ko yarinyar, tun bai zo duniya ba.
**** **** ****
S
afiyyah ta sha ‘yar wuya wajen yi mata dashen IVF, amma ta dade tana gayawa kanta babu wani dadi a duniya da ya wuce (samun Dan kanka).
Shikuma uban gayyar ba kananan kudi ya kashe akai ba, amma ya gayawa kansa shima gara su haihun, wato su samu Dan ko daya ne a rayuwarsu, in ba haka ba bazai taba samun kan Safiyyah ba. Haka Mama bazata barsu su huta ba.
Na farko idan har ba haihuwa tasamu ba bazata taba dawowa ‘Hijabhie’ dinsa ta baya ba, bazata dawo musu da farin cikin su irinna baya ba, da kulawar soyayyarta da yake ta kewa yazu dare da rana. Shima kuma ba zai huta da kwarzabar Mama data su Yaya Zubaida ba, duk dai akan rashin haihuwar matar tasa, itama Sophie bazata taba hutawa da gorinsu da wulakancinsu da habaicinsu ba wanda basa ko gajiya, kuma shi yafi komai saka mata inferiority complex. Kai sai ka rantse haihuwar nan kudi ake sakawa a sayota da arha a bakin titi, ko iyawar mutum ke bashi ita.
Abin farin ciki a garesu kuma shine kamar almara, daga attempt na farko, cikin ikon Allah watanni uku da yin dashennan aka tabbatar da zaunawar ciki na wata uku a jikin Safiyyah Usman (Mrs Zayyan Rafindadi).
Duk da cewa a mafi yawan lokuta kashi 25-30 cikin 100 na masu yin IVF a karon farko ne kawai ake yin nasara. Amma yiwuwar nasarar na karuwa bayan an sake gwadawa sau da dama.
Dole Likitocin suka rike Safiyyah a asibitin har tsayin watanni hudu don a samu cikin ya zauna da kyau, hutu zallah Safiyyah keyi a gadon asibiti, ta wanke goma ta tsoma biyar. Zayyan ya dauki nauyin komai na kulawarta da hutunta wato ya tsaya ma Safiyyah.
Samun miji tsayyaye akan damuwarka da bukatunka ma kadai irin Arch. Zayyan Bello Rafindadi, ba karamar sa’a bace ga diya mace. Ta wannan fannin kam Safiyyah tayi sa’a, ta kuma ta yi sa’a, ta yi wa mata ‘yan uwanta da yawa kwalele, na sa’ar samun mijin da ya tara wadannan qualities din. Shi Zayyan a halayyarsa da babi’unsa akwai kyautatawa iyali, he’s a caring husband, baida son kansa, baida mugunta, abin hannunsa kakaf! Na iyalinsa da ‘yan uwansa ne, mutum ne mai kulawa, mai tattalin farin cikin iyali, sannan mai sonta da tausayinta da son kwanciyar hankalinta, in ka dauke matsalar mahaifiyarsa Mama mace marar kawaici da rashin maida surukin da baiyi mata ba nata, da ‘yan uwansa mararsa kara da zumunci ga Safiyyarsa, da kiyayya da raini gareta maras dalili, to da sai ace Safiyyah tafi matar gwamna sa’ar rayuwar gidan miji kam, saidai kawai matar gwamna ta nuna mata firda-firdan motoci da kantamemen gida da rashin hutu da rashin kwanciyar hankali.
Yo kiyayyarsu maras dalili mana? Don ta ko’ina ta duba ta hanga dalilin kiyayyar Mama da ‘yan uwan Zayyan a gareta, bata iya ta hango ta ina ta kuskuro su kota ragesu ba, bata ga hujjarsu mai ma’ana na kinta ba, iyaka kokarinta kullum tana yi wajen kyautata musu, duk wani abu da ya zama hakkinsu ne a wuyanta Safiyyah babu jinkiri tana kokarin saukeshi ba sai Zayyan ya fada ko ya sani ba, ba kuma sai ya saka ta ba, hannunta a mike yake kullum ga kowa nasa, wajen kyauta da yawan alkhairi, balle ga su dangin mijinta da haihuwarsu barkar haihuwarsu ko bikinsu baya wuce alkhairinta, kuma sai tayi babbar bajinta take jin dadi, kai har da wanda ba hakkinta ba, Safiyyah yi musu take, saboda kaunar data ke yi ma Zayyan. Amma Mama Fatu da ‘ya’yanta babu ragayya ko kankani a tsakaninsu, babu godi bare an gode kawai don bata haihu ba, ko tace Allah bai bata haihuwa dasu ba, babu mai yaba kokarinta, bata da wani farin jini a idonsu saboda ubanta ba mai kudi bane, ba mai Mulki ba, kuma ba mai irin tsarin rayuwarsu ta ‘yan boko ba, babban dalilinsu kuma na yanzu an doshi decade bata haihu da dansu ba (shekara goma).
Sosai cikin jikin Safiyyah ya bayyana kansa a watanni na biyar da yin dashensa, Safiyyah abin nema ya samu wai matar Dansanda ta haifi barawo, tafi Zayyan So da dokin isowar IVF Baby dinsu.
Zancen nasarar IVF da suka samu ya kai kunnen Mama Fatu daga bakin Yaya Zubaina, kasancewar komai Zayyan zaiyi sai yayi shawara da Zubaina. Yanzunma ya damka mata alhakin fara hada musu kayan haihuwar Baby ne inda yace, ta hada komai (unisex) don yaki yarda ma ayi scan a gano musu jinsin jaririn, yace shi kome Allah ya basu abin so ne da kauna da tattali a gareshi, walau mace walau namiji.
Safiyyah tun samun cikin ta bata je Katsina ba, kuma basu hadu da Mama ba, don Zayyan ya hanata tafiye-tafiye tun fitowarsu asibiti, wato tun zaunawar cikin. Ta kan dai kirata a waya tayi gaisuwar da bata wani tasiri wajen canza matsayinta a gun Mama Fatu.
Don haka Mama bata san cikin IVF ya kankama ba.
Har saida Zubaina tazo ta sameta kan wane shiri ya kamata suyi na haihuwar matar Baffa, kuma ince ko ta bada dakan yajin haihuwa da sauransu, don dole suyi gagarumin shiri, su yi duk abinda ya kamata a haihuwar Baffan Mama ta farko, bayan kwashe shekaru goma ba’a samu cikin ba.
Ta cigaba da gayawa Mama cikin farin ciki da taya dan uwanta murna,
“yanzu kinga Mama cikin taimakon Allah IVF din da sukayi (dashen haihuwa) kamar da wasa ya zauna”.
Ina wuta Mama Fatu ta jefasu shi da Safiyyah? Don babban ashar Mama ta saki, tana cewa “Safiyyah ta ja mata Da ga halaka, saboda bakin cikin ta kasa haihuwa ta hanyar da Allah ya tsara, saboda tana bakin cikin kada ya auro wata ita ta haifa masa naturally.
Mama bata taba zaton maganar da Zayyan yayi mata watannin baya cewa wai ta tunzura Safiyyah ga son yin IVF zasu aikata din ba, ta dauka magana ce kawai ta fatar bakinsu. Shiyasa bata wani hana su sosai tun a lokacin ba.
Mama tace ita ko a zamanin jahiliyyah bata taba jin inda aka haihu haihuwar dan halak ta hanyar Dashe ba.
Tace dan Dashe ba cikin zuri’arta ba, duk da Zayyan ya gaya mata tun kafin ayi bata taba daukar zancen wani serious ba, sai bayan data ji sun aikata din kuma ya zauna. Ta fitini kanta da zage-zage. Zubaina ta rasa yadda zata yi ta ganar da Mama IVF ba haramun bane a addinance.
Tace a ranta Mama kamar wadda bata yi ilmin zamani ba? Koko ace ta take sanin, saboda son ranta.
Mama ta kafe akan ra’ayin ta na cewa ba dai cikin zuri’arta za’a ajiye dan Dashe ba. Har ita Zubainar Mama ta hadasu ta zage tas, tace itace babbar munafuka da ita kadai ake kulle-kulle a gidan Baffa, ita dashi duk an saka sunansu a minjaye su duka an shanye, to su kam wato itada sauran ‘yan uwansa sunfi karfin gidan Alaramma.
Nan da nan kuma Mama ta figi wayarta ta kira Safiyyah. Don ta kasa hakura da zancen IVF.
Safiyyah na zaune a falonta, ta saka tirtsetsen cikinta a gaba, wanda kullum taji motsi a cikinsa sai tayi tazbihi ta tsarkake kudura da iradar Ubangiji. Kunun gargajiya na “Tamba” take sha a kofin Mug, wayarta tayi ruri.
Koda ganin yau Mama da kanta ta kirata, Safiyyah farin ciki taji mai yawa, ta dauka a dokance cikin matukar girmamawa har da russunawarta, ta dauka sannu da jiki Mama zata yi mata, don tun fitowarta daga asibiti basu yi waya da Mama ba. Don ko kiran Mama tayi don ta gaidata Mama bata amsa kiranta sai taga dama. Kuma gashi yau ta kira ta da kanta ba sako ba. Don haka yau Safiyyah da taga kiran Mama cikin wayarta ba karamin farin ciki taji a ranta ba.
Amma tana dagawa da sallama jin gurnanin Mama kadai ta cikin wayar yasa taji gabanta ya fadi, mummunar faduwa.
Ta hadiyi miyau da kyar tana amsa wayar Mama cikin ladabi mai girma, Mama ta basar da gaisuwarta da ladabinta tace,
“Sannu Hakimar Baffa! Babbar mace Hakima a gidan Baffa! Ko ince sannu Hakimar Dandume ‘yar Mallam jikar Alaramma. Ni ba kira nayi don mu gaisa ba, kira nayi inji dalilin kawomin Dan dashe cikin zuri’ata mai tsafta.
Ashe karyar Malanta kuke babu sanin Allah cikin lamarinku, ki gayamin Ayar da ta ce in ka kasa haihuwa kayi dashen ciki, ko wadda tace dashen ciki ya halatta, zan so kwarai sanin dalilinki na baiwa kanki abinda Allah bai ga damar baki ba, saboda tsoron kada Baffa ya sake ki ne ko don kada ya kara aure da wadda zata haihu?
Da zai yi dayan biyun wadannan din da tuni bai yi ba? Yau kuke tare dashi? Ko yau aka fara jiran haihuwar taki?
Shin ana aure dole ne Safiyyah, ko Baffana shine autan maza da kika bi kika laqe masa haka? Alhalin bazaki amfanar dashi komai ba?
In kina nufin ‘ya’yan dashe zaki ke kawomin cikin jikokina kuma in amsa kin yi kuskure, don bazan amsa ba, ba dai ni Fatuma ce zan goya dan Dashe a bayana da sunan jika ba.
Don haka tun wuri ki nemi Kakar diyanki in kin haifa a can Dandume, bani Fatun Bello Rafindadi ba, don ban yarda da halaccin haihuwarsu a addinin musulunci ba…...”.
Safiyyah kasa karasa sauraron Mama tayi, ta saki wayar a kan kujera tana fidda hawaye masu zafi.
Ba cin mutuncin Mama gareta ne ya sata kuka ba. Face jin a fakaice Mama na son tabo mutuncin iyayenta, cewa basu san Allah ba. Alhalin su ko sanin anyi dashen ma basu yi ba.
Zayyan bai san da wannan wayar da Mama ta bugowa Sophie ba, itama kuma bata gaya masa ba, ita kadai ta bar abun a ranta yayi ta cinta wanda ya sabbaba mata sabuwar damuwa kuma.
A rashin saninta shima Mama ta kira shi har gabanta, tayi masa nasa wankin babban bargon akan Dashe da suka yi kwatankwacin nata, tace “ya bata kunya ya rasa mazantaka, ya bari Safiyyah ta mayar da shi waina a tanda, sai yadda taga dama take juyashi, tunda har ta ja shi suyi dashen Da da ilminsa da komai babu iznin ita data haife shi.
A karshe ta gaya masa cewa “wannan dan ko an haife shi ba jikanta bane, na Alaramma ne shikadai”.
Maganar nan tayi masa zafi kwarai, Mama na son sheganta masa Da ne tun ba’a haifeshi ba ko yaya? Wannan cikin da yadda yake son sa tun bai zo duniya ba? Ya kidima ya shiga rudu, ya shiga tashin hankali mai yawa akan kalaman Mama.
A iya saninsa ya gayawa Mama zancen zasu yi IVF, kuma bata yi wani mummunan umarni a kai ba. Cewa tayi kawai in sun ga shi zai fishshesu to suje su yi.
Don haka tunda ya dawo gida a ranar Safiyyah ta kasa gane kansa, amma koda wasa bai gaya mata komai ba akan zuwansa Katsina, itama kuma ta ja bakinta tayi shiru bata gaya masa wayar da suka yi da Mama akan cikin ta ba.
Haka kowannesu ya bar abun a ransa yana damunsa, har zuwa sanda suka manta da shi suka cigaba da shirin taryar Baby dinsu, cike da wata irin soyayya ta daban ga yaron, ko yarinyar, tun bai zo duniya ba.
**** **** ****