← Book details Hauwa Kulu Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 18

Sashe 7

Hauwa Kulu Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

ka da Hauwa”. Sarham, ya ma rasa inda zai sa kansa don farin ciki, kamar ya goya Mama, ya rasa ko wadanne irin kariman iyaye Allah ya albarkace shi da samu. Wadanda kullum bukatarsa da kwanciyar hankalinsa sune farkon abun dubawar su bata kowa ba. Har sai da ya yi kwallah saboda farin cikin amincewar su farad daya, abin da bai taba tsammani ba. Musamman Abba Prof. Ita kuwa Mama dalilinta na amincewa farad daya shine har gobe ta kasa yafe abinda Baban Madinah yayiwa Sarham na rainin arziki, wato bai bashi ita cikin mutunci da darajjawa ba sai bayan ya wulakanta shi ya kuma maida ita bazawara, da kuma gorin arzikin da yayi musu kafin ya basu auren 'yar sa. Sai yau ta samu abunda ya tsaya mata tuntuni a kokon rai, akan auren Madinah taji sukuf! Ya fada cikin cikinta. Ta kasa yafe wannan sai yau dinnan da a wurinta Sarham zaiyi aure daidai shi. Kuma inda ake ganin darajarsa da tasu. Inda za’a mutunta soyayyarsa. Da daddare suka shirya tafiya Kofar Na'isa shi da Abba Prof. don haka tun bayan isha Abba Prof. ke shiryawa. Sarham ya kira Madinah a waya ya gaya mata yau da dare ba zai samu shigowa Sorondinki ba, yana da uzuri wanda ba da jimawa ba zai sanar da ita ko mene insha Allahu. Ya kare zancensa da cewa, "Ina fatan Munawwarahta, Giwar Sarham, za ta kasance mai fahimtata a wannan karon ma, kamar koyaushe". Madinah taji jikinta yayi sanyi haka kawai, don bata ga dalilin wannan jirwayen ba, amma dai ta daure ta ce, "Insha Allah. Take care of yourself for us, good night Sweetheart". Ya ce, "Night!". Karfe takwas na daren ranar a kofar gidan Malam Bilyaminu ta yi musu shida mahaifin sa Abba Prof, Abbas Shanono. Abba ya zauna a mota har Sarham ya shiga ya yi wa Inna da Malam bayanin tare suke da mahaifinsa. Malam ya kara yarda da cewa Sarham da gaske yake, “wannan kai ne sha yanzu magani yanzu”, ya saka hularsa yana cewa, "Ikon Allah, ni da nake shirin ka zo ka kai ni in kwashi gaisuwa in kuma yi godiyar zumunci da kyautatawa, sai ka dauko shi da kansa tun kafin ni in fara zuwa? Baka kyauta ba". Da rawar jiki Malam ya yi wa Abba Prof. shimfidar darduma a nan tsakar gidansu ya je da kansa ya shigo da Abban. Abba ya ga mutunci da karrama dan Adam da sanin halacci wajen iyayen Hauwa, duk yadda yake tunanin talaucin nasu sai ya ga ba haka ba, kuma ba su da wata makusa da za'a kushe har aki auren jinin su akanta. Da gaske sunansu talakawa a bakin malam bahaushe. Amma fa ba irin talaucin da ya zama illa ba, tun daga soron gidan ka san ka zo gidan mutane masu tsaftar muhalli da tsaftar zuciya. Ko'ina ka duba tsaf tsaf yana tashin kamshin turaren wuta. Suka gaisa cikin karrama juna, Malam ya yi masa godiya a kan Sarham, ya kuma yaba masa a kan irin tarbiyyar da suka ba shi. Sannan ya tabbatar musu alkhairi zai yi ta bibiyar su har zuri’ar su. Shi kuma Abba ya ce, "ai babu komai don ya gine gidan kakannin jikokinsa, tunda gashi yanzu ya zo neman auren Hauwan ma dungurugum. Shi kuma Malam Bilyaminu da dukkan zuciyarsa ya jaddadawa Abba cewa ya baiwa Sarham auren Hauwa, ya sake jaddadawa, “ba Sarham ba ko wani daban Sarham ya kawo zai ba shi aurenta. Fatansa kawai a tausaya mata, ayi mata adalci a kuma dauke mata wahalhalun aure da hidimar da aka san bazata iya ba saboda lalurarta. Abba Prof. ya ce, Kada su ji komai, Sarham likitan ido ne, ya san komai a kan lalurar makanta, kuma tunda shi ya ce ya ji ya gani to ya ga zai iya ne. Ta fanninsu su iyayensa za su taya su kula da Hauwa kamar tana gabansu. Abba Prof bai bar gidan ba sai da suka tsayar da cewa, lallai kafin komawarsu kasar Ghana za a daura auren Dr. SARHAM da HAUWA. Malam Bilyaminu ya yi rantsuwa a kan bayan sadaki ba zai karbi komai ba, kuma ba za'a yi taron komai ba, aure kawai za a daura Hauwa ta tare a gidanta. Da Abba zai tafi ya ce a kira masa uwar sa wato Hauwa, yana so ya ganta. Inna ta shiga har dakinta ta same ta tana barci sadidan bata san wainar da ake soyawa ba sai da Inna ta tashe ta, "Ke Kulu, Kuluwa, Hauwa, taso ki sa hijabinki ki biyo ni". Hauwa ta mike cikin nauyin barci tana lalubar hijabin nata, ba tare da ta san ina za su je ba. Hannunta Inna ta kama har gaban Abba Prof. ta zaunar da ita tana gaya mata "Baban Likitana ne, ki gaishe shi". Hauwa ta gaida Abba, ba wata kunya a idonta a kansa don bata san ma me ya kawo shi gidan su ba, shi kuwa ya amsa fuska a sake, a ransa ya ce, Ban da rashin idon ai wannan ta ko ina matar aure ce. Tsari da zubin halittar jikinta shigen na mutanen Senegal. Ya koma gida a ranar ya gama magana da ‘yan uwansa waliyyan Sarham a kan ranar asabar su zo su je a daura auren. Wani ikon Allah tunda aka tsaida maganar auren Sarham da Hauwa ranar asabar Sarham bai iya ya kara zuwa gidan su Hauwa ba, kunyar Inna ya koma ji sosai. Sumayyah dai sai ji ta yi Mama ta ce mata asabar za a daura auren Bhaiya da yar mutanensa na Badala. Sumayyah a zaune take amma wani dan karamin ihu data saki hadi da juyi nan take, ya baiwa Mama mamaki, ta yi ta taka rawa daga tsaye, sannan ta zauna ta rangada guda wadda ta tashi Aunty Surayyah daga barcin la’asar din ta wanda ya zame mata farillah duk da kullum Mama na hana ta. Surayyah, data farka tagine me suke cewa, kamar kusan ace a sama ta tsinci zancen, bagatatan, wai Bhaiya zai kara aure, ta kuma tabbatar Madinah ba ta sani ba, don ko dazu sun yi waya da ita lafiya-lafiya ko kadan ba ta yi mata zancen nan ba. Surayyah gabadaya rudewa tayi, tana son ta kira Madinah ta labarta mata tana tsoron Yayan nasu da abida hakan zai haifar, kada ta yi masa riga-malam masallaci. Ta sani shi kuma baya so ka shiga sabgarsa musamman in bai s aka ciki ba. Shi ya sa ta yi shiru tana ta kawa zucin maganar. Haka ta wuni bugun cikin Sumayyah tana ta tambayar ta ko wace ce zai aura din? Sumayyah da ya ke ta san Surayya sarai, kuma ta san tsakaninta da Madina sai ta ce mata, “in zan baki shawara ki dauka, duk da nake kasa dake, ki fita daga abinda babu ruwanki. Nima ban san ko wace ce ba, amma ina backing maganar dari bisa dari sai me za’ayi?” Surayyah dai bata hakura ba, kuma bata dauki shawarar Sumayyah ba, ta sake bugun cikin Mama kan wace ce Bhaiya zai aura da Sumayyah ke ta murna haka??? Ta nuna kamar bata da issue da abin. Abinka da Uwa, sai Mama ta zauna ta bata labarin su kaf! Da irin kusancin da suke dashi da Sarham shekaru masu yawa a baya. Sai lokacin Surayyah ta tuna su, ta kuma gane yarinyar da yace yayiwa aiki ta makance ne wadada ya likewa tun daga lokacin, ta kuma gane sune wadanda yake turowa kudi tana cinyewa wadanda sabida su dan uwanta ya kusa daina gaisawa da ita. Surayyah cikin tsananin bacin rai ta ce, “kuma Mama shine kuka amince masa? Saboda Allah duka-duka yaushe Yaya Doctor yayi auren fari, wannan ai zalama ce da hadama, kuma me Madina ta rasa ko ta ragemu dashi da za’a yi mata kishiya ko arba'in ba ta yi da haihuwa masa ba?" Numfashin Surayya har sarkewa yakeyi don tsananin bacin rai. Mama na observing dinta a hankali don bata ga dalilin daukar zafinta akan maganar haka ba, na farko ba itace Madinah ba, na biyu ta san dai bata isa ta sa Sarham abu ko ta hana shi ba, ta ce. Mama ta nuna ta da yatsa tace "Surayyah bana son ki da shiga harkarsa, ke me guntun kashi a katara a idonsa, amma yace ya ayfe miki duk da nasan har abada bazai daina kallon ki da abin ba, ki rufawa kanki asiri ki fita daga harkar aurensa da duk matan da zai aura anan gaba ma. Ni na amince masa don auren soyayya Sarham zai yi wannan karon ma, kamar yadda ya auri Madinah don yana sonta, ba kuma don Madina ta gaza dashi ba ko mu tayi mana wani laifi, a’a kaddararsa ce auren mace fiye da daya, wadda shikadai yasan karfin dalilinsa". Tun magana na kankanuwa, wato abinda Hausawa suka ce abu kamar wasa karamar Magana ta zama babba cikin kwana daya, don har ga shi gobe ne daurin auren Dr. Sarham da Hauwa, kuma ya zo gidan ya fi sau a kirga sunyi hira da tsare tsare akan tarewar ta shi da Malam da Innarsa, inda Malam ya gaya masa baya bayan kowanne irin biki, a daura aure ya zo ya dauki matarsa ya tafi da ita duk inda yake so, amma har ya gama ya tafi abinsa bazaka ji ya nemi ganin Hauwa officially ba, ko ya nuna yana son yin magana kebewa da ita, kai gara da in ta gaida shi yana amsawa a shalake yanzu itama ko ta ji shi ta daina fitowa, ta daina ko kwakkwaran motsi idan ta ji shi a gidan, har sai ya tafi, ta maida kanta daddawar daka kawai. Inna ta rasa me ya sa ko ya zo yanzu ba ya wuce minti goma, zai gaishe ta suyi maganar da zasuyi da ita da Malam, sai yace ya wuce Sorondinki gun su Waheedah. Ita kuma ta kasa ce masa ko sau daya ne kafin daurin aure, ya kamata ya zaunar da Hauwa ya zanta da ita ya nemi soyayyarta duk da dais hi din ba bako bane amma Magana ta aure ai daban ce, ya kamata da bakin sa ya fada mata abin da ake ciki kan maganar aurensu, don ita kam Inna
Chapter 7 · 0% Book details