Sashe 11
Hauwa Kulu Part 3 Complete Hausa Novel · about 10 min read
MADINAH
Bayan Usman ya dauko ta. A kan hanyarsu ta zuwa gidan iyayenta daga filin jirgi kawai ta samu kanta da canza shawara. Ta ce a ranta macen kwarai ba ta yaji. Tsayawa ta ke ta fuskanci ‘challenges’ din gidanta dana mijinta ‘in general’ komai tsaurinsu in masu gyaruwa ne ta gyara. Zuciya mafi rinjaye na gaya mata Sarham wasa yake yi, domin ba zai taba iya hada ta da wata mace a zuciyarsa da duniyarsa ba.
Da wannan tunanin Dr. Madina ta canza shawara, ta ce da Usman ya wuce da ita gidanta ba gidansu ba. Tana gaya wa kanta wataqila akwai ta inda ta ragi Sarham tunda har ya fara yi mata wasan son karin aure.
Abin da ya kamata ta yi shi ne ta tsaya ta binciki ta ina wannan gibin nata yake, ta yi gaggawar cike shi. Ta ga dai ko aiki bata yi duk don ta samu lokacin sa da kyau shi da diyarsu. Ba kuma za ta gane ta ina ta rage shi din ba idan ba ya bude baki ya gaya mata ba.
Ta sa a ranta za ta yi magana ta gemu da Sarham din idan ya dawo, ta ji ta ina take kuskure shi da har tunanin karin aure ya yi crossing mind dinsa, dole ruwa ba ya tsami banza.
Da wannan Madinah ta baiwa kanta nutsuwa ta shiga gidanta ta bude ta soma gyare-gyare, bayan sun yi sallama da Yayanta Usman da cewa ya gayawa Hajjah Ramlah sai wajen gobe za ta shigo gidansu. Ta kawo sakonnin Hajjah Ramlah da ta taho da su daga Kano ta ba shi.
Amma me? Bayan ta manta da komai ta ci gaba da harkokinta cikin gidanta tana share-share da goge-goge, tana kuma kula da Waheedah, sai ga wayar kanwar Sarham wato Surayyah ta shigo mata.
Madinah ta amsa wayar Surayyah tana tsokanarta da amaryar Engnr. ta Aliyu ba da kanki a sare".
Tun daga nan Surayyah ta fahimci Madina ba ta san me ake ciki ba, don muryarta ras! Babu alamun damuwa a cikinta. Surayyah ta ce, cikin damuwa.
"Aunty Madinah kina ina?"
Madina ta amsa, "Na koma Jeddah Surayyah".
Surayyah ta ce, "Ga dukkan alamu ba ki san me ke faruwa da ke ba, kuma ni ba zan iya shiru ba, duk da an ce babu ruwana.
Ta nisa. "Aunty Madina ba zan taba manta tarin alkhairinki gare ni ba, har ma da wannan butulalliyar Allahn Sumayyah, hakika kin mana alkhairi mai yawa don haka ni ba zan ga inda za’a cuce ki in yi shiru ba.
Gaban Madina ya yi mugun faduwa, amma haka ta daure ta ci gaba da sauraron Surayyah ba ta katse mata hanzari ba, duk da a tsarinta ba a kawo mata gulma, kamar yadda ba ta zama ta yi gulmar wani ita ma, amma yau ta kasa tsayar da Surayyah sabida curiosity da ya ziyarceta irin na dan Adam.
"Yaya Doctor ya yi aure!".
Wadannan kalamai sune 'shock of her life' duk da cewa ta yi anticipating dinsu ko makamantansu, bayan zuciyarta ta gama karyata su daga bakin da ta tabbatar bai taba yi mata karya ba wato (bakin Sarham din da kansa).
Surayyah na jin irin numfashin da Madinah ke yi, sai taji tsoro, amma haka ta ci gaba da cewa, "Aunty Madinah, I am sorry to say, kuma yar talakawa fa ya dauko miki irin ‘yan cikin Badalar nan ‘yan tallan abinci, makauniya, almajira, basu da cin yau basu da na gobe sai abinda ya dauko ya basu, don talauci ubansu ya gudu ya barsu shekaru bakwai. Suka koma sayar da abinci a Tasha. Ko gidan zama ba su dashi, shi yake ciyar da su tun da jimawa.......". maganganu dai na gulma rututu
wadanda Madinah ba ta iya ta karasa ji ba ta saki wayarta a kasa ta rabe gida biyu.
Surayyah a can bangarenta ta ce, "Allah ya bi miki hakkinki Aunty Madinah, karshen wulakanci da kaskanci Yaya Doctor ya gama yi miki".
Mama ta gama shirin karbar amarya a dakin Sumayyah inda Madinah ma a nan aka karbe ta, don Malam Bilyaminu ya ce, ko kare kada a gayyato masa don biki, ya aurar da Hauwa ne ba don ya gaya wa duniya ba, sai don cika umarnin ubangiji na in 'ya'yanku sun kai munzali ku aurar da su.
Ya kuma gaya wa Abba Prof. duk wani abu na kayan daki da ake yi wa ya mace a bashi muhalli, zai yi wa Hauwa. Sai Abba ya ce, Sarham bai gama ginin gidansa na Kano ba har yau, za ta zauna tare da su ne kafin wucewarsu Jeddah. Sai dai ya bari sai can gaba, wato ranar da suka dawo kasar Kano da zama gaba daya sai ya saka mata kayan dakin.
Amma hakika wannan abu da Malam Bilyaminu ya fada na sayawa Hauwa kayan aure ya kara sayawa Hauwa mutunci a idon Abban da Mama, shi abu daya ke bata masa rai, in ya tuna Hauwa da uwarta sun sayar da abinci a tasha. Wannan kalma ta ‘yar tasha ya kasa daina ganin su Hauwa da ita. A cewar Sarham hakan yana cikin kaddarar su, sannan ba kowa da ya zauna ko yake sana'a a Tasha bane mutumin banza. Duk da haka dawowar Malam Bilyaminu a daidai wannan lokacin ya yi wa aibunsu wanka da soso da sabulu a idanun Farfesan.
Mama ta shirya masu zuwa taho da Hauwa kanwarta dake aure a Kaduna da kanwar Prof. Daga Shanono, amma Malam Bilyaminu ya ce don Allah su koma, Sarham ya zo ya tafi da matarsa da kansa shi wannan ne policy dinsa. Ba ya son kowacce irin bidi'a a auren Hauwa-Kulu albarka kawai yake nema mata.
Bai ki ba bayan kai ta gidan in sun so su yi walima kamar yadda Manzon Allah (S.A.W) ya koyar.
Daren yau ne ya kama Sarham zai tafi dauko Hauwa, tun safe yake gwada wayar Madinah ta ki shiga. Yana so ne yaji lafiyarta ya kuma gaya mata komai ya tabbata kafin Hauwa ta tare, ya kuma tabbatar yayi mata lallashin da za ta fahimce shi a kan aurensa da Hauwa. (Bai san tuni Surayyah ta kwaba masa aiki ba).
Duk da haka Madina ba ta bar gidanta ba, saboda a wurin ta karshen tozarta aure shi ne "yaji". A wurinta yaji ga macen aure wadda ta san abin da ta ke yi zubewar aji da zubewar kima ne.
Ita kuma Madina duk abin da zai zubar mata da aji da kima da martaba tana gudunsa a sittin, exactly yadda ta ke kallon auren da Sarham ya yi yanzu da makauniya ‘yar tasha, ‘yar talakawa ya zubar mata da aji, ya zubar mata da kima ya kaskantata ya wulakantata a idon tsararrakinta da duniya bakidaya.
A duniyar Subhana ta san tana son Dr. Sarham Abbas, tana kuma da wani irin kishi mai radadi a kansa, wanda hankali da tunani ba zai dauka ba, amma yau ji ta ke SON bakidayansa yana narkewa, yana zagwanyewa yana dalala kamar narkakkiyar dalma a kasa yana bin rariya.
Sai dai abu daya da ba zata yarda ta taba yi ba a rayuwar aurenta shi ne, "YAJI". Za ta jure ta zauna har Sarham ya dawo, in ya so in ta tabbatar da abin da Surayyah ta labarta mata a kan matar da ya aura daga bakinsa, to fa zamanta da Sarham ya kare. Ita ba ta saurin yanke hukunci a kan abin da ba ta da hujja kuma bata tabbatar ba. Wato dai bata yanke hukuncin one sided (daga bangare daya).
Wane irin makauniya irin yaran cikin BADALAR Kano da ke sayar da abinci a Tasha ana zaune kalau, miskiniya ce kenan ko Musaka? Duk ba wannan ba Makauniya fa? Shi kuma daga likitancin ido sai ya bige da auren makauniya, ‘yar talakawa? Shi kuwa Sarham me yake nema a rayuwarsa wannan faduwa kasa har yaushe??
Madinah ji take kamar ta dora hannu aka tayi ta kururuwa ita kadai. Sau tari tana jin ana fadin. Wani namijin in ya tashi karo aure in kayi duba da irin matar da yake da ita a gida, sai ka dauka hau ce ta hau kansa.
Madina ta yarda da Sarham matukar yarda, ta amince da shi da soyayyarsa iyakar amincewa, don haka wannan auren nasa da aka kara maimaita mata ya zama 'shock of her life' kuma in har Sarham ya tabbatar mata da hakan da bakinsa, to fa ta taho daga rakiyar duk wani Da namiji, ba Sarham kadai ba.
Maganar tafiya daga gidansa alhalin bai sake ta ba, ba shi ne solution ba, gara ta zauna su fuskanci juna idan ya dawo, don ta san matsayinta. Ta kuma tambayeshi hakikanin menene flaws dinta data cancanci wannan tozarcin.
Yanzu kam bayan ta ji irin matar da ya aura din, sai ta ki yarda wai gazawarta ta wani bangare ne ya sa Sarham yin wannan auren, za ta fi yarda in ya ce kawai ya daina sonta ne (short and simple).
Amma shin anya soyayya irin tasu wadda aka yi shekaru goma cur ana fafutukarta ta kuma samu actualizing ba jimawa don ko shekaru biyu ba su rufa da aure ba, za ta iya karewa a farau-farau din banza irin haka cikin dan lokaci???
Yanzu dai ta yarda ba gazawarta ba ce, ba kuma aibinta bane ko wani gap data bari, duba da irin matar da aka ce ya auro din.
Madinah a wannan gabar, ta kasa jure wani irin bakin ciki da ke cin ranta, tun farkon maganar bata ji kuka yazo mata ba sai yau, ta kifa fuska cikin tafukanta ta soma rera kuka na sarewa a kan mijin nata, dama duk wani da namiji mai numfashi, tana yi tana karyata soyayyar maza ko wacce iri ce, a yau Madina ta la'anci duk wata yarda da soyayyar da ta yi wa Sarham tsayin shekaru goma sha daya a baya.
**** **** ****
Maimakon irin shigar da angwaye ke yi ta manyan kaya ranar tarewar amarensu, abokai kuma su rako su dakin amarya. Dr. Sarham nasa salon daban ne, don wata farar T. Shirt ya saka samfurin 'Burberry' da bakin wandon 'Givenchy Jeans' mai kauri matuka, ya kuma taje sumar kansa sosai ya shafe ta da man da yake amfani da shi na musamman (Argan Oil for men), kowa ya san a dabi’arsa dama bai cika yin askin sumar kan shi ba sai tara suma da kykkyawan sajen (man’s pride) da baya gajiya da kula dasu. Sai kamshin turarensa na (Oud Abyad) da ‘Sandalia' na musamman yakeyi.
Dakin Mama ya fara zuwa ya same su ita da Sumayyah suna shirye-shiryensu su ma, ya ce, "Mama zan je in zo da ita yanzu, ina fatan Sumayyah ta gama gyaran dakin?"
Mama Mai Shari'a ta daga kai ta dubeshi, sai ta ga Baban na Waheedah ya koma mata yaro sabon jini, kuruciyar sa ta karu, kamar yanzu ne aka daura masa auren fari, wani boyayyen annuri ya fito sarari ya kayatar da idanun sa.
Da karsashi Sumayyah ta amsa,
"Komai fa ya kammala Bhaiya, har abincin da za ku ci na dare na kammala, na gasa maka kazar amarci da wani irin ‘french grill’ mai ruwa-ruwa dana koya online, sai jiran isowar kanwata, amarya, Hawwa-Jiddan Bhaiya, Yaya Sarham mai Jidda mai Madinah, bari in je in turare dakin da turaren 'hawii' yanzun nan”.
Murmushi kawai Sarham ya yi yana mamakin Sumayyah, in ya tuna tsiyar da ta shuka masa lokacin auren Madinah.
Mama ta ce, "Ai Sumayyah ko ita aka auro wa Hauwa sai haka, yau ko na minta daya ba ta zauna ta huta ba, duk abin da ta san Hauwa'u za ta bukata ta nemo ta ajiye mata a dakin nan har brush da maclean ba ta manta ba.
Sarham ya fadada murmushin sa zuwa dariya, ya ce, "Summy, mai abun mamaki, wanda ranta yake so ya ji dadinsa!".
Duk zancen nan da suke yi Surayyah da ke toilet din Mama tana jinsu, waya ta ke da Madinah a bandakin tana gaya mata cikin takaici mai yawa "Anti Madinah yanzu Yaya Doctor zai je ya dauko makauniyar nan fa, anya kin dauki matakin da ya dace? Ga ‘yar banzar yarinyar nan Sumayyah sai rawar kafa ta ke kamar ta fi shi son auren ma".
Madina ta kasa shiru wannan karon sabida a rayuwarta ta tsani gulma da daukar zance, ta kuma fahimci Surayyah halinta kenan, ta ce, "Surayyah please, in kin sake kirana mu yi magana wadda ta shafe mu, kada ki kara yi min zancen auren Sarham ko na yarinyar da ya aura, I may be intolerant, besides, is none of my business, in ba so kike kuma in samu ‘heart attack’ ba.
Ni wannan ba taimako na kike yi ba cutar da ni kikeyi a zuciyata da kwakwalwa ta".
Daga yadda ta ke maganar muryarta na daukewa sama-sama kamar mai fama da ciwon asthma, sai da Surayyah ta ji tsoro. Madina ta kashe wayarta daga nata bangaren, ta koma ta jingina da fuskar gadonta, ta lumshe ido tana ambaton sunan Ubangiji da neman daukinsa, na sanyayawa da tausasawa a gareta cewa ta ke a fili, idanu a rufe, hannu dafe da kirji;
"Ya Salamu-Sallim".
Bayan Usman ya dauko ta. A kan hanyarsu ta zuwa gidan iyayenta daga filin jirgi kawai ta samu kanta da canza shawara. Ta ce a ranta macen kwarai ba ta yaji. Tsayawa ta ke ta fuskanci ‘challenges’ din gidanta dana mijinta ‘in general’ komai tsaurinsu in masu gyaruwa ne ta gyara. Zuciya mafi rinjaye na gaya mata Sarham wasa yake yi, domin ba zai taba iya hada ta da wata mace a zuciyarsa da duniyarsa ba.
Da wannan tunanin Dr. Madina ta canza shawara, ta ce da Usman ya wuce da ita gidanta ba gidansu ba. Tana gaya wa kanta wataqila akwai ta inda ta ragi Sarham tunda har ya fara yi mata wasan son karin aure.
Abin da ya kamata ta yi shi ne ta tsaya ta binciki ta ina wannan gibin nata yake, ta yi gaggawar cike shi. Ta ga dai ko aiki bata yi duk don ta samu lokacin sa da kyau shi da diyarsu. Ba kuma za ta gane ta ina ta rage shi din ba idan ba ya bude baki ya gaya mata ba.
Ta sa a ranta za ta yi magana ta gemu da Sarham din idan ya dawo, ta ji ta ina take kuskure shi da har tunanin karin aure ya yi crossing mind dinsa, dole ruwa ba ya tsami banza.
Da wannan Madinah ta baiwa kanta nutsuwa ta shiga gidanta ta bude ta soma gyare-gyare, bayan sun yi sallama da Yayanta Usman da cewa ya gayawa Hajjah Ramlah sai wajen gobe za ta shigo gidansu. Ta kawo sakonnin Hajjah Ramlah da ta taho da su daga Kano ta ba shi.
Amma me? Bayan ta manta da komai ta ci gaba da harkokinta cikin gidanta tana share-share da goge-goge, tana kuma kula da Waheedah, sai ga wayar kanwar Sarham wato Surayyah ta shigo mata.
Madinah ta amsa wayar Surayyah tana tsokanarta da amaryar Engnr. ta Aliyu ba da kanki a sare".
Tun daga nan Surayyah ta fahimci Madina ba ta san me ake ciki ba, don muryarta ras! Babu alamun damuwa a cikinta. Surayyah ta ce, cikin damuwa.
"Aunty Madinah kina ina?"
Madina ta amsa, "Na koma Jeddah Surayyah".
Surayyah ta ce, "Ga dukkan alamu ba ki san me ke faruwa da ke ba, kuma ni ba zan iya shiru ba, duk da an ce babu ruwana.
Ta nisa. "Aunty Madina ba zan taba manta tarin alkhairinki gare ni ba, har ma da wannan butulalliyar Allahn Sumayyah, hakika kin mana alkhairi mai yawa don haka ni ba zan ga inda za’a cuce ki in yi shiru ba.
Gaban Madina ya yi mugun faduwa, amma haka ta daure ta ci gaba da sauraron Surayyah ba ta katse mata hanzari ba, duk da a tsarinta ba a kawo mata gulma, kamar yadda ba ta zama ta yi gulmar wani ita ma, amma yau ta kasa tsayar da Surayyah sabida curiosity da ya ziyarceta irin na dan Adam.
"Yaya Doctor ya yi aure!".
Wadannan kalamai sune 'shock of her life' duk da cewa ta yi anticipating dinsu ko makamantansu, bayan zuciyarta ta gama karyata su daga bakin da ta tabbatar bai taba yi mata karya ba wato (bakin Sarham din da kansa).
Surayyah na jin irin numfashin da Madinah ke yi, sai taji tsoro, amma haka ta ci gaba da cewa, "Aunty Madinah, I am sorry to say, kuma yar talakawa fa ya dauko miki irin ‘yan cikin Badalar nan ‘yan tallan abinci, makauniya, almajira, basu da cin yau basu da na gobe sai abinda ya dauko ya basu, don talauci ubansu ya gudu ya barsu shekaru bakwai. Suka koma sayar da abinci a Tasha. Ko gidan zama ba su dashi, shi yake ciyar da su tun da jimawa.......". maganganu dai na gulma rututu
wadanda Madinah ba ta iya ta karasa ji ba ta saki wayarta a kasa ta rabe gida biyu.
Surayyah a can bangarenta ta ce, "Allah ya bi miki hakkinki Aunty Madinah, karshen wulakanci da kaskanci Yaya Doctor ya gama yi miki".
Mama ta gama shirin karbar amarya a dakin Sumayyah inda Madinah ma a nan aka karbe ta, don Malam Bilyaminu ya ce, ko kare kada a gayyato masa don biki, ya aurar da Hauwa ne ba don ya gaya wa duniya ba, sai don cika umarnin ubangiji na in 'ya'yanku sun kai munzali ku aurar da su.
Ya kuma gaya wa Abba Prof. duk wani abu na kayan daki da ake yi wa ya mace a bashi muhalli, zai yi wa Hauwa. Sai Abba ya ce, Sarham bai gama ginin gidansa na Kano ba har yau, za ta zauna tare da su ne kafin wucewarsu Jeddah. Sai dai ya bari sai can gaba, wato ranar da suka dawo kasar Kano da zama gaba daya sai ya saka mata kayan dakin.
Amma hakika wannan abu da Malam Bilyaminu ya fada na sayawa Hauwa kayan aure ya kara sayawa Hauwa mutunci a idon Abban da Mama, shi abu daya ke bata masa rai, in ya tuna Hauwa da uwarta sun sayar da abinci a tasha. Wannan kalma ta ‘yar tasha ya kasa daina ganin su Hauwa da ita. A cewar Sarham hakan yana cikin kaddarar su, sannan ba kowa da ya zauna ko yake sana'a a Tasha bane mutumin banza. Duk da haka dawowar Malam Bilyaminu a daidai wannan lokacin ya yi wa aibunsu wanka da soso da sabulu a idanun Farfesan.
Mama ta shirya masu zuwa taho da Hauwa kanwarta dake aure a Kaduna da kanwar Prof. Daga Shanono, amma Malam Bilyaminu ya ce don Allah su koma, Sarham ya zo ya tafi da matarsa da kansa shi wannan ne policy dinsa. Ba ya son kowacce irin bidi'a a auren Hauwa-Kulu albarka kawai yake nema mata.
Bai ki ba bayan kai ta gidan in sun so su yi walima kamar yadda Manzon Allah (S.A.W) ya koyar.
Daren yau ne ya kama Sarham zai tafi dauko Hauwa, tun safe yake gwada wayar Madinah ta ki shiga. Yana so ne yaji lafiyarta ya kuma gaya mata komai ya tabbata kafin Hauwa ta tare, ya kuma tabbatar yayi mata lallashin da za ta fahimce shi a kan aurensa da Hauwa. (Bai san tuni Surayyah ta kwaba masa aiki ba).
Duk da haka Madina ba ta bar gidanta ba, saboda a wurin ta karshen tozarta aure shi ne "yaji". A wurinta yaji ga macen aure wadda ta san abin da ta ke yi zubewar aji da zubewar kima ne.
Ita kuma Madina duk abin da zai zubar mata da aji da kima da martaba tana gudunsa a sittin, exactly yadda ta ke kallon auren da Sarham ya yi yanzu da makauniya ‘yar tasha, ‘yar talakawa ya zubar mata da aji, ya zubar mata da kima ya kaskantata ya wulakantata a idon tsararrakinta da duniya bakidaya.
A duniyar Subhana ta san tana son Dr. Sarham Abbas, tana kuma da wani irin kishi mai radadi a kansa, wanda hankali da tunani ba zai dauka ba, amma yau ji ta ke SON bakidayansa yana narkewa, yana zagwanyewa yana dalala kamar narkakkiyar dalma a kasa yana bin rariya.
Sai dai abu daya da ba zata yarda ta taba yi ba a rayuwar aurenta shi ne, "YAJI". Za ta jure ta zauna har Sarham ya dawo, in ya so in ta tabbatar da abin da Surayyah ta labarta mata a kan matar da ya aura daga bakinsa, to fa zamanta da Sarham ya kare. Ita ba ta saurin yanke hukunci a kan abin da ba ta da hujja kuma bata tabbatar ba. Wato dai bata yanke hukuncin one sided (daga bangare daya).
Wane irin makauniya irin yaran cikin BADALAR Kano da ke sayar da abinci a Tasha ana zaune kalau, miskiniya ce kenan ko Musaka? Duk ba wannan ba Makauniya fa? Shi kuma daga likitancin ido sai ya bige da auren makauniya, ‘yar talakawa? Shi kuwa Sarham me yake nema a rayuwarsa wannan faduwa kasa har yaushe??
Madinah ji take kamar ta dora hannu aka tayi ta kururuwa ita kadai. Sau tari tana jin ana fadin. Wani namijin in ya tashi karo aure in kayi duba da irin matar da yake da ita a gida, sai ka dauka hau ce ta hau kansa.
Madina ta yarda da Sarham matukar yarda, ta amince da shi da soyayyarsa iyakar amincewa, don haka wannan auren nasa da aka kara maimaita mata ya zama 'shock of her life' kuma in har Sarham ya tabbatar mata da hakan da bakinsa, to fa ta taho daga rakiyar duk wani Da namiji, ba Sarham kadai ba.
Maganar tafiya daga gidansa alhalin bai sake ta ba, ba shi ne solution ba, gara ta zauna su fuskanci juna idan ya dawo, don ta san matsayinta. Ta kuma tambayeshi hakikanin menene flaws dinta data cancanci wannan tozarcin.
Yanzu kam bayan ta ji irin matar da ya aura din, sai ta ki yarda wai gazawarta ta wani bangare ne ya sa Sarham yin wannan auren, za ta fi yarda in ya ce kawai ya daina sonta ne (short and simple).
Amma shin anya soyayya irin tasu wadda aka yi shekaru goma cur ana fafutukarta ta kuma samu actualizing ba jimawa don ko shekaru biyu ba su rufa da aure ba, za ta iya karewa a farau-farau din banza irin haka cikin dan lokaci???
Yanzu dai ta yarda ba gazawarta ba ce, ba kuma aibinta bane ko wani gap data bari, duba da irin matar da aka ce ya auro din.
Madinah a wannan gabar, ta kasa jure wani irin bakin ciki da ke cin ranta, tun farkon maganar bata ji kuka yazo mata ba sai yau, ta kifa fuska cikin tafukanta ta soma rera kuka na sarewa a kan mijin nata, dama duk wani da namiji mai numfashi, tana yi tana karyata soyayyar maza ko wacce iri ce, a yau Madina ta la'anci duk wata yarda da soyayyar da ta yi wa Sarham tsayin shekaru goma sha daya a baya.
**** **** ****
Maimakon irin shigar da angwaye ke yi ta manyan kaya ranar tarewar amarensu, abokai kuma su rako su dakin amarya. Dr. Sarham nasa salon daban ne, don wata farar T. Shirt ya saka samfurin 'Burberry' da bakin wandon 'Givenchy Jeans' mai kauri matuka, ya kuma taje sumar kansa sosai ya shafe ta da man da yake amfani da shi na musamman (Argan Oil for men), kowa ya san a dabi’arsa dama bai cika yin askin sumar kan shi ba sai tara suma da kykkyawan sajen (man’s pride) da baya gajiya da kula dasu. Sai kamshin turarensa na (Oud Abyad) da ‘Sandalia' na musamman yakeyi.
Dakin Mama ya fara zuwa ya same su ita da Sumayyah suna shirye-shiryensu su ma, ya ce, "Mama zan je in zo da ita yanzu, ina fatan Sumayyah ta gama gyaran dakin?"
Mama Mai Shari'a ta daga kai ta dubeshi, sai ta ga Baban na Waheedah ya koma mata yaro sabon jini, kuruciyar sa ta karu, kamar yanzu ne aka daura masa auren fari, wani boyayyen annuri ya fito sarari ya kayatar da idanun sa.
Da karsashi Sumayyah ta amsa,
"Komai fa ya kammala Bhaiya, har abincin da za ku ci na dare na kammala, na gasa maka kazar amarci da wani irin ‘french grill’ mai ruwa-ruwa dana koya online, sai jiran isowar kanwata, amarya, Hawwa-Jiddan Bhaiya, Yaya Sarham mai Jidda mai Madinah, bari in je in turare dakin da turaren 'hawii' yanzun nan”.
Murmushi kawai Sarham ya yi yana mamakin Sumayyah, in ya tuna tsiyar da ta shuka masa lokacin auren Madinah.
Mama ta ce, "Ai Sumayyah ko ita aka auro wa Hauwa sai haka, yau ko na minta daya ba ta zauna ta huta ba, duk abin da ta san Hauwa'u za ta bukata ta nemo ta ajiye mata a dakin nan har brush da maclean ba ta manta ba.
Sarham ya fadada murmushin sa zuwa dariya, ya ce, "Summy, mai abun mamaki, wanda ranta yake so ya ji dadinsa!".
Duk zancen nan da suke yi Surayyah da ke toilet din Mama tana jinsu, waya ta ke da Madinah a bandakin tana gaya mata cikin takaici mai yawa "Anti Madinah yanzu Yaya Doctor zai je ya dauko makauniyar nan fa, anya kin dauki matakin da ya dace? Ga ‘yar banzar yarinyar nan Sumayyah sai rawar kafa ta ke kamar ta fi shi son auren ma".
Madina ta kasa shiru wannan karon sabida a rayuwarta ta tsani gulma da daukar zance, ta kuma fahimci Surayyah halinta kenan, ta ce, "Surayyah please, in kin sake kirana mu yi magana wadda ta shafe mu, kada ki kara yi min zancen auren Sarham ko na yarinyar da ya aura, I may be intolerant, besides, is none of my business, in ba so kike kuma in samu ‘heart attack’ ba.
Ni wannan ba taimako na kike yi ba cutar da ni kikeyi a zuciyata da kwakwalwa ta".
Daga yadda ta ke maganar muryarta na daukewa sama-sama kamar mai fama da ciwon asthma, sai da Surayyah ta ji tsoro. Madina ta kashe wayarta daga nata bangaren, ta koma ta jingina da fuskar gadonta, ta lumshe ido tana ambaton sunan Ubangiji da neman daukinsa, na sanyayawa da tausasawa a gareta cewa ta ke a fili, idanu a rufe, hannu dafe da kirji;
"Ya Salamu-Sallim".